• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Abin Da Zai Kawo Min Cikas Wajen Inganta Rayuwar Jama’a – Sadiya Farouq

by Sulaiman
3 years ago
in Rahotonni
0
Babu Abin Da Zai Kawo Min Cikas Wajen Inganta Rayuwar Jama’a – Sadiya Farouq
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ta bayyana cewa duk wani tugu da ‘yan baƙin ciki masu son ganin bayan kyawawan shirye-shiryen inganta rayuwa da gwamnatin Buhari ke yi domin cimma burin ‘yanto ‘yan Nijeriya marasa galihu miliyan 100 daga ƙuncin fatara zuwa shekara ta 2030 ba zai kashe mata ƙarfin gwiwa ba.

Ministar ta bayyana haka ne a martanin da ta yi kan wani rahoto da wasu masu kiran kan su ‘APC Initiative for Good Governance’, wato Ƙungiyar Tabbatar da Nagartaccen Mulki na APC, su ka bayar inda su ka yi iƙirarin wai ta kwashe dukkan Shirye-Shiryen Inganta Rayuwa da ma’aikatar ta ke aiwatarwa na dukkan jihohin ƙasar nan ta kai su Jihar Bauchi.

  • Sauyin Tsarinmu Ya Bamu Nasarar Gudanar Da Zaben Osun – INEC

Ƙungiyar, wadda a Bauchi ta ke, ta yi iƙirarin ne a sanarwar da wani mai suna Nasiru Cigari ya rattaba wa hannu, inda ta ƙara da cewa wai ministar ta bar aikin ofishin ta ta tare a Bauchi domin ta taimaka wa mijin ta, Eya Mashal Abubakar Sadique (mai ritaya) wajen yaƙin neman zaɓen da ya ke yi na zama gwamnan jihar a zaɓen shekarar 2023 a ƙarƙashin tutar jam’iyyar APC.

A martanin da mai taimaka mata ta musamman a aikin jarida, Madam Nneka Ikem Anibeze, ta fitar, ministar ta bayyana cewa ita kan ta wannan ƙungiya, ƙungiyar ƙarya ce domin babu ita, sannan zargin da ta yi wani shiri ne na mugunta haɗi da ƙage.

A cewar ta, “Tun daga lokacin da aka kafa wannan ma’aikata a cikin watan Agusta na shekarar 2019, aƙalla ‘yan Nijeriya miliyan 20 ne su ka amfana da shirye-shirye daban-daban na ma’aikatar. Sun haɗa da matasan da su ka gama jami’a da ma waɗanda ba su gama ba su 1,064,774 waɗanda aka bai wa horo a ƙarƙashin shirin ‘N-Power’, waɗanda a cikin su Jihar Bauchi ta zama ta 11 daga cikin jihohi 36 da Gundumar Babban Birnin Tarayya.

Labarai Masu Nasaba

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Ta ce: “Jihohin da su ka fi amfana su ne Binuwai, Delta, Inugu, FCT, Kaduna, Kano, Legas, Osun, Oyo da Ribas, sannan sai Bauchi.

“A yanzu haka a ƙarƙashin shirin Ciyar Da ‘Yan Makaranta, jimillar yara miliyan 9.9 ‘yan aji 1 zuwa 3 a makarantun firamare na gwamnati 53,000 a duk faɗin ƙasar nan ana ba su abinci mai zafi sau ɗaya a duk ranar da su ka je makaranta, kuma Jihar Bauchi ita ce ta huɗu a yawan makarantun firamare da ke amfana da shirin, wato ta bi bayan jihohin Kano, Binuwai da Kaduna. Haka kuma Kano ta fi kowace jiha yawan yaran da ake ciyarwa, daga ita sai Katsina, Kaduna, Neja, Jigawa, Binuwai, kafin Bauchi.”

Anibeze ta ce ministar, wadda Babban Sakatare ya wakilta, kwanan nan ta ƙaddamar da shirin Agajin Agajin Kuɗi ga Marasa Galihu a ranar 4 ga Yuli, 2022 a garin Oshogbo na Jihar Osun.

Ta ƙara da cewa: “Ya kamata wannan ƙungiyar ƙaryar ta faɗa wa mabiyan ta abin da ya sa Hajiya Sadiya Farouq ba ta fara rabon kuɗin ga mabuƙatan da ke Jihar Bauchi ba.

Ta ce: “Sadiya Umar Farouq ‘yar siyasar Nijeriya ce wadda ba ta damu da ƙabilanci ba, sannan uwa ce kuma matar aure, mai taimakon jama’a kuma Musulmar gaske. Ta na raba kayan agaji daidai wa daida ga talakawa mabuƙata ba tare da la’akari da jihar da mutum ya fito ba ko yaren sa ko addinin sa.

