A ƙalla mutane biyar sun mutu yayin da wasu 15 suka jikkata sakamakon fashewar wani bam da ya tashi a jihar Kano a ranar Asabar, 21 ga Yuni, 2025. Jami’an tsaro na ci gaba da binciken lamarin.
Kwamishinan Ƴansandan jihar, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya bayyana cewa fashewar na iya kasancewa bam da Sojoji suke jigila, wanda aka yi samu akasi ya fashe. “Na ga abin kamar bama-baman Sojoji ne suka fashe,” in ji shi.
Daily Trust ta ruwaito cewa an kai waɗanda suka jikkata asibiti da ke kusa da wurin don samun agaji. Binciken farko ya nuna cewa wata babbar mota ce ke ɗauke da kayan fashewar a hanyar zuwa Jihar Yobe.
Har yanzu ba a tabbatar da ko motar Sojoji ce ke ɗauke da bam ɗin ba. Rundunar Ƴansandan ta ce tana ci gaba da bincike don gano musabbabin fashewar.
Kwamishinan ya kuma yi kira ga jama’a da su kwantar da hankalinsu, yana mai cewa za a ba da cikakken bayani bayan an gama binciken.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp