• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Na Iya Runtsawa Idan Na Tuna Halin Da Marayu Ke Ciki -Rukayya Abdurrahman

by Sulaiman and Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
in Rahotonni
0
Ba Na Iya Runtsawa Idan Na Tuna Halin Da Marayu Ke Ciki -Rukayya Abdurrahman
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamared Hajiya Rukayya Abdurrahaman wadda akafi sani da Uwar Marayu, Shugabar KungiyarTallafa Wa Marayu da Zawarawa ta Jihar Kano, ‘Yar Gwagwarmaya Mai kishin Tallafa wa Marayu da iyaye Mata musamman Zawarawa a Jihar Kano.

A tattaunawar ta da Wakilinmu a Kano Abdullahi Muhammad Sheka ta bayyana tsananin damuwar da ta ke tsintar kanta a ciki idan ta tuna irin halin da Marayu da Mata Zawara ke ciki a irin halin rayuwar da ake fama da ita a wannan lokaci, sannan ta bayyana shirin wannan Gidauniya na yunkurin samar da tallafi ga Marayu da sauran masu bukata ta musamman. Ga dai yadda tattaunawar ta Kasance.

  • Obasanjo Ya Roki Marayun Borno Su Yafe Wa ‘Yan Ta’addar Da Suka Kashe Iyayensu

Za mu so mu san wacce muke tare da ita a halin yanzu?
Alhamdulillahi kamar yadda aka sani ni dai, sunana Kwamared Hajiya Rukayya Abdurrahaman haifaffiyar Unguwar Gwagwarwa, Karamar Hukumar Nasarawa a Jihar Kano na yi karatun addinin musamman Alkur’ani, ilimin addini da na zamani gwargwadon ikon, yanzu haka ina ci gaba karatun digiri har da digirgir a fannin tsimi da tanadi a Jami’ar Bayero da ke Kano, sannan kuma ni ce Shugabar Kungiyar Tallafawa Marayu da Zawarawa da cigabansu ta Jihar Kano a halin yanzu.

Marayu

Ganin ke Mace ce kuma kika rungumi wannan tsari na taimakon Marayu da Zawarawa, shin ko me ya ja hankalinki zuwa wannan aikin alhairi?
Kamar yadda na ambata tun a cikin gabatarwar da na yi, na taso a cikin al’umma da ke fama da irin wannan matsala, sannan karatun addini da na yi ya ba ni damar fahimtar muhimmancin tallafa wa Marayu da kuma gagarumin kalubalen da ke addabar wadanda suka tsinci kai a irin wannan hali, babban tashin hankalin shi ne yadda matsalar maraici ke jefa kananan yara harkar shaye-shaye, sace-sace da barace-barace wanda hakan na zubar da kimar addinin mu na Musulunci da al’adunmu. Wannan shi ne abinda kullum idan na tuna ke hana ni runtsawa.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Kwamared yaushe aka kafa wannan kungiya?
Mun kafa wannan kungiya shekaru biyar da suka gabata karkashin Jagorancin Galadiman Kano Alhaji Abbas Sunusi, tare da gudunmawar wasu mashuhuran mutane masu zuciyar taimakon al’umma wanda zuwa yanzu muna da cibiyoyi guda biyu, daya na Unguwar Hotoro gudan kuma na Unguwar Kabuga duk a Jihar Kano

Mene ne ayyukan da kuka fi mayar da hankali akansu?
Alhamdulillahi kamar yadda na ambata akwai taimaka wa Marayu wadanda muke koya masu sana’o’in dogaro da kai, mayar da su Makarantu, sannan da daukar nauyin karatun nasu, hakazalika muna bibiyar lafiyarsu, tare da biya masu kudaden maganunguna. Yanzu haka muna da sama da Marayu 100 da duk mako muke haduwa dasu ana koya masu sana’a tare da koya masu karatun addini da na zamani, sannan muna aamar masu da dan abin sawa a bakin salati.

Marayu

Wanne tanadi wannan kungiya ta yi wa Mata Zawarawa?
Gaskiya lamarin Zawarawa shima lamari ne mai zaman kansa, domin wasu matan mutuwa aka yi aka barsu da Marayu kenan aiki biyu ya samu mace guda ga zawarci ga kula da marayun da aka bar Mata. Wannan tasa daga kafuwar wannan kungiya zuwa yau mun taimakawa zawa sama da dubu biyar, wadanda muke Koyawa sana’u iri daban daban, Kama daga dinki, tursruksn wuta, girke girke, kula rayuwarsu domin gudun afkawa ciki wata mummunar dabi’a, sannan da tallafawa wadanda suka samu mazajen aure tare da bibiyar su domin ganin yadda suke ci gaba kula da sana’o’in da aka koya masu.

Ta yaya wannan kungiya ke samun kudeden gudanar da harkokin ta?
Muna samun tallafi daga hannun wasu mutanen kirki da wasu da bama da son a ambata sunansu, amma dai babu shakka uban wannan kungiya Galadiman Kano da Kwamishinan yada labaran Jihar Kano Kwamared Myhammad Garba babu shakka suna yin bakin kokari kwari da gaske.

Kungiya irin wannan na bukatar matsuguni Wanda zata ci gaba lura da kula da wadannan marayu, shin ko ita wannan kungiyar nada nata matsuguni na dindin?
“Kaji inda gizo ke sakar” yanzu haka maganar da ake amma bamu umarnin hada kayanmu domin ficewa daga gidan da muke gudanar da wannan aikin alhairi za su sayar da kayansu, kuma babbar matsalar ita ce idan aka tashe mu ba mu san inda kuma zamu nufa ba, kenan kaga wannan aikin ya gamu da tasgaro wanda hakan ka iya takaita amfanin da al’umma ke samu karkashin ayyukan wannan kungiya.

Wane kira za ki yi ga mahukunta da masu hannu da shuni domin shigowa cikin wannan aiki alhairi?
Babban kiranmu ga mahukunta da sauran masu bukatar zuba jarinsu a inda ba gara ba zago shi ne, lallai su yi kokarin sayawa wannan kungiya matsuguni domin amfanin marayu, sannan bisa yadda muke fadi tashi a fadin kananan Hukumomin Jihar Kano 44, akwai bukatar samun motar da zamu ci gaba da tiri tiri da wadannan marayu tare da bibiyar Zawarawan da aka koyawa sana’ar dogaro da kai domin ganin suna ci gaba amfanarta, Wanda rashin abin hawa na ragewa aikin namu armashi.

Mene fatan ki na karshe?
Fatan na karshe cikawa da imani, kuma tare da rokon Allah ya karbi wannan kyakkyawan aiki, sannan wadanda ke bayar da gudunmawa suma Allah ya hada mu a ladan.

Mun gode
Nima na gode


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

“Mun Kammala Ayyuka Sama Da 2000” – Fantami

Next Post

2023: Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Rufe NTA, RN, Pride FM, Gamji FM Kan Yada Gangamin PDP

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2 weeks ago
Marayu
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

3 weeks ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

3 weeks ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

4 weeks ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

4 weeks ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 month ago
Next Post
Majalisar Jihar Zamfara Ta Zartar Da Dokar Kariya Ga Masu Bukata Ta Musanman

2023: Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Rufe NTA, RN, Pride FM, Gamji FM Kan Yada Gangamin PDP

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.