ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba A Gwamnatin Tinubu Aka Bunkasa Jihar Legas Ba – Kakakin Yakin Neman Zaben Atiku

by Sulaiman
4 years ago
Tinubu

Yayin da zaɓen 2023 ke ƙara gabatowa, kakakin yaɗa labaran manyan jam’iyyu biyu, wato PDP da APC, na ci gaba da antaya wa ɓangarorin junan su zafafan raddi.

Ciki makon jiya, Kakakin Yaɗa Kamfen ɗin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, Daniel Bwala, ya yaɓa wa Bola Tinubu da ke takarar shugaban ƙasa a APC zafafan raddi.

  • Zan Sayar Da Matatun Mai Ga ‘Yan Kasuwa Idan Aka Zabe Ni – Atiku

Bwala ya yi iƙirarin cewa masu tutiya da Tinubu ya bunƙasa Legas lokacin da ya na gwamna, to ba gaskiya ba ne. Bwala ya ce babu abin da Tinubu ya yi sai karɓar haraji kawai, amma ba shi ya gina wuraren da ya riƙa karɓar harajin ba.

ADVERTISEMENT

Ya ce: “Idan za a yi duba da idon basira, za a ga cewa Tinubu ba Legas ya gina ba, haraji ya riƙa karɓa daga manyan kamfanoni, masana’antu da hukumomin gwamnatin tarayya kawai.

“Lokacin da ya yi gwamna daga 1999 zuwa 2007, bai gina wani abin kirki ba. Haraji ya riƙa karɓa. Ya tarar akwai tashoshin jiragen ruwa, tashar jirgin sama, sannan hedikwatar bankunan Najeriya duk a Legas su ke. Kuma can ne cibiyar kasuwanci. Don ya riƙa karɓar haraji da yawa ai ba abin mamaki ba ne.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

“Kuma a lokacin an yi zargin cewa kamfanin da gwamnatin Legas ta bai wa kwangilar karɓar harajin, na Tinubu ne.

“Ashe kenan duk wanda aka ce masa ga aikin karɓar haraji, idan ka karɓa, ka ɗauki kashi 30%, ai dole ya yi ƙoƙari.”

Da ya koma batun dimokraɗiyya kuwa, Bwala ya ce lokacin da Tinubu ya na gwamna babu wanda ya kai shi yunƙurin kashe dimokraɗiyya a ƙasar nan.

Ya ce: “Ba a taɓa yin gwamnan da ya yi amfani da ‘yan majalisar jihar sa ya tsige mataimakan sa mabiyi da mabiyi har uku ba, sai Bola Tinubu.

“Sannan kuma duk mutanen da ya ke ɗorawa a siyasa, ba farin jinin jama’a ko karɓuwar su ce ke kai su ga nasara ba, sai ƙarfa-ƙarfar Tinubu, inji Bwala cikin wasu gajerun bidiyon da riƙa yaɗawa a shafukan sada zumuntar sa na soshiyal midiya.”

Daga nan kuma Bwala ya koma batun manufofin APC a ƙarƙashin mulkin Tinubu idan ya ci zaɓe, ya ce ba wani sabon tunani ba ne aka bijiro da shi, “daftari ne da manufofin da marigayi Abiola ya yi kamfen da su aka wanko.”

Baya ga wannan wankiyar daftarin manufofin Abiola, Bwala ya ce taken manufofin wanda a Turance ake kira “Renewed Hope”, ya nuna kenan duk masifar da aka shiga a gwamnatin APC za a sake maimaitawa kenan.

“Idan kuma sun ce wata sabuwa ce, to dai waɗanda su ka zauna su ka tsara manufofin APC a 2015, Tinubu ne ya haɗa wa Buhari su. Idan yanzu sun sake kawo wani salo daban, tunda su na cikin wannan gwamnatin, ai hakan ya na nufin kenan salon yanzu da wannan gwamnati ke kai, ya kai Najeriya ya baro kenan.

“Kuma irin kamfen ɗin da su ke yi, su na nuna gwamnatin Buhari ta gaza,” cewar Bwala.

Da ya ke magana kan Daraktan Yaɗa Labaran Kamfen ɗin TInubu, wato Festus Keyamo, Bwala ya ce ai su Keyamo ɗin ne su ka maka Tinubu kotu lokacin da ya na gwamna, su ka ce ya yi ƙaryar makarantun da ya yi iƙirarin cewa ya yi karatu.

“To abin da za a ƙara lura a nan, Keyamo ɗin nan da ke ta ɓaɓatun tallar Tinubu a yanzu, shi ne dai a wancan lokacin ya ci gaba da maka Tinubu kotu, har zuwa Kotun Ƙoli, ya na ƙalubalantar takardun makarantar sa.

“An kori ƙarar a Kotun Ƙoli saboda Keyamo bai haɗa kwafe-kwafen takardun hujjojin sa da rantsuwar kotu (affidavit) ba, amma kotu ba cewa ta yi Tinubu na da gaskiya ba,” inji Bwala.

Ya nanata cewa saboda tun farko Keyamo bai je kotu ya yi rantsuwa ba, ya haɗa kwafen takardar rantsuwar sa kwafen hujjojin dalilin maka Tinubu kotu, shi ya sa aka kori ƙarar kawai.

Tinubu
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Sharhi: Kasar Sin Na Son Kara Bude Kofarta Ga Kasashen Duniya

Sharhi: Kasar Sin Na Son Kara Bude Kofarta Ga Kasashen Duniya

LABARAI MASU NASABA

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

June 5, 2026
Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 5, 2026
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

June 5, 2026
Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.