• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bana Satar Mutane, Kashe Su Kawai Nake Yi – Kasurgumin Dan Bindiga, Aleiro 

Aleiro ya ce yaransa ke garkuwa da mutane, shi yafi kwarewa wajen kashe mutane

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai, Rahotonni
0
Bana Satar Mutane, Kashe Su Kawai Nake Yi – Kasurgumin Dan Bindiga, Aleiro 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasurgumin dan bindigar da ya addabi jihohin Zamfara da Katsina, Ado Aleiro, wanda a baya-bayan nan aka yi wa sarautar Sarkin Fulanin ‘Yandoton, ya yi ikirarin cewa ba ya garkuwa da mutane face kawai kisa yake yi.

Nadin sarautar Aleiro wanda shi ne jagoran ‘yan ta’adda a Tsafe da Faskari a jahohin Zamfara da Katsina, ya jawo cece-kuce a fadin kasar nan.

  • Wayar Da Kai: INEC Za Ta Hada Hannu Da Kungiyar ‘Darika Awareness Forum Katsina’ 
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Kansila A Adamawa

Daga bisani gwamnatin jihar ta dakatar da Sarkin garin, Aliyu Marafa, wanda ya bai wa Aleiro sarautar, wanda ake nema ruwa a jallo a makwabciyar jihar Katsina bisa laifin kashe-kashen jama’a.

Gwamnatin Katsina ta bayar da tukuicin Naira miliyan biyar kan bayanan da suka kai ga kama Aleiro, wanda ake zargi da kashe mutane 52 a garin Kadisau da ke karamar hukumar Faskari a shekarar 2019.

Aleiro ya shaida wa BBC cewa ya fusata da Hausawa da gwamnatin Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

Aleiro ya ce yayin da mutanensa ke garkuwa da mutane, shi kuma ya fi sha’awar kashe mutane ne kawai.

“Mutane ke garkuwa da mutane; ni ina zuwa na kashe su ne (mutane),” in ji Aleiro.

Wani na hannun daman Aleiro da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida wa tawagar ‘BBC Africa Eye’ cewa “An cire Fulani daga ayyukan gwamnati da sauran abubuwan da suma shafi tattalin arziki, kuma sojojin saman Nijeriya na kai hari ga Fulani makiyaya da kuma kashe musu shanu.

“Ta yaya Fulani suka zama marasa kima haka a Nijeriya?” Kamar yadda ya tambaya.

Ya koka da yadda aka rufe hanyoyin kiwo, wanda da su Fulani suka dogara yayin da kasa da ruwa suka yi karanci.

Mun Sayi Makamai Da Yawa – Wadanda Suka Sace Daliban Makarantar Jangebe

BBC ta kuma yi hira da ‘yan ta’addan da suka sace daliban makarantar sakandaren mata ta gwamnati da ke Jangebe a karamar hukumar Talata Mafara a jihar Zamfara.

Yayin da gwamnatin jihar ta ce ba ta biya kudin fansar daliban mata ba, wani dan bindiga da ba a bayyana sunansa ba, ya ce an biyansu Naira miliyan 60 kafin su sako daliban.

Da aka tambaye shi me suka yi da kudin, sai ya ce, “Mun kara sayen bindigogi.”

An kuma fitar da al’amuran da suka tada hankali ciki har da na wani yaro da ya mutu sakamakon harbin bindiga a lokacin da suka sace daliban.

“Na tuna yadda ya daga kai ya dube ni yayin da yake cikin wannan hali,” mahaifin yaron ya shaida wa BBC.

“Abun ya min zafi yadda yarona ya sha wahala…Na yi bakin ciki.”

BBC ta tattaro cewa matashin wanda ‘yar uwarsa na cikin ‘yan matan makarantar Jangebe da aka sace, jami’an tsaro ne suka kashe shi.

Wani bangare na binciken da tawagar ‘Documentary’ ta gudanar, shi ne yadda al’ummar Hausawa ke ci gaba da zaluntar al’ummar Fulani, wanda ya bayyana a haduwar tawagar da mazauna yankin Kurfar Danya.

“Idan aka yarda, za mu kashe kowane Bafulatani, ko da a cikin gari ne,” in ji wani daga cikin ‘yan banga, “saboda sun kashe iyayenmu, yaranmu, sun jefar da gawarwakinsu a nan.”

Wani mazaunin garin ya bayyana rashin amincewa da kisan da ‘yan ta’adda suka yi wa mutane sama da 200.

Mazauna yankin sun kai dan jaridar BBC zuwa wuraren da birne mutane.

Haka zalika an kara tabbatar da cewa tashe-tashen hankula a yankin na da nasaba da daukar fansa, maimakon kariya.

Kungiyoyin ’yan banga galibi mazauna al’ummar Hausawa ne.

“A bayyane yake cewa kabilanci ne,” in ji Hassan, wani dan ta’adda wanda yana daya daga cikin Fulanin farko da suka fara shigo da bindigogi cikin Zamfara tare da daukar makamai karkashin wata kungiyar ta’addanci.

“Idan ba haka ba, me zai sa Bafulatani ya kashe Bahaushe wanda bai masa komai? A bayyane abun yake, rikici ne na kabilanci.”

An sha yin maganganu cewar hare-haren ‘yan bindiga a wasu jihohin arewa maso yamma na da alaka da rikicin kabilanci ko kuma daukar fansa, wanda hakan ta fi faruwa a tsakanin ‘yan bindigar da ‘yan banga ko kuma ‘yan sa-kai a jihohin Zamfara da Katsina.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Banga'Yan Sa-Kai'YantodoAdo AleiroKatsinaSarautaSatar mutaneZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hamshakin Dillalin Kwayoyi Ya Shiga Hannu A Jigawa

Next Post

Fulani Sun Kulla Yarjejeniyar Zaman Lafiya Da Kabilar Irigwe A Jihar Filato

Related

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

13 hours ago
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

16 hours ago
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027
Siyasa

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

22 hours ago
Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19
Manyan Labarai

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

23 hours ago
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Boko Haram 5, Sun Kwato Makamai A Borno

2 days ago
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano
Manyan Labarai

2027: PDP Ta Mutu, APC Na Shirin Sake Yin Nasara – Martanin Ganduje Ga Lamido 

2 days ago
Next Post
Fulani Sun Kulla Yarjejeniyar Zaman Lafiya Da Kabilar Irigwe A Jihar Filato

Fulani Sun Kulla Yarjejeniyar Zaman Lafiya Da Kabilar Irigwe A Jihar Filato

LABARAI MASU NASABA

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 13, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

May 13, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.