• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bagudu Ya Gabatar Da Takardun Shaida A Kotun Sauraren Kararrakin Zabe A Kebbi

by Umar Faruk
2 years ago
in Labarai
0
Bagudu Ya Gabatar Da Takardun Shaida A Kotun Sauraren Kararrakin Zabe A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Abubakar Atiku Bagudu na Jihar Kebbi, ya gabatar da takardun shaida a gaban kotun sauraron kararrakin zabe da ke zamanta a Birnin Kebbi, inda ya ke kalubalantar nasarar lashe zaben Sanata Muhammadu Adamu Aliero, PDP da INEC a gaban kotun ta hanyar lauyansa.

Idan za a tuna dai Bagudu yana kalubalantar nasarar da Sanata Aliero ya samu kan zaben Sanatan Kebbi ta tsakiya da ya gudana a kwanakin baya.

  • Nijeriya Za Ta Yi Kawance Da WHO Kan Rigakafi
  • Gwamnatin Kebbi Za Ta Hada Hannu Da Masanan Masar Wajen Bunkasa Noma Da Kiwo

Ci gaba da gabatar da takardun wani bangare ne na zaman sauraren karar na matakin farko na sauraren karar da ya shigar da kuma neman kotu ta karbe su a matsayar shaida kamar yadda dokar zabe ta tanada.

Lauyan Gwamna Bagudu, Barista Lagalo D. Lagalo, ya ce, “A karamar hukumar Kalgo mun nemi gabatar da fom 32 na EC8A1, amma 30 ne kawai a wurinsu biyu ba su samu ba, sun gabatar da fom guda 8 na EC 8C1. Ya kuma mika fom din EC8C1 na kananan hukumomi guda takwas wadanda su ne suka hada gundumar Kebbi ta tsakiya ta jihar a matsayin wani bangare na takardun shakda ga abin da yake kalubalantar ga zaben na Sanata Muhammadu Adamu Aliero.”

Haka kuma ya gabatar da fom daya na takardar takaitaccen sakamako na EC8B1 watau (summary results sheet) da kuma nau’i daya na EC8E1 bayyana sakamakon zabe. Daga nan sai ya sanar da kotun cewa, “Duk takardun da aka jera a shafi na 28,29, 30,31 da 34 ba su samuwa, amma za a gabatar da su a ranar da za a dawo zaman na gaba,” in ji shi”.

Labarai Masu Nasaba

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

“Duk da haka, har yanzu a karamar hukumar Kalgo mun lissafta fom biyu EC40G (pu) amma daya ne kawai ake samu a mazaba ta uku a runfa ta daya. Ya bayyana wa kotun cewa a zaman na yau abin da suke da shi ke nan. Amma a ranar da aka sanya don dawowa zaman Kotun na gaba za a gabatar da duk takardun da aka bayyana cewa babusu a hannu za a tabbatar da cewa an gabatar da su a gaban kotun.”

Kazalika, Barista Lagalo ya tabbatar wa kotun za a shigar da takardun a ranar da za a dawo zaman Kotun daga bisani kuma ya nemi a dage zaman har zuwa ranar Litinin 15 ga watan Mayu na shekara ta 2023 don kammala gabatar da shedar takardu.

A bangarensu Lauyan sanata Adamu Aliero, Barrister Aminu Hassan a matsayin wadanda ake kara na farko, lauyan PDP a matsayar wadanda ake kara na biyu D.D Dodo SAN wanda lauyan hukumar INEC da ake kara na uku Barrister Magnus Ihejirika ya tsayawa yayin gabatar da shaidar takardun a gabn kotun sun amince da dage cigaba da Shari’ar zuwa ranar Litinin 15 ga watan da muke ciki.

Kotun ta amince da takaddun da aka gabatar a gabanta kuma an yi musu alama azaman Nunin AAB1 zuwa AAB 16, AAB17G, AAB 19 da AAB 20 bi da bi.

Shugabar kotun, Honourable Justice Margret Opara ta ce, “Bisa yarjejeniyar da lauyoyin na dukkan bangarori suka amince an dage sauraren karar zuwa ranar Litinin 15 ga Mayu 2023 don ci gaba da zaman sauraron karar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BaguduKaraKebbiKotu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bayani A Kan Starlink, Da Yadda Tsarinsa Yake

Next Post

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gabatar Da Shawarwarin Daidaita Ci Gaban Alakar Sin Da Turai

Related

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

49 minutes ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

2 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

6 hours ago
Bagudu
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

7 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

8 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

11 hours ago
Next Post
Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gabatar Da Shawarwarin Daidaita Ci Gaban Alakar Sin Da Turai

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gabatar Da Shawarwarin Daidaita Ci Gaban Alakar Sin Da Turai

LABARAI MASU NASABA

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Bagudu

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.