• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bana Satar Mutane, Kashe Su Kawai Nake Yi – Kasurgumin Dan Bindiga, Aleiro 

Aleiro ya ce yaransa ke garkuwa da mutane, shi yafi kwarewa wajen kashe mutane

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai, Rahotonni
0
Bana Satar Mutane, Kashe Su Kawai Nake Yi – Kasurgumin Dan Bindiga, Aleiro 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasurgumin dan bindigar da ya addabi jihohin Zamfara da Katsina, Ado Aleiro, wanda a baya-bayan nan aka yi wa sarautar Sarkin Fulanin ‘Yandoton, ya yi ikirarin cewa ba ya garkuwa da mutane face kawai kisa yake yi.

Nadin sarautar Aleiro wanda shi ne jagoran ‘yan ta’adda a Tsafe da Faskari a jahohin Zamfara da Katsina, ya jawo cece-kuce a fadin kasar nan.

  • Wayar Da Kai: INEC Za Ta Hada Hannu Da Kungiyar ‘Darika Awareness Forum Katsina’ 
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Kansila A Adamawa

Daga bisani gwamnatin jihar ta dakatar da Sarkin garin, Aliyu Marafa, wanda ya bai wa Aleiro sarautar, wanda ake nema ruwa a jallo a makwabciyar jihar Katsina bisa laifin kashe-kashen jama’a.

Gwamnatin Katsina ta bayar da tukuicin Naira miliyan biyar kan bayanan da suka kai ga kama Aleiro, wanda ake zargi da kashe mutane 52 a garin Kadisau da ke karamar hukumar Faskari a shekarar 2019.

Aleiro ya shaida wa BBC cewa ya fusata da Hausawa da gwamnatin Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

Aleiro ya ce yayin da mutanensa ke garkuwa da mutane, shi kuma ya fi sha’awar kashe mutane ne kawai.

“Mutane ke garkuwa da mutane; ni ina zuwa na kashe su ne (mutane),” in ji Aleiro.

Wani na hannun daman Aleiro da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida wa tawagar ‘BBC Africa Eye’ cewa “An cire Fulani daga ayyukan gwamnati da sauran abubuwan da suma shafi tattalin arziki, kuma sojojin saman Nijeriya na kai hari ga Fulani makiyaya da kuma kashe musu shanu.

“Ta yaya Fulani suka zama marasa kima haka a Nijeriya?” Kamar yadda ya tambaya.

Ya koka da yadda aka rufe hanyoyin kiwo, wanda da su Fulani suka dogara yayin da kasa da ruwa suka yi karanci.

Mun Sayi Makamai Da Yawa – Wadanda Suka Sace Daliban Makarantar Jangebe

BBC ta kuma yi hira da ‘yan ta’addan da suka sace daliban makarantar sakandaren mata ta gwamnati da ke Jangebe a karamar hukumar Talata Mafara a jihar Zamfara.

Yayin da gwamnatin jihar ta ce ba ta biya kudin fansar daliban mata ba, wani dan bindiga da ba a bayyana sunansa ba, ya ce an biyansu Naira miliyan 60 kafin su sako daliban.

Da aka tambaye shi me suka yi da kudin, sai ya ce, “Mun kara sayen bindigogi.”

An kuma fitar da al’amuran da suka tada hankali ciki har da na wani yaro da ya mutu sakamakon harbin bindiga a lokacin da suka sace daliban.

“Na tuna yadda ya daga kai ya dube ni yayin da yake cikin wannan hali,” mahaifin yaron ya shaida wa BBC.

“Abun ya min zafi yadda yarona ya sha wahala…Na yi bakin ciki.”

BBC ta tattaro cewa matashin wanda ‘yar uwarsa na cikin ‘yan matan makarantar Jangebe da aka sace, jami’an tsaro ne suka kashe shi.

Wani bangare na binciken da tawagar ‘Documentary’ ta gudanar, shi ne yadda al’ummar Hausawa ke ci gaba da zaluntar al’ummar Fulani, wanda ya bayyana a haduwar tawagar da mazauna yankin Kurfar Danya.

“Idan aka yarda, za mu kashe kowane Bafulatani, ko da a cikin gari ne,” in ji wani daga cikin ‘yan banga, “saboda sun kashe iyayenmu, yaranmu, sun jefar da gawarwakinsu a nan.”

Wani mazaunin garin ya bayyana rashin amincewa da kisan da ‘yan ta’adda suka yi wa mutane sama da 200.

Mazauna yankin sun kai dan jaridar BBC zuwa wuraren da birne mutane.

Haka zalika an kara tabbatar da cewa tashe-tashen hankula a yankin na da nasaba da daukar fansa, maimakon kariya.

Kungiyoyin ’yan banga galibi mazauna al’ummar Hausawa ne.

“A bayyane yake cewa kabilanci ne,” in ji Hassan, wani dan ta’adda wanda yana daya daga cikin Fulanin farko da suka fara shigo da bindigogi cikin Zamfara tare da daukar makamai karkashin wata kungiyar ta’addanci.

“Idan ba haka ba, me zai sa Bafulatani ya kashe Bahaushe wanda bai masa komai? A bayyane abun yake, rikici ne na kabilanci.”

An sha yin maganganu cewar hare-haren ‘yan bindiga a wasu jihohin arewa maso yamma na da alaka da rikicin kabilanci ko kuma daukar fansa, wanda hakan ta fi faruwa a tsakanin ‘yan bindigar da ‘yan banga ko kuma ‘yan sa-kai a jihohin Zamfara da Katsina.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Banga'Yan Sa-Kai'YantodoAdo AleiroKatsinaSarautaSatar mutaneZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hamshakin Dillalin Kwayoyi Ya Shiga Hannu A Jigawa

Next Post

Fulani Sun Kulla Yarjejeniyar Zaman Lafiya Da Kabilar Irigwe A Jihar Filato

Related

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

46 minutes ago
Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

3 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

9 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

21 hours ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

22 hours ago
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA
Manyan Labarai

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

1 day ago
Next Post
Fulani Sun Kulla Yarjejeniyar Zaman Lafiya Da Kabilar Irigwe A Jihar Filato

Fulani Sun Kulla Yarjejeniyar Zaman Lafiya Da Kabilar Irigwe A Jihar Filato

LABARAI MASU NASABA

Kwanciyar Aure

Yadda Hadarin Mutuwa Ke Karuwa Yayin Ko Bayan Saduwa Da Iyali

July 26, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Himmatuwa Wajen Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Himmatuwa Wajen Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

July 26, 2025
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

July 26, 2025
‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

July 26, 2025
Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

July 26, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

July 26, 2025
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

July 26, 2025
Kotu

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

July 26, 2025
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.