ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Mu Janye Tsofaffin Takardun Naira Ba – CBN

by Sadiq
3 years ago
CBN

Babban bankin Nijeriya (CBN) ya sake tabbatar wa ‘yan kasar nan cewar akwai isassun takardun kudi na Naira tare da kwantar da hankalin mutane na daina shiga firgici saboda karancin kudade a bankuna.

CBN, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba, ya sake nanata cewa tsofaffi da sabbin takardun kudi na Naira suna daram.

  • An Wayar Da Kan Malamai Game Da Ajiyar Kudin Aikin Hajjin 2024 A Kaduna
  • An Kwace Kambun Hilda Baci A Gasar Dafa Abinci Ta Duniya

“Don kaucewa shakku, muna nanata cewa akwai isassun takardun kudi a fadin kasar nan don gudanar da duk harkokin tattalin arziki na yau da kullum,” in ji kakakin CBN, Isa AbdulMumin.

ADVERTISEMENT

“Saboda haka, an umarci rassan bankin CBN a fadin kasar nan da su ci gaba da fitar da takardun kudi daban-daban na tsofaffi da sabbi cikin adadi mai yawa zuwa bankunan kasuwanci don ci gaba da rarrabawa ga abokan huldar bankuna.

“Muna so mu sake bayyana cewa duk takardun kudi na banki da CBN ke bayarwa suna nan a kan doka. Kamar yadda sashe na 20 (5) na dokar CBN ta shekarar 2007, babu wanda ya isa ya ki karbar Naira a matsayin hanyar biyan kudi.”

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

CBN “ya sake tabbatar da cewa akwai isassun takardun kudi don saukaka ayyukan tattalin arziki na yau da kullum”.

A watan Oktoban shekarar da ta gabata ne tsohon gwamnan CBN, Godwin Emefiele, ya bayyana shirin sake fasalin wasu kudade, sannan ya bukaci ‘yan Nijeriya da su musanya tsofaffin takardunsu kafin ranar 31 ga watan Junairu, 2023.

Wannan hukunci ya haifar da tabarbarewar tattalin arziki yayin da ‘yan Nijeriya da dama suka shiga mawuyacin hali, lamarin da ya haifar da tarzoma a wasu jihohin da kone wasu bankuna da kuma injinan cire kudi.

Daga baya bankin ya amince da tsawaita wa’adin canjin takardun Naira.

Wasu gwamnonin jam’iyyar APC na wancan lokacin sun kai CBN da gwamnatin tarayya zuwa kotun koli inda kotun koli ta yanke hukunci a watan Maris na 2023 cewa tsofaffin takardun kudi na N200, N500, da N1,000 za su ci gaba da aiki har zuwa ranar 31 ga Disamba. , 2023.

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Taron MDD: Gwamntin Tarayya Za Ta Dauki Nauyin Gudanar Da Makarantar UNESCO A Nijeriya – Minista

Taron MDD: Gwamntin Tarayya Za Ta Dauki Nauyin Gudanar Da Makarantar UNESCO A Nijeriya - Minista

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.