• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Batun Kare Martabar Kyawawan Al’adun Hausawa

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
in Rahotonni
0
Batun Kare Martabar Kyawawan Al’adun Hausawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Fili na musamman domin makaranta, wanda zai rika ba wa kowa damar tofa albarkacin bakinsa kan abin da ya dame shi cikin zuciya, na rayywar yau da kullum, ko makamancin haka.

Filin namu na yau yana tafe da bayanin Abba Abubakar Yakubu, dangane da abin da ya dame shi cikin zuciya. Inda ya fara da cewa:

  • Ra’ayoyinku A Kan Batun Hako Man Fetur A Yankin Bauchi Da Gombe
  • Yadda Za A Kula Da Tafin Kafa Lokacin Hunturu

“Al’adun da kuke kyama, yanzu sun zama abin kwalliyar ku, saura ku karbi addininmu!”. Wadannan wasu kalamai ne na izgili da wani wanda ba musulmi ba ya rubuta a kasan jikin wani hoton wasu ma’aurata sabbin aure, wato Ango da Amarya, wanda aka dauka lokacin wani shagalin bikin aure.

Yanayin hoton ya nuna Angon cikin shigar kananan kaya ya sa kwat da wando da madaurin wuya, yayin da ita kuma Amaryar ta sanya farar rigar leshi da siffar dinkin Amaren turawa, kai ka ce dai bikin na wadanda ba musulmi ba ne.

Ba su kadai ba, hatta ga sauran abokai da kawayen Amarya ma duk irin wannan shiga ta kananan kaya suka yi, wasu ma kansu babu kallabi. Sai dai mai yiwuwa ka yi mamakin jin cewa, wannan Amarya da Ango ‘Ya’yan Musulmi ne, kuma ma cikakkun Hausawa ne, Amina da Bashir.

Labarai Masu Nasaba

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Ko da yake da gani ka san biki ne na wasu ‘ya’yan masu hannu da shuni, ‘yan siyasa ko wasu hamshakan ‘yan boko, saboda irin yadda aka kawata wajen bikin da kuma irin manyan mawakan da aka gayyata daga kudancin kasar nan.

Ba ina nufin yin irin wannan shigar ta sabawa koyarwar addini ba ne, wannan hakkin malamai ne su inganta ko su tsawatar a kai, amma ni abin da ya fi daukar hankalina shi ne; kayan da suka sa sun sabawa bikin aure na al’adar Bahaushe. Idan mun lura, saboda sabawar ce ma har wani yake ganin, saura kiris a ajiye addinin ma a gefe.

Na fara rubutu na da wannan salo ne domin nuna mana irin lalacewar da al’adun Malam Bahaushe suka samu kansu a ciki, musamman a bangaren bikin aure, kuma abin takaici masu fada a ji daga cikin al’ummar Arewa na daga wadanda ke kara angiza irin wannan lalacewar tarbiyya da al’ada.

Abin takaici ne yau ka je wajen bikin ‘ya’yan manyan kasar nan ka ga irin bidi’o’in da aka shirya da abubuwan da ake gudanarwa da sunan biki, wadanda ko kusa ba su yi kama da na Hausawa ba, kuma ma ba su dace da koyarwar addini ba.

Idan mai karatu ya lura da kalaman da na rubuta a farkon wannan sharhin na san zai yi tunanin lallai sauran abokan zaman mu su kansu suna mamakin yadda garin kwaikwayonsu da muke yi har mun kusa wuce makadi da rawa.

Kalaman da aka yi amfani da su a farkon wannan rubutu ba kirkira ba ne, tabbas! haka wani ya rubuta a shafin Instagram na wasu masu biki da suka sa hotunan auren su.

Ashe kenan idan har wadanda ba Hausawa ba za su rika mamakin yadda rayuwar mu ta canza, muka manta da namu kyawawan al’adun muka koma kwaikwayon wasu, za mu yi takaici da cizon yatsa kan wasu abubuwan da ke faruwa a rayuwar akasarin Hausawa ko ‘yan Arewa, ba kawai a sha’anin biki ba, har ma da sauran harkokin mu na rayuwa.

Matasa da iyayensu sun rungumi wasu halaye da suka saba da asalin tarbiyya, yakana, kunya da mutunta kai da aka san Hausawa da su.

Haka mutum zai yi ta ganin wasu abubuwan takaici da ke faruwa, tsakanin masu shirin aure, wanda ake kira hotunan kafin biki (Pre-Wedding Pictures), wani salon daukar hoto na ‘yan zamani.

Yadda za ka ga masoyan ko masu shirin auren na rungumar junansu, sumbatar juna da wasu sassan jikinsu, za ka rantse ma’aurata ne, sun yi aure tuni, ba wai shirin auren suke yi ba. To, in ma auren suka yi, haka addinin Musulunci da al’adar mu ta koyar a rika yi, don bayyana soyayya da burge mutane?.

Wasa a hankali muna kara yin baya baya da tarbiyyar mu ta addini da wanda iyaye da magabatan mu na kwarai suka dora mu a kai.

Muna rungumar wasu al’adu da ba su dace ba, kuma wata rana za mu ji kunyar a danganta mu da su, musamman idan yaran mu suka taso suka ga abubuwan da muka aikata a lokacin kuruciyar mu. Wanne abin koyi muke bar musu? Wacce rayuwa muke fatan su yi nan gaba, a matsayin su na manyan gobe?

Daga Abba Abubakar Yakubu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Al'adun HausawaAureBiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsokaci A Kan Mazan Da Ba Su Yi Wa Matansu Kwalliya A Gida

Next Post

An Rantsar Da Ademola Adeleke A Matsayin Gwamnan Osun Na 6

Related

Hausawa
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

6 hours ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

1 day ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

1 week ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

1 week ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

2 weeks ago
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

2 months ago
Next Post
An Rantsar Da Ademola Adeleke A Matsayin Gwamnan Osun Na 6

An Rantsar Da Ademola Adeleke A Matsayin Gwamnan Osun Na 6

LABARAI MASU NASABA

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Hausawa

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.