• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Zamu Rufe Rijistar Zabe Ba Har Sai Abinda Hali Ya Yi – Shugaban INEC

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Ba Zamu Rufe Rijistar Zabe Ba Har Sai Abinda Hali Ya Yi – Shugaban INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya bayyana cewa ba za a rufe rajistar zaɓe ba har sai hukumar ta gamsu da cewa jama’a sun yi amfani da damar ƙarin wa’adin da za ta yi, sun yi rajista sosai.

Yakubu ya ce saboda haka mutane su kwantar da hankalin su, INEC ba za ta rufe yin rajistar zaɓe ba a ranar 30 ga Yuni, 2022.

  • 2023: INEC Ta Kara Wa’adin Yin Rajistar Katin Zabe

Shugaban ya yi wannan albishir ne yayin da ya ke wa dandazon matasa jawabi a Tsohon Dandalin Fareti a Abuja.

Inec
Shugaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, Kwamishinonin hukumar, Sakataren Hukumar, tare da sauran jama’a a wurin taron da ya gudana a tsohon filin fareti na kasa da ke Abuja

Matasan dai sun taru ne domin halartar gangamin wayar wa da matasa kai kan muhimmancin yin rajista.

INEC ce ta shirya gangamin tare da haɗin-gwiwar ƙungiyar bin diddigin zaɓe ta ‘Yiaga Africa’, kuma Ƙungiyar Tarayyar Turai ce ta ɗauki nauyin shirya taron.

Labarai Masu Nasaba

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

A jawabin sa da ya ke yi a ranar Asabar, Yakubu ya ce, “Ku na so ku sani ko INEC za ta rufe yin rajista nan da kwanaki biyar? To a madadin INEC ina tabbatar maku da cewa ba za a rufe rajista ba har sai mun gamsu da cewa yawan jama’ar da mu ke son ganin sun mallaki rajistar zaɓe duk sun samu dama sun yi rajista.”

Yakubu ya ce nan ba da daɗewa ba INEC za ta fitar ranar da za daina rajista.

Yayin da ya ke ƙarin haske kan cigaban da ake samu wajen aikin rajista, ya ce a cikin kwana biyar cakal da ake rajista a cikin Tsohon Filin Fareti, an yi wa mutum fiye da 14,000 rajista.

A wani labarin makamancin wannan, Farfesa Yakubu ya jaddada cewa INEC za ta ƙara yawan na’urorin rajistar zaɓe a dukkan jihohin ƙasar nan.

Ya ce INEC za ta ƙara wa’adin yin rajista domin tabbatar da cewa ta bai wa ɗimbin ‘yan Nijeriya isasshen lokacin yin rajista, ta yadda jama’a da dama za su samu jefa ƙuri’a a zaɓen 2023.

Inec

Ya ce: “Mun raba ƙarin na’urorin yin rajista zuwa jihohi a wannan makon, kuma yanzu ma za a ƙara aikawa da su a wasu wuraren tsakanin Litinin zuwa Juma’a.”

Lokacin da ya ke amsa jinjinar da dandazon matasa su ka riƙa yi, su na cewa, “Ba ma son maguɗin zaɓe”, Yakubu ya tabbatar masu da cewa, “Zaɓen gwamnan Jihar Ekiti da aka yi a makon jiya ya yi kyau. Na gwamnan Jihar Osun da za a yi nan gaba zai fi na Osun kyau. Shi kuma zaɓen 2023 zai fi kowane sahihanci.”

Inec

A jawabin sa, Jakaden Tarayyar Turai a Najeriya da ECOWAS, Samuel Isipi, ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da kada su riƙa sayar da ƙuri’un su ga ‘yan siyasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Aka Tilastawa Tsohon Alkalin-alkalai Tanko Yin Murabus Din Dole

Next Post

PDP Ta Ja Kunnen Tsohon Shugaban Kasa, Obasanjo Kan Dan Takararta

Related

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME
Ilimi

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

10 minutes ago
Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja
Kiwon Lafiya

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

2 hours ago
Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida
Manyan Labarai

Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

3 hours ago
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩
Manyan Labarai

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

15 hours ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

15 hours ago
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama
Manyan Labarai

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

16 hours ago
Next Post
PDP Ta Ja Kunnen Tsohon Shugaban Kasa, Obasanjo Kan Dan Takararta

PDP Ta Ja Kunnen Tsohon Shugaban Kasa, Obasanjo Kan Dan Takararta

LABARAI MASU NASABA

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

September 8, 2025
Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

September 8, 2025
Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

September 8, 2025
Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

September 7, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

September 7, 2025
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

September 7, 2025
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.