ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wuraren Bayar Da Tallafi Sun Zama Tarkon Mutuwa

by Leadership Hausa
2 years ago
tallafi

Shekaru da dama da suka wuce, wuraren da ake samun mace-macen mutane masu yawa a Nijeriya sune ta hanyar hadurran mota, farmakin ‘yan fashi da makami da kuma rikice-rikicien da suke tasow a tsakanin al’umma, amma kuma a shekaru kamar goma da suka wuce an samu wasu hanyoyin mace-macen da suka hada da ayyukan ta’addanci da na ‘yan ta’adda, garkuwa da mutane da kuma rikice-rikicen makiyaya da manoma, wasu hanyoyin sun kuma hada da na ‘yan kungiyoyin asiri, masu cire sassan mutane domin tsafi da kuma kashe-kashe don tsafi sun zama hanyoyin da ke daukar rayukan mkutane da dama a Nijeriya a wannan lokacin.

A wannan lokacin kuma an lura da cewa, ‘yan Nijeriya da dama suna mutuwa ne a wurane da basu taba yin tunanin zai iya zama musu fagen mutuwa ba, wadannan wurare sune inda ake bayar da tallafi ga al’umma don rage radadin matasalolin tattalin arziki da al’umma suka shiga sakamakon tsare-tsaren tattalin arzikin da kasa ke fuskanta.Wurane ne da mutane ke tururuwa don samun abin da za su sa a bakin salati.

  • Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Fitar Da Miliyan 309.5 Don Tallafawa Ɗaliban Da Ke Karatu a Ƙasashen waje 
  • Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Samar Ya Wuce Misali Ko Damuwar Amurka Ta Wuce Kima?

Wata jami’ar Sibil Difen mai suna Fatima Bala, na daga cikin mutum 10 da suka rasa rayukansu a yayin da turmutsitsin da ya auku a wurin raba kayan tallafin abinci a gidan Sanata Aliyu Magatakardan Wamakko a unguwar Gawon Nama cikin birnin Sakwatto a yayin raba tallafin kayan abincin salla.

ADVERTISEMENT

Rahotannin sun nuna cewa, mutum 30 ne suka ji raunuka daban-daban a turmutsitsin da ya auku a ranar 4 ga watan Afrilu na wannan shekarar.

Yayin da ‘yansanda basu cika daukar matakin hukunci a kan irin wannan lamarin ba, amma jami’yyar PDP a nata bangaren ta nemi a tabbatar da an gudanar da cikakken bincike tare da hukunta wadanda ke da hannu a lamarin, ta kuma yi korafin cewa,wannan ba shi ne karo na farko ba da irin wannan lamarin ke faruwa a gidan tsohon gwamnan wajen raba kayan abinci da nufin tallafa wa al’umma.
“Jami’yyar PDP ta nemi a gudanar da cikakken bincike da nufin samar da tsarin da zai taimaka wajen kiyaye aukuwar irin hakan a nan gaba.

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

“Wannan ba shi ne karo na farko ba da irin wannan ke faruwa a wurin saboda yadda aka kasa yin cikakken tsarin da zai kare rayuwar al’umma”, wannan wani bangare ne na takardar sanarwar da jami’in wasta labarai na jam’iyyar PDP na Jihar Sakwatto, Hassan Sahabi Sanyinnawal, ya sanya wa hannu aka kuma raba wa manema labarai.

Turmutsitsin da ya auku a gidan Sanata Wamakko na daya daga cikin ireirensa da suka faru a sassan kasar nan, wanda ko a watan da ya gabata wannan jaridar ta yi sharhi a kan haka.

Bangaren sharhin da muka yi a wancan lokacin shi ne kamar haka: “A ranar 24 ga watan Fabrairu lokacin da hukumar kwastam ta fara sayar da shinkafar gwamnati a farashi mai sauki wanda aka yi a ofishita da ke Harbey Road, Yaba, a jihar Legas mutum 7 suka mutu sakamakon turmutsitsin da aka samu a kokkarinsu na sayen shinkafar.An samu matsalar ne yayin da al’umma suka yi shawarar balla kofar ofishin suka yi kokarin shiga don yi wasoso a wannan yanayin ne aka tattake wasu, wasu suka suma.

A wani lamari kuma na irin wannan, mutum 7 ne suka mutu a turmutsitsin da ya auku yayin da gidauniyar ‘AYM Shafa Foundation’ ta yi rabon zakka a garin Bauchi ranar Juma’a 24 ga watan Maris 2024.

Yawancin wadanda suka mutu mata da yara ne wadanda suka yi tururuwa zuwa ofishin gidauniyar da ke hanyar Bauchi zuwa Jos domin karbar zakkar naira dubu goma-goma.

Haka kuma a Jihar Nasara, daliban jami’a 2 suka mutu yayin da gwamnatin jihar ke rabon kayan abinci. Gwamnatin jihar ta sa manyan makarantun jihar ne a cikin wadanda za su amfana da tallafin abinci don rage musu radadin tsadar rayuwar da ake fuskanta sakamakon cire tallafin man fetur.

Ire-iren wannan turmutsitsin wajen raba tallafin abinci ba sabon abu ba ne, a shekarar da ta gabata mutum 30 suka mutu a yayin da wata kungiya ta kaddamar da rabon abinci a wata coci a garin Fatakwa ta Jihar Ribas.Turmutsitsin ya samo asali ne sakamakon balla shinge da masu shirya rabon abincin suka sa da mutane suka yi ne a yayin rabon abincin.

Haka kuma rahottanin sun nuna cewa, gidauniyar ‘Shafa Foundation’ ta yi irin wannan rabon a watan Ramadan inda wasu mutane suka jikkata.”

A matsayinmu na gidan jarida, muna ganin lamarin a matsayin abin takaici ta yadda irin wannan abin na faruwa amma a ce dukkan jami’an tsaromu su kasa daukar mataki na bincike ko daukar mataki har sai wata jam’iyya da yi korafi.A bayyana lamarin yake kuma cewa, yawancin irin wannan rabon abincin da ake yi a gaban jami’an tsaro ake yin shi.

Muna kara jaddada kiran cewa, duk wata kungiyar da ke shirin bayar da irin wannan tallafin ya kamata ta dauki matakan da suka kamata na kare aukuwar turmutsitsin da zai kai ga rasa rayuwar al’umma.Muna kuma kara jaddada kiran da jam’iyyar PDP ta yi na bukatar ‘yansanda su gudanar da bincike domin gano irin sakacin da aka yi da nufin hukunta duk wadanda yake da hannu wajen mutuwar mutane a wajen rabon tallafin abinci.

A kasa kamar Nijeriya da tsare-tsare gwamnati suka talauta al’ummarta da dama,dole ne a kwana da sanin cewa, duk wata yekuwar bayar da tallafi zata tattaro al’umma masu yawa saboda haka ya kamata a yi isasshen shirin kare rayuwar al’umma.

tallafi
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Next Post
Neja

Wasu Yara Da Suka Kulle Kansu A Tsohuwar Mota Sun Rasu A Neja

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.