• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Batun Kare Martabar Kyawawan Al’adun Hausawa

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
in Rahotonni
0
Batun Kare Martabar Kyawawan Al’adun Hausawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Fili na musamman domin makaranta, wanda zai rika ba wa kowa damar tofa albarkacin bakinsa kan abin da ya dame shi cikin zuciya, na rayywar yau da kullum, ko makamancin haka.

Filin namu na yau yana tafe da bayanin Abba Abubakar Yakubu, dangane da abin da ya dame shi cikin zuciya. Inda ya fara da cewa:

  • Ra’ayoyinku A Kan Batun Hako Man Fetur A Yankin Bauchi Da Gombe
  • Yadda Za A Kula Da Tafin Kafa Lokacin Hunturu

“Al’adun da kuke kyama, yanzu sun zama abin kwalliyar ku, saura ku karbi addininmu!”. Wadannan wasu kalamai ne na izgili da wani wanda ba musulmi ba ya rubuta a kasan jikin wani hoton wasu ma’aurata sabbin aure, wato Ango da Amarya, wanda aka dauka lokacin wani shagalin bikin aure.

Yanayin hoton ya nuna Angon cikin shigar kananan kaya ya sa kwat da wando da madaurin wuya, yayin da ita kuma Amaryar ta sanya farar rigar leshi da siffar dinkin Amaren turawa, kai ka ce dai bikin na wadanda ba musulmi ba ne.

Ba su kadai ba, hatta ga sauran abokai da kawayen Amarya ma duk irin wannan shiga ta kananan kaya suka yi, wasu ma kansu babu kallabi. Sai dai mai yiwuwa ka yi mamakin jin cewa, wannan Amarya da Ango ‘Ya’yan Musulmi ne, kuma ma cikakkun Hausawa ne, Amina da Bashir.

Labarai Masu Nasaba

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

Ko da yake da gani ka san biki ne na wasu ‘ya’yan masu hannu da shuni, ‘yan siyasa ko wasu hamshakan ‘yan boko, saboda irin yadda aka kawata wajen bikin da kuma irin manyan mawakan da aka gayyata daga kudancin kasar nan.

Ba ina nufin yin irin wannan shigar ta sabawa koyarwar addini ba ne, wannan hakkin malamai ne su inganta ko su tsawatar a kai, amma ni abin da ya fi daukar hankalina shi ne; kayan da suka sa sun sabawa bikin aure na al’adar Bahaushe. Idan mun lura, saboda sabawar ce ma har wani yake ganin, saura kiris a ajiye addinin ma a gefe.

Na fara rubutu na da wannan salo ne domin nuna mana irin lalacewar da al’adun Malam Bahaushe suka samu kansu a ciki, musamman a bangaren bikin aure, kuma abin takaici masu fada a ji daga cikin al’ummar Arewa na daga wadanda ke kara angiza irin wannan lalacewar tarbiyya da al’ada.

Abin takaici ne yau ka je wajen bikin ‘ya’yan manyan kasar nan ka ga irin bidi’o’in da aka shirya da abubuwan da ake gudanarwa da sunan biki, wadanda ko kusa ba su yi kama da na Hausawa ba, kuma ma ba su dace da koyarwar addini ba.

Idan mai karatu ya lura da kalaman da na rubuta a farkon wannan sharhin na san zai yi tunanin lallai sauran abokan zaman mu su kansu suna mamakin yadda garin kwaikwayonsu da muke yi har mun kusa wuce makadi da rawa.

Kalaman da aka yi amfani da su a farkon wannan rubutu ba kirkira ba ne, tabbas! haka wani ya rubuta a shafin Instagram na wasu masu biki da suka sa hotunan auren su.

Ashe kenan idan har wadanda ba Hausawa ba za su rika mamakin yadda rayuwar mu ta canza, muka manta da namu kyawawan al’adun muka koma kwaikwayon wasu, za mu yi takaici da cizon yatsa kan wasu abubuwan da ke faruwa a rayuwar akasarin Hausawa ko ‘yan Arewa, ba kawai a sha’anin biki ba, har ma da sauran harkokin mu na rayuwa.

Matasa da iyayensu sun rungumi wasu halaye da suka saba da asalin tarbiyya, yakana, kunya da mutunta kai da aka san Hausawa da su.

Haka mutum zai yi ta ganin wasu abubuwan takaici da ke faruwa, tsakanin masu shirin aure, wanda ake kira hotunan kafin biki (Pre-Wedding Pictures), wani salon daukar hoto na ‘yan zamani.

Yadda za ka ga masoyan ko masu shirin auren na rungumar junansu, sumbatar juna da wasu sassan jikinsu, za ka rantse ma’aurata ne, sun yi aure tuni, ba wai shirin auren suke yi ba. To, in ma auren suka yi, haka addinin Musulunci da al’adar mu ta koyar a rika yi, don bayyana soyayya da burge mutane?.

Wasa a hankali muna kara yin baya baya da tarbiyyar mu ta addini da wanda iyaye da magabatan mu na kwarai suka dora mu a kai.

Muna rungumar wasu al’adu da ba su dace ba, kuma wata rana za mu ji kunyar a danganta mu da su, musamman idan yaran mu suka taso suka ga abubuwan da muka aikata a lokacin kuruciyar mu. Wanne abin koyi muke bar musu? Wacce rayuwa muke fatan su yi nan gaba, a matsayin su na manyan gobe?

Daga Abba Abubakar Yakubu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Al'adun HausawaAureBiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsokaci A Kan Mazan Da Ba Su Yi Wa Matansu Kwalliya A Gida

Next Post

An Rantsar Da Ademola Adeleke A Matsayin Gwamnan Osun Na 6

Related

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

14 hours ago
Fyade
Rahotonni

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

1 week ago
APC
Manyan Labarai

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

1 week ago
Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Sanar Da Dakatar Da Ayyukanta Saboda Alhinin Rasuwar Buhari
Labarai

Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari

2 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

2 weeks ago
2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu
Manyan Labarai

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

2 weeks ago
Next Post
An Rantsar Da Ademola Adeleke A Matsayin Gwamnan Osun Na 6

An Rantsar Da Ademola Adeleke A Matsayin Gwamnan Osun Na 6

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga ZaÉ“en Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.