• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babbar Sallah: Bana Raguna Sun Gagari Kundila

•Layya Sai Wane Da Wane

by Bello Hamza and Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
in Rahotonni
0
rago
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ga dukkan alamu a bikin Babbar Sallar bana raguna sun gagari kundela bisa la’akari da yadda farashinsu ya ninninka fiye da na ‘yan shekarun da suka gabata. Wannan kuwa ya auku ne sakamakon yadda ake samun hauhawar farashin kayan masarufi da sauran abubuwa na rayuwa a ‘yan kwanakin nan.

Al’amarin ya yi matukar tayar da hankalin masu karamin karfi. A bara an yi kuka da yadda farashin rago ya fi karfin talaka amma a wannan shekarar lamarin raguna sun gagari kundila, layya ta zama sai wane da wane.

  • Ra’ayoyinku A Kan Tsadar Ragunan Layya A Wannan Shekarar (Ra’ayi)

Wasu wakalinmu sun duba mana yadda farashin yake a garuruwansu, ga kuma rahoton da suka aiko mana dangane da wannan dan karen tsada da ragunan suka yi.

Babbar Sallar bana, Sallar da Yara ke yawan yi wa wakar cewa, “Gobe sallah za mu ci naman damushere” kila a wannan karon Sallar za a yi ta kadamus. Musamman ganin yadda dabbobi Suka yi matukar tsada, wadda a wannan Shekarar Kafi Zurun ma na neman gagarar matsakaicin Talaka.

Irin Kano birni ne da ke yin cikar kwari a duk lokutan sallah irin wanan, amma a wannan lokaci sakamakon matsin tattalin arziki da tsadar dabbobi yasa har yanzu Kasuwannin kamar an yi ruwa an dauke, Kasuwar Dabbobi ta Unguwa uku ita ce Kasuwar da a hukumance ke gudanar da harkokin ta bisa Sahalewar Gwamnati, amma sauran kasuwannin duk suna cin tasu Kasuwar ne a matsayin ‘yan share wuri zauna kawai.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Yanzu haka duk inda ka zaga a kwaryar birnin zaka tarar da an bude Kasuwannin tsaye da aka kasa dabbobi domin neman masu saya, Baya ga dabbobin da ake shiga da su lungu da sakon Kasuwanni da rukunin ungawanin masu hannu da shuni ko za a dace da mai saye.

Kamar yadda LEADERSHIP HAUSA ta samu zarafin tattaunawa da wani dillalin dabbobi a Kasuwar Dabbobi ta Unguwa Uku Malam Idi Sheka cewa ya yi, “Mukam har yanzu mun kasa rarrabewa tsakanin barcin makaho, ga dai dabbobi kamar abayar kyauta, sai dan karen tsada ga kuma rashin masaya, dan dalon sa wanda a shekarun baya idan ka baiwa wani irinsa ma ce a zai yi bai isa layya ba, amma yanzu shi ne farashinsa ya fara daga Dubu 150,000.00 zuwa sama yayin da turkakken ake maganar Miliyon daya harda doriya.

Wani abu da yafi daukar hankali shi ne yadda ake kyautata zaton kasuwar Rakuma ce za ta fi ci a wannan karon, domin da yawa Rakuna sunfi shanu rangwame. Haka lamarin yake a bangaren Raguna, Wanda Idon LEADERSHIP ya gane mata Ragon Naira Dubu 600,000.00 zuwa sama. Yayin da ake samun can matunbirin Rakumin Naira Dubu dari da doriya.

Duk da cewa Ma’aikatan Gwamnatin sai cikin wannan satin suka fara jin alert, hakan yasa ake ganin masu dan guzuri ka iya tunkarar Kafi Zuru ko kuma neman shiga watanda domin samun dan abinda za a dan jefa a miyar Salla.

Sai dai kuma kasuwar masu sayar da kaskon suya da matsamin Nama sun baje kolinsu bisa fatan suma suci kasuwarsu, Haka lamarin yake bangaren masu albasa sun kasa sun tsare itama albasar tana dan Karen tsada duk domin gabatowar Sallar.

Suma ‘yan siyasar da irin wannan lokaci suke rabon raguna ga abokan siyasarsu, masoya da Kuma masu rabo, Amma har yanzu shiru kake hi Wai Malam yaci shirwa, bil hasali ma tuni suke ta sulalewa zuwa Kasa Mai tsarki domin gudanar da aikin Hajjin.

Al’umma Su Yi Hidima Daidai Karfinsu
Wani Malamin addnin Musuluncin a garin Samarun Zariya mai suna Malam Lukman Alfah ya bayyana cewa, yakamata al’umma su fahinci cewa, al’amarin layya kamar sauran ibadojin da Allah (SWT) Ya dora mana suna da ka’doji ba wai an barsu mu yi kara zube ba ne, Malam Lukman yana magana ne a kan yadda mutane ke kukan yadda raguna suka yi tashin gwauron zabi, ya ce, Layya ba wajibi bane a kan Musulmi amma Sunnah ce mai karfi da ake so Musulmai su karfafa yinta, ya kuma kamata al’umma su dauki lamarin layya daidai karfinsu, “Yin layya da Rago shi ne almuhimm amma in mutum ba shi da halin yin haka akwai wasu dabbobi da Allah ya halasta yin layya da su, kamar Tunkiya, Bunsuru Rakuma da Shanu, amma an fi karfafa yin layya da Raguna. Ya kuma kara da cewa, Allah Madaukakin Sarki ba Yana dubi ga girmar dabba ko tsadarta bane amma Yana dubi ne ga zuciyar mai layyar, saboda haka yakamata Musulmi ya yi aikin ibadar daidai karfinsa, ”Sai kaga mutum yana tunkarar Ragunan dubu dari ko abin da ya fi haka, bayan akwai raguna daidai karfinsa irin na dubu arba’in zuwa talatin’ in ji shi.

Malam Lukman Alfa ya kuma ce, an sunnanta raba naman layya kashi biyu zuwa uku, a raba wa ‘yan uwa da makwabta a kuma ciyar da iyali sauran, ta haka wadanda basu samu yin layyar ba za su amfana da naman. Daga nan ya nemi gwamnati ta kara kokari a kan kawo karshe matsalar tsaron da ake fuskanta a sassan kasar nan wanda yana daga cikin abubuwan da suka jawo tsadar dabbobi a wanan shekarar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilin Da Ya Sa Ba Zan Binciki Buhari Da Gwamnatocin Baya Ba – Peter Obi

Next Post

An Gano Masu Barbada Gishiri A Kan Abinci Ba Za Su Yi Tsawon Rai Ba

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2 weeks ago
rago
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

3 weeks ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

4 weeks ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

1 month ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

1 month ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 month ago
Next Post
An Gano Masu Barbada Gishiri A Kan Abinci Ba Za Su Yi Tsawon Rai Ba

An Gano Masu Barbada Gishiri A Kan Abinci Ba Za Su Yi Tsawon Rai Ba

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.