ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Wanda Ya Bata Wa Wike Rai – Sule Lamido

by Sadiq
3 years ago
Wike

Tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, ya ce babu wanda ya bata wa Gwamna Wike na Jihar Ribas rai, inda ya yi karin haske kan yadda jam’iyyar PDP ya zabi Atiku Abubakar a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar.

Lamido ya yi tsokaci kan rigimar da ke tsakanin Atiku da Wike a wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Channels.

  • Dalilin Da Yasa Ban Halarci Taron NBA Ba – Kwankwaso 
  • Wayar Salula Ta Haddasa Gobara A Gidan Mai A Legas

Ya ce, “Wannan jam’iyya kamar kowace jam’iyya a Nijeriya tana da tsarin mulkinta, ka’idoji da tsare-tsare kuma idan aka duba tsarin da PDP ke yi tun daga matsayin mai ba da shawara har zuwa shugaban majalisar wakilai, Gwamna, Majalisar Dokoki ta Kasa akwai tsare-tsaren da duk majalisa ce ke samar da kowane mataki.

ADVERTISEMENT

“Mutane sun nemi takara; wasu sun yi nasara, wasu kuma sun fadi. Haka kuma a matsayin shugaba da gwamna. To mene ne abun bacin rai game da Wike? A gani na waye ya yi wa Wike laifi? Wane ya bata masa rai? Babu wannan batun. A babban taron jam’iyya da aka yi a Abuja Wike da kansa ya ce an yi sabihin zabe. To mene ne abun bacin rai? Wane ne ya yi laifi? Ina so in sani da farko saboda me yasa Wike ke kawo batun nan?

“Taron ya fitar da dan takara wanda ya lashe zaben fidda-gwani. Idan akwai kuskure taron ne ya bata wa Wike rai, ba kuma shugaban jam’iyya ba.”

LABARAI MASU NASABA

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

Lamido ya bayyana cewa, Wike ba shi da ikon juya siyasa a Jihar Ribas saboda yana matsayin gwamna.

Ya kara da cewa, “Wike mutum ne. Ba na jin saboda shi gwamna ne zai juya mutann Ribas. Mutanen Ribas da dama na yin PDP tun 1999. Ba zai yiwu ya juya yadda yake so ba saboda shi gwamna ne; hakan ba zai iya aiki ba.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC
Manyan Labarai

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa
Siyasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025
Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP
Siyasa

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

November 12, 2025
Next Post
An Shiga Alhinin Kisan Gillar Da Aka Yi Wa Sheikh Goni Aisami Gashuwa, A Yobe

Mai Mala Buni Ya Bai Wa 'Ya'yan Sheikh Aisami Da Aka Yi Wa Kisan Gilla Aiki

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.