• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babbar Sallah: Bana Raguna Sun Gagari Kundila

•Layya Sai Wane Da Wane

by Bello Hamza and Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
in Rahotonni
0
rago
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ga dukkan alamu a bikin Babbar Sallar bana raguna sun gagari kundela bisa la’akari da yadda farashinsu ya ninninka fiye da na ‘yan shekarun da suka gabata. Wannan kuwa ya auku ne sakamakon yadda ake samun hauhawar farashin kayan masarufi da sauran abubuwa na rayuwa a ‘yan kwanakin nan.

Al’amarin ya yi matukar tayar da hankalin masu karamin karfi. A bara an yi kuka da yadda farashin rago ya fi karfin talaka amma a wannan shekarar lamarin raguna sun gagari kundila, layya ta zama sai wane da wane.

  • Ra’ayoyinku A Kan Tsadar Ragunan Layya A Wannan Shekarar (Ra’ayi)

Wasu wakalinmu sun duba mana yadda farashin yake a garuruwansu, ga kuma rahoton da suka aiko mana dangane da wannan dan karen tsada da ragunan suka yi.

Babbar Sallar bana, Sallar da Yara ke yawan yi wa wakar cewa, “Gobe sallah za mu ci naman damushere” kila a wannan karon Sallar za a yi ta kadamus. Musamman ganin yadda dabbobi Suka yi matukar tsada, wadda a wannan Shekarar Kafi Zurun ma na neman gagarar matsakaicin Talaka.

Irin Kano birni ne da ke yin cikar kwari a duk lokutan sallah irin wanan, amma a wannan lokaci sakamakon matsin tattalin arziki da tsadar dabbobi yasa har yanzu Kasuwannin kamar an yi ruwa an dauke, Kasuwar Dabbobi ta Unguwa uku ita ce Kasuwar da a hukumance ke gudanar da harkokin ta bisa Sahalewar Gwamnati, amma sauran kasuwannin duk suna cin tasu Kasuwar ne a matsayin ‘yan share wuri zauna kawai.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

Yanzu haka duk inda ka zaga a kwaryar birnin zaka tarar da an bude Kasuwannin tsaye da aka kasa dabbobi domin neman masu saya, Baya ga dabbobin da ake shiga da su lungu da sakon Kasuwanni da rukunin ungawanin masu hannu da shuni ko za a dace da mai saye.

Kamar yadda LEADERSHIP HAUSA ta samu zarafin tattaunawa da wani dillalin dabbobi a Kasuwar Dabbobi ta Unguwa Uku Malam Idi Sheka cewa ya yi, “Mukam har yanzu mun kasa rarrabewa tsakanin barcin makaho, ga dai dabbobi kamar abayar kyauta, sai dan karen tsada ga kuma rashin masaya, dan dalon sa wanda a shekarun baya idan ka baiwa wani irinsa ma ce a zai yi bai isa layya ba, amma yanzu shi ne farashinsa ya fara daga Dubu 150,000.00 zuwa sama yayin da turkakken ake maganar Miliyon daya harda doriya.

Wani abu da yafi daukar hankali shi ne yadda ake kyautata zaton kasuwar Rakuma ce za ta fi ci a wannan karon, domin da yawa Rakuna sunfi shanu rangwame. Haka lamarin yake a bangaren Raguna, Wanda Idon LEADERSHIP ya gane mata Ragon Naira Dubu 600,000.00 zuwa sama. Yayin da ake samun can matunbirin Rakumin Naira Dubu dari da doriya.

Duk da cewa Ma’aikatan Gwamnatin sai cikin wannan satin suka fara jin alert, hakan yasa ake ganin masu dan guzuri ka iya tunkarar Kafi Zuru ko kuma neman shiga watanda domin samun dan abinda za a dan jefa a miyar Salla.

Sai dai kuma kasuwar masu sayar da kaskon suya da matsamin Nama sun baje kolinsu bisa fatan suma suci kasuwarsu, Haka lamarin yake bangaren masu albasa sun kasa sun tsare itama albasar tana dan Karen tsada duk domin gabatowar Sallar.

Suma ‘yan siyasar da irin wannan lokaci suke rabon raguna ga abokan siyasarsu, masoya da Kuma masu rabo, Amma har yanzu shiru kake hi Wai Malam yaci shirwa, bil hasali ma tuni suke ta sulalewa zuwa Kasa Mai tsarki domin gudanar da aikin Hajjin.

Al’umma Su Yi Hidima Daidai Karfinsu
Wani Malamin addnin Musuluncin a garin Samarun Zariya mai suna Malam Lukman Alfah ya bayyana cewa, yakamata al’umma su fahinci cewa, al’amarin layya kamar sauran ibadojin da Allah (SWT) Ya dora mana suna da ka’doji ba wai an barsu mu yi kara zube ba ne, Malam Lukman yana magana ne a kan yadda mutane ke kukan yadda raguna suka yi tashin gwauron zabi, ya ce, Layya ba wajibi bane a kan Musulmi amma Sunnah ce mai karfi da ake so Musulmai su karfafa yinta, ya kuma kamata al’umma su dauki lamarin layya daidai karfinsu, “Yin layya da Rago shi ne almuhimm amma in mutum ba shi da halin yin haka akwai wasu dabbobi da Allah ya halasta yin layya da su, kamar Tunkiya, Bunsuru Rakuma da Shanu, amma an fi karfafa yin layya da Raguna. Ya kuma kara da cewa, Allah Madaukakin Sarki ba Yana dubi ga girmar dabba ko tsadarta bane amma Yana dubi ne ga zuciyar mai layyar, saboda haka yakamata Musulmi ya yi aikin ibadar daidai karfinsa, ”Sai kaga mutum yana tunkarar Ragunan dubu dari ko abin da ya fi haka, bayan akwai raguna daidai karfinsa irin na dubu arba’in zuwa talatin’ in ji shi.

Malam Lukman Alfa ya kuma ce, an sunnanta raba naman layya kashi biyu zuwa uku, a raba wa ‘yan uwa da makwabta a kuma ciyar da iyali sauran, ta haka wadanda basu samu yin layyar ba za su amfana da naman. Daga nan ya nemi gwamnati ta kara kokari a kan kawo karshe matsalar tsaron da ake fuskanta a sassan kasar nan wanda yana daga cikin abubuwan da suka jawo tsadar dabbobi a wanan shekarar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilin Da Ya Sa Ba Zan Binciki Buhari Da Gwamnatocin Baya Ba – Peter Obi

Next Post

An Gano Masu Barbada Gishiri A Kan Abinci Ba Za Su Yi Tsawon Rai Ba

Related

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

4 weeks ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

1 month ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

1 month ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Rahotonni

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

1 month ago
Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Rahotonni

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

1 month ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

2 months ago
Next Post
An Gano Masu Barbada Gishiri A Kan Abinci Ba Za Su Yi Tsawon Rai Ba

An Gano Masu Barbada Gishiri A Kan Abinci Ba Za Su Yi Tsawon Rai Ba

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.