• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Na Iya Runtsawa Idan Na Tuna Halin Da Marayu Ke Ciki -Rukayya Abdurrahman

by Sulaiman and Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
in Rahotonni
0
Ba Na Iya Runtsawa Idan Na Tuna Halin Da Marayu Ke Ciki -Rukayya Abdurrahman
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamared Hajiya Rukayya Abdurrahaman wadda akafi sani da Uwar Marayu, Shugabar KungiyarTallafa Wa Marayu da Zawarawa ta Jihar Kano, ‘Yar Gwagwarmaya Mai kishin Tallafa wa Marayu da iyaye Mata musamman Zawarawa a Jihar Kano.

A tattaunawar ta da Wakilinmu a Kano Abdullahi Muhammad Sheka ta bayyana tsananin damuwar da ta ke tsintar kanta a ciki idan ta tuna irin halin da Marayu da Mata Zawara ke ciki a irin halin rayuwar da ake fama da ita a wannan lokaci, sannan ta bayyana shirin wannan Gidauniya na yunkurin samar da tallafi ga Marayu da sauran masu bukata ta musamman. Ga dai yadda tattaunawar ta Kasance.

  • Obasanjo Ya Roki Marayun Borno Su Yafe Wa ‘Yan Ta’addar Da Suka Kashe Iyayensu

Za mu so mu san wacce muke tare da ita a halin yanzu?
Alhamdulillahi kamar yadda aka sani ni dai, sunana Kwamared Hajiya Rukayya Abdurrahaman haifaffiyar Unguwar Gwagwarwa, Karamar Hukumar Nasarawa a Jihar Kano na yi karatun addinin musamman Alkur’ani, ilimin addini da na zamani gwargwadon ikon, yanzu haka ina ci gaba karatun digiri har da digirgir a fannin tsimi da tanadi a Jami’ar Bayero da ke Kano, sannan kuma ni ce Shugabar Kungiyar Tallafawa Marayu da Zawarawa da cigabansu ta Jihar Kano a halin yanzu.

Marayu

Ganin ke Mace ce kuma kika rungumi wannan tsari na taimakon Marayu da Zawarawa, shin ko me ya ja hankalinki zuwa wannan aikin alhairi?
Kamar yadda na ambata tun a cikin gabatarwar da na yi, na taso a cikin al’umma da ke fama da irin wannan matsala, sannan karatun addini da na yi ya ba ni damar fahimtar muhimmancin tallafa wa Marayu da kuma gagarumin kalubalen da ke addabar wadanda suka tsinci kai a irin wannan hali, babban tashin hankalin shi ne yadda matsalar maraici ke jefa kananan yara harkar shaye-shaye, sace-sace da barace-barace wanda hakan na zubar da kimar addinin mu na Musulunci da al’adunmu. Wannan shi ne abinda kullum idan na tuna ke hana ni runtsawa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

Kwamared yaushe aka kafa wannan kungiya?
Mun kafa wannan kungiya shekaru biyar da suka gabata karkashin Jagorancin Galadiman Kano Alhaji Abbas Sunusi, tare da gudunmawar wasu mashuhuran mutane masu zuciyar taimakon al’umma wanda zuwa yanzu muna da cibiyoyi guda biyu, daya na Unguwar Hotoro gudan kuma na Unguwar Kabuga duk a Jihar Kano

Mene ne ayyukan da kuka fi mayar da hankali akansu?
Alhamdulillahi kamar yadda na ambata akwai taimaka wa Marayu wadanda muke koya masu sana’o’in dogaro da kai, mayar da su Makarantu, sannan da daukar nauyin karatun nasu, hakazalika muna bibiyar lafiyarsu, tare da biya masu kudaden maganunguna. Yanzu haka muna da sama da Marayu 100 da duk mako muke haduwa dasu ana koya masu sana’a tare da koya masu karatun addini da na zamani, sannan muna aamar masu da dan abin sawa a bakin salati.

Marayu

Wanne tanadi wannan kungiya ta yi wa Mata Zawarawa?
Gaskiya lamarin Zawarawa shima lamari ne mai zaman kansa, domin wasu matan mutuwa aka yi aka barsu da Marayu kenan aiki biyu ya samu mace guda ga zawarci ga kula da marayun da aka bar Mata. Wannan tasa daga kafuwar wannan kungiya zuwa yau mun taimakawa zawa sama da dubu biyar, wadanda muke Koyawa sana’u iri daban daban, Kama daga dinki, tursruksn wuta, girke girke, kula rayuwarsu domin gudun afkawa ciki wata mummunar dabi’a, sannan da tallafawa wadanda suka samu mazajen aure tare da bibiyar su domin ganin yadda suke ci gaba kula da sana’o’in da aka koya masu.

Ta yaya wannan kungiya ke samun kudeden gudanar da harkokin ta?
Muna samun tallafi daga hannun wasu mutanen kirki da wasu da bama da son a ambata sunansu, amma dai babu shakka uban wannan kungiya Galadiman Kano da Kwamishinan yada labaran Jihar Kano Kwamared Myhammad Garba babu shakka suna yin bakin kokari kwari da gaske.

Kungiya irin wannan na bukatar matsuguni Wanda zata ci gaba lura da kula da wadannan marayu, shin ko ita wannan kungiyar nada nata matsuguni na dindin?
“Kaji inda gizo ke sakar” yanzu haka maganar da ake amma bamu umarnin hada kayanmu domin ficewa daga gidan da muke gudanar da wannan aikin alhairi za su sayar da kayansu, kuma babbar matsalar ita ce idan aka tashe mu ba mu san inda kuma zamu nufa ba, kenan kaga wannan aikin ya gamu da tasgaro wanda hakan ka iya takaita amfanin da al’umma ke samu karkashin ayyukan wannan kungiya.

Wane kira za ki yi ga mahukunta da masu hannu da shuni domin shigowa cikin wannan aiki alhairi?
Babban kiranmu ga mahukunta da sauran masu bukatar zuba jarinsu a inda ba gara ba zago shi ne, lallai su yi kokarin sayawa wannan kungiya matsuguni domin amfanin marayu, sannan bisa yadda muke fadi tashi a fadin kananan Hukumomin Jihar Kano 44, akwai bukatar samun motar da zamu ci gaba da tiri tiri da wadannan marayu tare da bibiyar Zawarawan da aka koyawa sana’ar dogaro da kai domin ganin suna ci gaba amfanarta, Wanda rashin abin hawa na ragewa aikin namu armashi.

Mene fatan ki na karshe?
Fatan na karshe cikawa da imani, kuma tare da rokon Allah ya karbi wannan kyakkyawan aiki, sannan wadanda ke bayar da gudunmawa suma Allah ya hada mu a ladan.

Mun gode
Nima na gode


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

“Mun Kammala Ayyuka Sama Da 2000” – Fantami

Next Post

2023: Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Rufe NTA, RN, Pride FM, Gamji FM Kan Yada Gangamin PDP

Related

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

4 weeks ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

1 month ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

1 month ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Rahotonni

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

1 month ago
Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Rahotonni

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

1 month ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

2 months ago
Next Post
Majalisar Jihar Zamfara Ta Zartar Da Dokar Kariya Ga Masu Bukata Ta Musanman

2023: Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Rufe NTA, RN, Pride FM, Gamji FM Kan Yada Gangamin PDP

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

May 12, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

May 12, 2025
He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

May 12, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

May 12, 2025
Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

May 12, 2025
Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

May 12, 2025
Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

May 12, 2025
Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 12, 2025
NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

May 12, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa

May 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.