• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bai Kamata A Manta Da Abin Da Ya Faru A Kabul Ba

by CMG Hausa
2 years ago
Kabul

Shekaru biyu ke nan, tun bayan da Amurka ta janye sojojinta daga kasar Afghanistan. A ranar 30 ga watan Agustan shekarar 2021, jirgin saman soja na karshe na Amurka ya tashi daga filin jirgin saman birnin Kabul, wanda ya dasa aya ga yakin Afghanistan da aka kwashe tsawon shekaru 20 ana yinsa.

Yakin da Amurka ta kaddamar a Afghanistan cikin shekaru 20 da suka wuce, ya lalata kasar tare da makomar al’ummarta, tare kuma da hallaka mutane dubu 174, ciki har da fararen hula sama da dubu 30, baya ga kuma miliyoyin al’ummar kasar da suka zama ‘yan gudun hijira.

  • Kasashen Sin Da Afghanistan Da Pakistan Sun Sha Alwashin Karfafa Hadin Gwiwar Inganta Tsaro

Duk da cewa Amurka ta janye sojojinta daga Afghanistan, amma har yanzu tana kakabawa kasar takunkumin tattalin arziki, tare da kwace kudade daga al’ummar kasar, matakan da suka jefa kasar cikin matsalolin jin kai.

A kwanakin baya, majalisar harkokin wajen kasar Amurka ta fitar da wani rahoto na tantance matakan da Amurka ta dauka, na janye sojojinta daga Afghanistan, wanda ya yi suka game da yanayi na rashin tsari da oda wajen kwashe sojojin, amma ba tare da bayyana ainihin abubuwan da ya kamata gwamnatin Amurka ta yi tunani a kansu ba.

Kaddamar da yaki a kan wata kasa mai mulkin kanta, abu ne da ya keta dokokin kasa da kasa, amma ko me ya sa rahoton bai yi bayani a kan hakan ba? Dubun dubatar fararen hula sun hallaka, ko jikkata a sakamakon yakin na tsawon shekaru 20, baya ga tabarbarewar yanayin tsaro da zaman lafiya a yankin. Ko me ya sa rahoton bai yi bayani a kan hakan ba? Amurka ta fake ne da sunan “wanzar da dimokuradiyya”, wajen tsoma baki cikin harkokin gidan wasu kasashe, amma me ya sa rahoton bai yi bayani a kan hakan ba?

LABARAI MASU NASABA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Ba shakka, al’ummun duniya ba za su yi na’am da rahoton ba.

Amurka na daukar kanta a matsayin misali wajen kare hakkin dan Adam da dimokuradiyya, amma ga abin da ta haifar a Afghanistan, da ma sauran sassan duniya. Idan ba ta daina daukar matakai na nuna fin karfi, da ma gyara yadda take tsoma baki cikin harkokin gidan wasu kasashe yadda ta ga dama ba, to, ba shakka, abin da ya faru a Afghanistan zai ci gaba da faruwa a sauran sassan duniya. (Mai Zane:Mustapha Bulama)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal
Daga Birnin Sin

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025
Daga Birnin Sin

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
Next Post
Afirka

Dandalin Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afrika Zai Kara Bunkasa Huldar Bangarorin Biyu A Fannin Aikin Soja

LABARAI MASU NASABA

Kabul

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Matatar dangote

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

October 10, 2025
Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

October 10, 2025
Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

October 10, 2025
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

October 10, 2025
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.