• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Na Iya Runtsawa Idan Na Tuna Halin Da Marayu Ke Ciki -Rukayya Abdurrahman

by Sulaiman and Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
Marayu

Kwamared Hajiya Rukayya Abdurrahaman wadda akafi sani da Uwar Marayu, Shugabar KungiyarTallafa Wa Marayu da Zawarawa ta Jihar Kano, ‘Yar Gwagwarmaya Mai kishin Tallafa wa Marayu da iyaye Mata musamman Zawarawa a Jihar Kano.

A tattaunawar ta da Wakilinmu a Kano Abdullahi Muhammad Sheka ta bayyana tsananin damuwar da ta ke tsintar kanta a ciki idan ta tuna irin halin da Marayu da Mata Zawara ke ciki a irin halin rayuwar da ake fama da ita a wannan lokaci, sannan ta bayyana shirin wannan Gidauniya na yunkurin samar da tallafi ga Marayu da sauran masu bukata ta musamman. Ga dai yadda tattaunawar ta Kasance.

  • Obasanjo Ya Roki Marayun Borno Su Yafe Wa ‘Yan Ta’addar Da Suka Kashe Iyayensu

Za mu so mu san wacce muke tare da ita a halin yanzu?
Alhamdulillahi kamar yadda aka sani ni dai, sunana Kwamared Hajiya Rukayya Abdurrahaman haifaffiyar Unguwar Gwagwarwa, Karamar Hukumar Nasarawa a Jihar Kano na yi karatun addinin musamman Alkur’ani, ilimin addini da na zamani gwargwadon ikon, yanzu haka ina ci gaba karatun digiri har da digirgir a fannin tsimi da tanadi a Jami’ar Bayero da ke Kano, sannan kuma ni ce Shugabar Kungiyar Tallafawa Marayu da Zawarawa da cigabansu ta Jihar Kano a halin yanzu.

Marayu

Ganin ke Mace ce kuma kika rungumi wannan tsari na taimakon Marayu da Zawarawa, shin ko me ya ja hankalinki zuwa wannan aikin alhairi?
Kamar yadda na ambata tun a cikin gabatarwar da na yi, na taso a cikin al’umma da ke fama da irin wannan matsala, sannan karatun addini da na yi ya ba ni damar fahimtar muhimmancin tallafa wa Marayu da kuma gagarumin kalubalen da ke addabar wadanda suka tsinci kai a irin wannan hali, babban tashin hankalin shi ne yadda matsalar maraici ke jefa kananan yara harkar shaye-shaye, sace-sace da barace-barace wanda hakan na zubar da kimar addinin mu na Musulunci da al’adunmu. Wannan shi ne abinda kullum idan na tuna ke hana ni runtsawa.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Kwamared yaushe aka kafa wannan kungiya?
Mun kafa wannan kungiya shekaru biyar da suka gabata karkashin Jagorancin Galadiman Kano Alhaji Abbas Sunusi, tare da gudunmawar wasu mashuhuran mutane masu zuciyar taimakon al’umma wanda zuwa yanzu muna da cibiyoyi guda biyu, daya na Unguwar Hotoro gudan kuma na Unguwar Kabuga duk a Jihar Kano

Mene ne ayyukan da kuka fi mayar da hankali akansu?
Alhamdulillahi kamar yadda na ambata akwai taimaka wa Marayu wadanda muke koya masu sana’o’in dogaro da kai, mayar da su Makarantu, sannan da daukar nauyin karatun nasu, hakazalika muna bibiyar lafiyarsu, tare da biya masu kudaden maganunguna. Yanzu haka muna da sama da Marayu 100 da duk mako muke haduwa dasu ana koya masu sana’a tare da koya masu karatun addini da na zamani, sannan muna aamar masu da dan abin sawa a bakin salati.

Marayu

Wanne tanadi wannan kungiya ta yi wa Mata Zawarawa?
Gaskiya lamarin Zawarawa shima lamari ne mai zaman kansa, domin wasu matan mutuwa aka yi aka barsu da Marayu kenan aiki biyu ya samu mace guda ga zawarci ga kula da marayun da aka bar Mata. Wannan tasa daga kafuwar wannan kungiya zuwa yau mun taimakawa zawa sama da dubu biyar, wadanda muke Koyawa sana’u iri daban daban, Kama daga dinki, tursruksn wuta, girke girke, kula rayuwarsu domin gudun afkawa ciki wata mummunar dabi’a, sannan da tallafawa wadanda suka samu mazajen aure tare da bibiyar su domin ganin yadda suke ci gaba kula da sana’o’in da aka koya masu.

Ta yaya wannan kungiya ke samun kudeden gudanar da harkokin ta?
Muna samun tallafi daga hannun wasu mutanen kirki da wasu da bama da son a ambata sunansu, amma dai babu shakka uban wannan kungiya Galadiman Kano da Kwamishinan yada labaran Jihar Kano Kwamared Myhammad Garba babu shakka suna yin bakin kokari kwari da gaske.

Kungiya irin wannan na bukatar matsuguni Wanda zata ci gaba lura da kula da wadannan marayu, shin ko ita wannan kungiyar nada nata matsuguni na dindin?
“Kaji inda gizo ke sakar” yanzu haka maganar da ake amma bamu umarnin hada kayanmu domin ficewa daga gidan da muke gudanar da wannan aikin alhairi za su sayar da kayansu, kuma babbar matsalar ita ce idan aka tashe mu ba mu san inda kuma zamu nufa ba, kenan kaga wannan aikin ya gamu da tasgaro wanda hakan ka iya takaita amfanin da al’umma ke samu karkashin ayyukan wannan kungiya.

Wane kira za ki yi ga mahukunta da masu hannu da shuni domin shigowa cikin wannan aiki alhairi?
Babban kiranmu ga mahukunta da sauran masu bukatar zuba jarinsu a inda ba gara ba zago shi ne, lallai su yi kokarin sayawa wannan kungiya matsuguni domin amfanin marayu, sannan bisa yadda muke fadi tashi a fadin kananan Hukumomin Jihar Kano 44, akwai bukatar samun motar da zamu ci gaba da tiri tiri da wadannan marayu tare da bibiyar Zawarawan da aka koyawa sana’ar dogaro da kai domin ganin suna ci gaba amfanarta, Wanda rashin abin hawa na ragewa aikin namu armashi.

Mene fatan ki na karshe?
Fatan na karshe cikawa da imani, kuma tare da rokon Allah ya karbi wannan kyakkyawan aiki, sannan wadanda ke bayar da gudunmawa suma Allah ya hada mu a ladan.

Mun gode
Nima na gode

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Next Post
Majalisar Jihar Zamfara Ta Zartar Da Dokar Kariya Ga Masu Bukata Ta Musanman

2023: Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Rufe NTA, RN, Pride FM, Gamji FM Kan Yada Gangamin PDP

LABARAI MASU NASABA

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.