ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babbar Sallah: Bana Raguna Sun Gagari Kundila

•Layya Sai Wane Da Wane

by Bello Hamza and Abdullahi Muh'd Sheka
4 years ago
rago

Ga dukkan alamu a bikin Babbar Sallar bana raguna sun gagari kundela bisa la’akari da yadda farashinsu ya ninninka fiye da na ‘yan shekarun da suka gabata. Wannan kuwa ya auku ne sakamakon yadda ake samun hauhawar farashin kayan masarufi da sauran abubuwa na rayuwa a ‘yan kwanakin nan.

Al’amarin ya yi matukar tayar da hankalin masu karamin karfi. A bara an yi kuka da yadda farashin rago ya fi karfin talaka amma a wannan shekarar lamarin raguna sun gagari kundila, layya ta zama sai wane da wane.

  • Ra’ayoyinku A Kan Tsadar Ragunan Layya A Wannan Shekarar (Ra’ayi)

Wasu wakalinmu sun duba mana yadda farashin yake a garuruwansu, ga kuma rahoton da suka aiko mana dangane da wannan dan karen tsada da ragunan suka yi.

ADVERTISEMENT

Babbar Sallar bana, Sallar da Yara ke yawan yi wa wakar cewa, “Gobe sallah za mu ci naman damushere” kila a wannan karon Sallar za a yi ta kadamus. Musamman ganin yadda dabbobi Suka yi matukar tsada, wadda a wannan Shekarar Kafi Zurun ma na neman gagarar matsakaicin Talaka.

Irin Kano birni ne da ke yin cikar kwari a duk lokutan sallah irin wanan, amma a wannan lokaci sakamakon matsin tattalin arziki da tsadar dabbobi yasa har yanzu Kasuwannin kamar an yi ruwa an dauke, Kasuwar Dabbobi ta Unguwa uku ita ce Kasuwar da a hukumance ke gudanar da harkokin ta bisa Sahalewar Gwamnati, amma sauran kasuwannin duk suna cin tasu Kasuwar ne a matsayin ‘yan share wuri zauna kawai.

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

Yanzu haka duk inda ka zaga a kwaryar birnin zaka tarar da an bude Kasuwannin tsaye da aka kasa dabbobi domin neman masu saya, Baya ga dabbobin da ake shiga da su lungu da sakon Kasuwanni da rukunin ungawanin masu hannu da shuni ko za a dace da mai saye.

Kamar yadda LEADERSHIP HAUSA ta samu zarafin tattaunawa da wani dillalin dabbobi a Kasuwar Dabbobi ta Unguwa Uku Malam Idi Sheka cewa ya yi, “Mukam har yanzu mun kasa rarrabewa tsakanin barcin makaho, ga dai dabbobi kamar abayar kyauta, sai dan karen tsada ga kuma rashin masaya, dan dalon sa wanda a shekarun baya idan ka baiwa wani irinsa ma ce a zai yi bai isa layya ba, amma yanzu shi ne farashinsa ya fara daga Dubu 150,000.00 zuwa sama yayin da turkakken ake maganar Miliyon daya harda doriya.

Wani abu da yafi daukar hankali shi ne yadda ake kyautata zaton kasuwar Rakuma ce za ta fi ci a wannan karon, domin da yawa Rakuna sunfi shanu rangwame. Haka lamarin yake a bangaren Raguna, Wanda Idon LEADERSHIP ya gane mata Ragon Naira Dubu 600,000.00 zuwa sama. Yayin da ake samun can matunbirin Rakumin Naira Dubu dari da doriya.

Duk da cewa Ma’aikatan Gwamnatin sai cikin wannan satin suka fara jin alert, hakan yasa ake ganin masu dan guzuri ka iya tunkarar Kafi Zuru ko kuma neman shiga watanda domin samun dan abinda za a dan jefa a miyar Salla.

Sai dai kuma kasuwar masu sayar da kaskon suya da matsamin Nama sun baje kolinsu bisa fatan suma suci kasuwarsu, Haka lamarin yake bangaren masu albasa sun kasa sun tsare itama albasar tana dan Karen tsada duk domin gabatowar Sallar.

Suma ‘yan siyasar da irin wannan lokaci suke rabon raguna ga abokan siyasarsu, masoya da Kuma masu rabo, Amma har yanzu shiru kake hi Wai Malam yaci shirwa, bil hasali ma tuni suke ta sulalewa zuwa Kasa Mai tsarki domin gudanar da aikin Hajjin.

Al’umma Su Yi Hidima Daidai Karfinsu
Wani Malamin addnin Musuluncin a garin Samarun Zariya mai suna Malam Lukman Alfah ya bayyana cewa, yakamata al’umma su fahinci cewa, al’amarin layya kamar sauran ibadojin da Allah (SWT) Ya dora mana suna da ka’doji ba wai an barsu mu yi kara zube ba ne, Malam Lukman yana magana ne a kan yadda mutane ke kukan yadda raguna suka yi tashin gwauron zabi, ya ce, Layya ba wajibi bane a kan Musulmi amma Sunnah ce mai karfi da ake so Musulmai su karfafa yinta, ya kuma kamata al’umma su dauki lamarin layya daidai karfinsu, “Yin layya da Rago shi ne almuhimm amma in mutum ba shi da halin yin haka akwai wasu dabbobi da Allah ya halasta yin layya da su, kamar Tunkiya, Bunsuru Rakuma da Shanu, amma an fi karfafa yin layya da Raguna. Ya kuma kara da cewa, Allah Madaukakin Sarki ba Yana dubi ga girmar dabba ko tsadarta bane amma Yana dubi ne ga zuciyar mai layyar, saboda haka yakamata Musulmi ya yi aikin ibadar daidai karfinsa, ”Sai kaga mutum yana tunkarar Ragunan dubu dari ko abin da ya fi haka, bayan akwai raguna daidai karfinsa irin na dubu arba’in zuwa talatin’ in ji shi.

Malam Lukman Alfa ya kuma ce, an sunnanta raba naman layya kashi biyu zuwa uku, a raba wa ‘yan uwa da makwabta a kuma ciyar da iyali sauran, ta haka wadanda basu samu yin layyar ba za su amfana da naman. Daga nan ya nemi gwamnati ta kara kokari a kan kawo karshe matsalar tsaron da ake fuskanta a sassan kasar nan wanda yana daga cikin abubuwan da suka jawo tsadar dabbobi a wanan shekarar.

rago
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja
rago
Abdullahi Muh'd Sheka
+ posts Bio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

MASU ALAKA

rago
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
rago
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
An Gano Masu Barbada Gishiri A Kan Abinci Ba Za Su Yi Tsawon Rai Ba

An Gano Masu Barbada Gishiri A Kan Abinci Ba Za Su Yi Tsawon Rai Ba

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.