Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home WASANNI

Ba Na Son Barcelona Su Dawo Firimiya- WENGER

by Tayo Adelaja
October 9, 2017
in WASANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Mai koyar da ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Arsenal, Arsene Wenger ya bayyana ra’ayinsa na cewar baya goyon bayan raɗe-raɗin da akeyi na cewar, ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barcelona za ta koma gasar Firimiya ta ƙasar Ingila, in har dai yankin Cataloniya ya ɓalle daga ƙasar Sifen.

Yankin na Cataloniya dai yana neman ɓallewa ne daga ƙasar Sifen, domin yakoma cin gashin kansa, yayinda a kwanakin baya aka yi ƙoƙarin kaɗa ƙuri’ar raba gardama, domin ba yankin damar ɓallewa.

samndaads

Ministan wasanni na ƙasar ta Sifen ya bayyana cewar idan har yankin na Cataloniya ya ɓalle daga ƙasar Sifen, to ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barcelona za ta iya komawa gasar Firimiya domin taci gaba  da taka leda.

Akwai ruɗani dai akan idan ƙungiyoyin da suke yankin na Cataloniya zasu koma buga wasa domin ƙungiyoyi uku ne kawai a yankin waɗanda suka haɗa da Barcelona, Espanyol, da kuma Girona.

Ya ƙara da cewar idan hakane ai yakamata yai kawai a dawo da Celtic ko Rangers, tunda sune yan ‘yankin Birtaniya, amma idan har Barcelona ne za su koma Firimiya yana ganin abin bazaiyi tsari ba.

Bugu da ƙari ya ƙara da cewar magoya baya zasu sha wahala wajen zuwa kallon wasa, inda yace yana fatan za’a sasanta lamarin a siyasan ce tunda ai magana ce ta siyasa bata ƙwallon ƙafa ba.

A ƙarshe wenger yayi fatan cewa maganar bazatayi nisa ba, kuma Barcelona zasuyi zaman su a ƙasar Sifen.

Ɗan wasan Barcelona dai, Gerard Pique ya na ɗaya daga cikin masu goyon bayan ɓallewar yankin na Cataloniya daga Sifen, saboda ko a kwanakin baya sai da magoya bayan, ƙasar Sifen suka yiwa ɗan wasan ihu a filin ɗaukar horo da kuma lokacin da ƙasar take buga wasa.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

AC Milan Za Ta Taya Aguiro Idan Sanches Ya Koma Mancity

Next Post

Neymar Na Son EUFA Ta Kori Barcelona Daga Champions League

RelatedPosts

Guardiola

Yanzu Manchester United Ce Kawai Nake Son Karyawa Wuya – Guardiola

by Sulaiman Ibrahim
1 hour ago
0

Kociyan kungiyar kwallon kafa ta Manchester City, Pep Guardiola, ya...

Carlo Ancelotti

Ina Fatan Zuwa Kofin Zakarun Turai A Everton – Carlo Ancelotti

by Sulaiman Ibrahim
1 hour ago
0

Mai horar da ‘yan wasan kungiyar kwallon kafa ta Eberton...

Cavani

Na Dawo Da Karfina – Cavani

by Sulaiman Ibrahim
1 hour ago
0

Dan wasan gaba na kungiyar kwallon kafa ta Manchester United,...

Next Post

Neymar Na Son EUFA Ta Kori Barcelona Daga Champions League

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version