“In ba domin kada a ce mun ƙyale ba, to, da wannan ma’aikata ba ta ɓata lokacin ta da kuzarin ta har ta kula kashi ba wajen maida martani ga wannan ƙazamin rahoton na wannan sakaryar ƙungiyar ta ‘yan neman ganin bayan mutum, to amma mun ga ya dace a gyara ɓarnar da su ke son aikatawa.

“Sadiya Umar Farouq dai ‘yar asalin Jihar Zamfara ce wadda ke auren tsohon Hafsan Hafsoshin Mayaƙan Sama, Eya Mashal Abubakar Sadique. Kasancewar ta matar ɗan Jihar Bauchi ya ba ta damar da duk wata mace ‘yar Bauchi ta ke da ita.

“Saboda haka, wannan ƙungiya mai suna ‘APC Initiative for Good Governance’ wadda ba a san ta ba kuma ba ta da rajista, ba za ta iya hana ta shuka ko cin moriyar wani alheri na cigaban jihar mijin ta ba daidai da haƙƙin jihar a kason da ma’aikatar da ta ke jagoranta ta bayar, kuma duk wata kutungwila da ƙarya da aka shirya ba za su hana ta mara wa mijin ta baya ba a ƙudirin sa na siyasa.

“Babu wani lokaci da Sadiya Umar Farouq ta taɓa karkatar da Shirye-shiryen Inganta Rayuwa na jihohi 36 da Gundumar Birnin Tarayya zuwa Bauchi, kuma ba ta taɓa barin ayyukan ofis da su ka rataya a wuyan ta ba ta koma Bauchi.

“Akasin hakan ma, ta na aiki ba tare da gajiyawa ba kuma bilhaƙƙi da gaskiya wajen tabbatar da cewa babu wani mabuƙaci ɗan Nijeriya da aka bar shi cikin yunwa, tare da nufin ɗaga matsayin su daga inda ta same su.

“Mai girma Minista, jim kaɗan bayan ta ƙaddamar da Shirin Bada Tallafin Kuɗi Ga Mabuƙata, ta tafi Saudiyya domin sauke farali, tare da amincewar mai girma Shugaban Ƙasa, kuma ana sa ran dawowar ta bakin aiki a wannan makon.

“Ba mu damu da yanayin da ƙungiyar ‘APC Initiative for Good Governance’ ta samu kan ta a ciki ba na firgicin ganin martaba da manyan nasarorin da ministar ke samu, domin dai ita babban abin da ke gaban ta shi ne ta sauke nauyin da aka ɗora wa ma’aikatar ta.

“A yayin da Sadiya Umar Farouq ta fuskanci alƙibla tare da jajircewa kan muradin mai girma Shugaban Ƙasa na ƙarfafa rayuwar ‘yan Nijeriya ta hanyar fito da shirye-shirye daban-daban don tabbatar da an kula da kowane mabuƙaci ɗan Nijeriya, sai ga wasu marasa aikin yi waɗanda siyasa ba ta yi da su a Jihar Bauchi, waɗanda ba su da wata gudunmawar alheri da za su iya kawowa, sun koma zaman haifar da rikici maras alfanu, su na haifar da saɓani da rashin jituwa, su na ɓata lokacin su wajen sarar mai girma Minista.

“Su kuwa talakawa mabuƙata, waɗanda saboda su ne aka kafa Ma’aikatar Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, su na murna da kyakkyawan shugabancin da Sadiya Umar Farouq ta ke yi. Ta na aiki tuƙuru domin a rage fatara a ƙasar nan, kamar yadda mai girma Shugaban Ƙasa ya ƙudirci ceto ‘yan Nijeriya miliyan 100 daga ƙangin fatara.

“Ministar, da ma’aikatar ta, ba su damu da irin waɗannan ƙananan maganganun da ake kitsawa ba, kuma ko kaɗan ba za su yi ƙasa a gwiwa ba wajen ƙoƙarin da su ke yi na tabbatar da sun kawo waraka ga mabuƙatan ƙasar nan.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Miji Ya Bar Matarsa, Ya Tsere Tare Da Sabuwar Budurwarsa

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Fasto Bayan Karba Kudin Fansa A Kaduna

Related

Farouq
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

1 hour ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

1 day ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

1 week ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

1 week ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

2 weeks ago
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

2 months ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Kashe Fasto Bayan Karba Kudin Fansa A Kaduna

'Yan Bindiga Sun Kashe Fasto Bayan Karba Kudin Fansa A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Farouq

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.