ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Na Iya Runtsawa Idan Na Tuna Halin Da Marayu Ke Ciki -Rukayya Abdurrahman

by Sulaiman and Abdullahi Muh'd Sheka
4 years ago
Marayu

Kwamared Hajiya Rukayya Abdurrahaman wadda akafi sani da Uwar Marayu, Shugabar KungiyarTallafa Wa Marayu da Zawarawa ta Jihar Kano, ‘Yar Gwagwarmaya Mai kishin Tallafa wa Marayu da iyaye Mata musamman Zawarawa a Jihar Kano.

A tattaunawar ta da Wakilinmu a Kano Abdullahi Muhammad Sheka ta bayyana tsananin damuwar da ta ke tsintar kanta a ciki idan ta tuna irin halin da Marayu da Mata Zawara ke ciki a irin halin rayuwar da ake fama da ita a wannan lokaci, sannan ta bayyana shirin wannan Gidauniya na yunkurin samar da tallafi ga Marayu da sauran masu bukata ta musamman. Ga dai yadda tattaunawar ta Kasance.

  • Obasanjo Ya Roki Marayun Borno Su Yafe Wa ‘Yan Ta’addar Da Suka Kashe Iyayensu

Za mu so mu san wacce muke tare da ita a halin yanzu?
Alhamdulillahi kamar yadda aka sani ni dai, sunana Kwamared Hajiya Rukayya Abdurrahaman haifaffiyar Unguwar Gwagwarwa, Karamar Hukumar Nasarawa a Jihar Kano na yi karatun addinin musamman Alkur’ani, ilimin addini da na zamani gwargwadon ikon, yanzu haka ina ci gaba karatun digiri har da digirgir a fannin tsimi da tanadi a Jami’ar Bayero da ke Kano, sannan kuma ni ce Shugabar Kungiyar Tallafawa Marayu da Zawarawa da cigabansu ta Jihar Kano a halin yanzu.

ADVERTISEMENT

Marayu

Ganin ke Mace ce kuma kika rungumi wannan tsari na taimakon Marayu da Zawarawa, shin ko me ya ja hankalinki zuwa wannan aikin alhairi?
Kamar yadda na ambata tun a cikin gabatarwar da na yi, na taso a cikin al’umma da ke fama da irin wannan matsala, sannan karatun addini da na yi ya ba ni damar fahimtar muhimmancin tallafa wa Marayu da kuma gagarumin kalubalen da ke addabar wadanda suka tsinci kai a irin wannan hali, babban tashin hankalin shi ne yadda matsalar maraici ke jefa kananan yara harkar shaye-shaye, sace-sace da barace-barace wanda hakan na zubar da kimar addinin mu na Musulunci da al’adunmu. Wannan shi ne abinda kullum idan na tuna ke hana ni runtsawa.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Kwamared yaushe aka kafa wannan kungiya?
Mun kafa wannan kungiya shekaru biyar da suka gabata karkashin Jagorancin Galadiman Kano Alhaji Abbas Sunusi, tare da gudunmawar wasu mashuhuran mutane masu zuciyar taimakon al’umma wanda zuwa yanzu muna da cibiyoyi guda biyu, daya na Unguwar Hotoro gudan kuma na Unguwar Kabuga duk a Jihar Kano

Mene ne ayyukan da kuka fi mayar da hankali akansu?
Alhamdulillahi kamar yadda na ambata akwai taimaka wa Marayu wadanda muke koya masu sana’o’in dogaro da kai, mayar da su Makarantu, sannan da daukar nauyin karatun nasu, hakazalika muna bibiyar lafiyarsu, tare da biya masu kudaden maganunguna. Yanzu haka muna da sama da Marayu 100 da duk mako muke haduwa dasu ana koya masu sana’a tare da koya masu karatun addini da na zamani, sannan muna aamar masu da dan abin sawa a bakin salati.

Marayu

Wanne tanadi wannan kungiya ta yi wa Mata Zawarawa?
Gaskiya lamarin Zawarawa shima lamari ne mai zaman kansa, domin wasu matan mutuwa aka yi aka barsu da Marayu kenan aiki biyu ya samu mace guda ga zawarci ga kula da marayun da aka bar Mata. Wannan tasa daga kafuwar wannan kungiya zuwa yau mun taimakawa zawa sama da dubu biyar, wadanda muke Koyawa sana’u iri daban daban, Kama daga dinki, tursruksn wuta, girke girke, kula rayuwarsu domin gudun afkawa ciki wata mummunar dabi’a, sannan da tallafawa wadanda suka samu mazajen aure tare da bibiyar su domin ganin yadda suke ci gaba kula da sana’o’in da aka koya masu.

Ta yaya wannan kungiya ke samun kudeden gudanar da harkokin ta?
Muna samun tallafi daga hannun wasu mutanen kirki da wasu da bama da son a ambata sunansu, amma dai babu shakka uban wannan kungiya Galadiman Kano da Kwamishinan yada labaran Jihar Kano Kwamared Myhammad Garba babu shakka suna yin bakin kokari kwari da gaske.

Kungiya irin wannan na bukatar matsuguni Wanda zata ci gaba lura da kula da wadannan marayu, shin ko ita wannan kungiyar nada nata matsuguni na dindin?
“Kaji inda gizo ke sakar” yanzu haka maganar da ake amma bamu umarnin hada kayanmu domin ficewa daga gidan da muke gudanar da wannan aikin alhairi za su sayar da kayansu, kuma babbar matsalar ita ce idan aka tashe mu ba mu san inda kuma zamu nufa ba, kenan kaga wannan aikin ya gamu da tasgaro wanda hakan ka iya takaita amfanin da al’umma ke samu karkashin ayyukan wannan kungiya.

Wane kira za ki yi ga mahukunta da masu hannu da shuni domin shigowa cikin wannan aiki alhairi?
Babban kiranmu ga mahukunta da sauran masu bukatar zuba jarinsu a inda ba gara ba zago shi ne, lallai su yi kokarin sayawa wannan kungiya matsuguni domin amfanin marayu, sannan bisa yadda muke fadi tashi a fadin kananan Hukumomin Jihar Kano 44, akwai bukatar samun motar da zamu ci gaba da tiri tiri da wadannan marayu tare da bibiyar Zawarawan da aka koyawa sana’ar dogaro da kai domin ganin suna ci gaba amfanarta, Wanda rashin abin hawa na ragewa aikin namu armashi.

Mene fatan ki na karshe?
Fatan na karshe cikawa da imani, kuma tare da rokon Allah ya karbi wannan kyakkyawan aiki, sannan wadanda ke bayar da gudunmawa suma Allah ya hada mu a ladan.

Mun gode
Nima na gode

Marayu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Marayu
Abdullahi Muh'd Sheka
+ posts Bio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Majalisar Jihar Zamfara Ta Zartar Da Dokar Kariya Ga Masu Bukata Ta Musanman

2023: Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Rufe NTA, RN, Pride FM, Gamji FM Kan Yada Gangamin PDP

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.