• English
  • Business News
Friday, September 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba A Gwamnatin Tinubu Aka Bunkasa Jihar Legas Ba – Kakakin Yakin Neman Zaben Atiku

by Sulaiman
3 years ago
in Siyasa
0
Ba A Gwamnatin Tinubu Aka Bunkasa Jihar Legas Ba – Kakakin Yakin Neman Zaben Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da zaɓen 2023 ke ƙara gabatowa, kakakin yaɗa labaran manyan jam’iyyu biyu, wato PDP da APC, na ci gaba da antaya wa ɓangarorin junan su zafafan raddi.

Ciki makon jiya, Kakakin Yaɗa Kamfen ɗin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, Daniel Bwala, ya yaɓa wa Bola Tinubu da ke takarar shugaban ƙasa a APC zafafan raddi.

  • Zan Sayar Da Matatun Mai Ga ‘Yan Kasuwa Idan Aka Zabe Ni – Atiku

Bwala ya yi iƙirarin cewa masu tutiya da Tinubu ya bunƙasa Legas lokacin da ya na gwamna, to ba gaskiya ba ne. Bwala ya ce babu abin da Tinubu ya yi sai karɓar haraji kawai, amma ba shi ya gina wuraren da ya riƙa karɓar harajin ba.

Ya ce: “Idan za a yi duba da idon basira, za a ga cewa Tinubu ba Legas ya gina ba, haraji ya riƙa karɓa daga manyan kamfanoni, masana’antu da hukumomin gwamnatin tarayya kawai.

“Lokacin da ya yi gwamna daga 1999 zuwa 2007, bai gina wani abin kirki ba. Haraji ya riƙa karɓa. Ya tarar akwai tashoshin jiragen ruwa, tashar jirgin sama, sannan hedikwatar bankunan Najeriya duk a Legas su ke. Kuma can ne cibiyar kasuwanci. Don ya riƙa karɓar haraji da yawa ai ba abin mamaki ba ne.

Labarai Masu Nasaba

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

Gwamnan Bauchi Ya Gargaɗi Magoya Bayan Wike A PDP

“Kuma a lokacin an yi zargin cewa kamfanin da gwamnatin Legas ta bai wa kwangilar karɓar harajin, na Tinubu ne.

“Ashe kenan duk wanda aka ce masa ga aikin karɓar haraji, idan ka karɓa, ka ɗauki kashi 30%, ai dole ya yi ƙoƙari.”

Da ya koma batun dimokraɗiyya kuwa, Bwala ya ce lokacin da Tinubu ya na gwamna babu wanda ya kai shi yunƙurin kashe dimokraɗiyya a ƙasar nan.

Ya ce: “Ba a taɓa yin gwamnan da ya yi amfani da ‘yan majalisar jihar sa ya tsige mataimakan sa mabiyi da mabiyi har uku ba, sai Bola Tinubu.

“Sannan kuma duk mutanen da ya ke ɗorawa a siyasa, ba farin jinin jama’a ko karɓuwar su ce ke kai su ga nasara ba, sai ƙarfa-ƙarfar Tinubu, inji Bwala cikin wasu gajerun bidiyon da riƙa yaɗawa a shafukan sada zumuntar sa na soshiyal midiya.”

Daga nan kuma Bwala ya koma batun manufofin APC a ƙarƙashin mulkin Tinubu idan ya ci zaɓe, ya ce ba wani sabon tunani ba ne aka bijiro da shi, “daftari ne da manufofin da marigayi Abiola ya yi kamfen da su aka wanko.”

Baya ga wannan wankiyar daftarin manufofin Abiola, Bwala ya ce taken manufofin wanda a Turance ake kira “Renewed Hope”, ya nuna kenan duk masifar da aka shiga a gwamnatin APC za a sake maimaitawa kenan.

“Idan kuma sun ce wata sabuwa ce, to dai waɗanda su ka zauna su ka tsara manufofin APC a 2015, Tinubu ne ya haɗa wa Buhari su. Idan yanzu sun sake kawo wani salo daban, tunda su na cikin wannan gwamnatin, ai hakan ya na nufin kenan salon yanzu da wannan gwamnati ke kai, ya kai Najeriya ya baro kenan.

“Kuma irin kamfen ɗin da su ke yi, su na nuna gwamnatin Buhari ta gaza,” cewar Bwala.

Da ya ke magana kan Daraktan Yaɗa Labaran Kamfen ɗin TInubu, wato Festus Keyamo, Bwala ya ce ai su Keyamo ɗin ne su ka maka Tinubu kotu lokacin da ya na gwamna, su ka ce ya yi ƙaryar makarantun da ya yi iƙirarin cewa ya yi karatu.

“To abin da za a ƙara lura a nan, Keyamo ɗin nan da ke ta ɓaɓatun tallar Tinubu a yanzu, shi ne dai a wancan lokacin ya ci gaba da maka Tinubu kotu, har zuwa Kotun Ƙoli, ya na ƙalubalantar takardun makarantar sa.

“An kori ƙarar a Kotun Ƙoli saboda Keyamo bai haɗa kwafe-kwafen takardun hujjojin sa da rantsuwar kotu (affidavit) ba, amma kotu ba cewa ta yi Tinubu na da gaskiya ba,” inji Bwala.

Ya nanata cewa saboda tun farko Keyamo bai je kotu ya yi rantsuwa ba, ya haɗa kwafen takardar rantsuwar sa kwafen hujjojin dalilin maka Tinubu kotu, shi ya sa aka kori ƙarar kawai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Sake Gwabzawa Da Madrid Da Liverpool A Zagayen 16 Na Kofin Zakarun Turai

Next Post

Sharhi: Kasar Sin Na Son Kara Bude Kofarta Ga Kasashen Duniya

Related

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Siyasa

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

2 days ago
2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Gargaɗi Magoya Bayan Wike A PDP

2 days ago
Ina Da Yaƙinin Tinubu Ne Zai Lashe Zaɓen 2027 — Wike
Siyasa

Ina Da Yaƙinin Tinubu Ne Zai Lashe Zaɓen 2027 — Wike

4 days ago
Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai
Siyasa

Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai

4 days ago
Ɗan Majalisa Zai Saya Wa Makinde Fam Ɗin Takarar Shugaban Ƙasa A 2027
Siyasa

Ɗan Majalisa Zai Saya Wa Makinde Fam Ɗin Takarar Shugaban Ƙasa A 2027

5 days ago
Peter Obi Ya Caccaki Gwamnati Kan Ƙarin Kuɗin Fasfo
Siyasa

Peter Obi Ya Caccaki Gwamnati Kan Ƙarin Kuɗin Fasfo

1 week ago
Next Post
Sharhi: Kasar Sin Na Son Kara Bude Kofarta Ga Kasashen Duniya

Sharhi: Kasar Sin Na Son Kara Bude Kofarta Ga Kasashen Duniya

LABARAI MASU NASABA

'Yan Bindiga

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

September 5, 2025
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

September 5, 2025
Sojoji Sun Kwato Makamai Da Babura, Sun Ceto Mutane 3 A Kaduna 

Sojoji Sun Kama Ɗan Bindiga Ɗauke Da Makamai A Jihar Filato

September 5, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Jimamin Rasuwar Mutane A Nutsewar Jirgin Ruwa A Borgu, Ta Umurci NEMA Ta Kai Agaji 

September 5, 2025
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

September 5, 2025
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

September 5, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ƙuduri Aniyar Daƙile Ambaliyar Ruwa A Birane

Gwamnatin Kano Ta Ƙuduri Aniyar Daƙile Ambaliyar Ruwa A Birane

September 5, 2025
Noma

An Shiga Damuwa Yayin Da Gwamnatin Nijeriya Ke Jinkiri Wajen Biyan ‘Yan Kwangila

September 5, 2025
Sojoji Sun Cafke Ɗan Ta’adda Ɗauke Da Makamai A Filato

Sojoji Sun Cafke Ɗan Ta’adda Ɗauke Da Makamai A Filato

September 5, 2025
Ministan Wajen Najeriya: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Samarwa Afirka Damammakin Ci Gaba

Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Nijeriya Sun Koka Kan Rashin Biyan Basussukan Albashi

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.