ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku A Kan Batun Hako Man Fetur A Yankin Bauchi Da Gombe

by Aisha Seyoji
4 years ago
Man Fetur

Wannan makon mun kawo ra’ayoyin masu bibiyar mu a kan kaddamar da fara hakar Man Fetur a yankin jihohin Bauchi da Gombe da Shugaba Buhari ya yi. Ko wannan zai taimaka wajen tsamo al’ummar yankin daga kangin talauci?

Sani Ladan

Masha Allah, wannan babban lamari ne kullum addu’ar mu Allah ya azurta yankin nan namu na arewa da dukiyar da ake mana takama da ita, muna farin ciki kuma muna baiwa shugabanin mu na arewa su dage su sa ido, lallai kada wani abu ya kawo cikas a kan wannan muhimmin aiki, koda Buhari yana jan kafa to ya dace su fizgeshi a guje don ya kammala aikin kafin wa’adinsa na sauka. Allah ya bamu sa a ya taimake mu, mun gode.

ADVERTISEMENT

Comr Hassan S Umar

Alhamdulillahi, daga karamar Hukumar Minjibir. Wannan batu na hako man fetur a yankin Arewa. Mun dade muna dakon ranar domin idan baki, Mantaba tun kusan lokacin Gwamnatin Dr. Goodluck E Jonathan ake ikirarin gano rijiyoyin Man Fetur musammnan a Jihar Borno, a matsayinmu na yan gwagwarmaya da eman kawo cigaban al’umma, muna murna kuma tunda gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ta fara ikirarin Man Fetur din musamman jihohin Bauchi da Gombe muke cike da fatan samun haka domin rikicin da ke faruwa a kudu maso gabas din kasarnan. Babbar silarsa shi ne ‘Crude Oil Resources’.

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

Wanda batu ne me matukar fadi da ba zan iya tafashi awannan shafin ba.

Amma nasan akwai abubuwa a takaice kamar haka

-Tashe Tashen Hankula

-Samun aikin yi

-Makarkashiyar EU

Babu lokacin yin bkyani filla-filla amma abinda ba lallai kinsani ba akwai yankuna da suke da Man Fetur a kasa kamar Kano, Zamfara, Borno, Gombe da Bauchi, akwai sharshi da yawa gaskiya amma a takaice

Wannan ba karamar nasara bace, Allah ya tabbatar.

Amb Ibrahim Adam Dan-Sarauta

Idan har da gaske ne abin zai yi wu to lallai an dauko hanya ta kusa da ke shirin kawo ci gaba a Jihohin Bauchi da Gombe da ma Arewa baki daya.

Irin wannan ayyyukan na gayaran ma’adanan tattalin arizikin Arewa ba tun yanzu ya kamata a ce ana yi ba, domin su ne za su samar da habakar tattalin arzikin na Arewa da kuma magance zaman kashe wando da wasu daga cikin matasan mu suke fama da shi sannan kuma ina mai tabbatar miki da cewa za a rage harkokin ta’addanci.

Domin kashi casa’in na ‘dan ta’adda da suka addabi Arewacin kasar nan talauci ne ya ke jefa su.

Allah ya sa mu dace ya kuma ba da ikon aiwatarwa amin.

 Sulaiman Muhammad

Gaskiya na yi farin ciki sosai da jin wannan labarin domin zai haifar da cigaba sosai ta fannoni da dama

Kabo Idris Saminu

Gaskiya indan da gaske wannan aikin zai tabbata ina sa rai da cewa taulaci da ake fama dashi zai ragu matuka da gaske domin za a samu ayyukan yi, babu zaman banza ya kare.

Wannan ra’ayi nane nagode da daukar sako na. Bissalam.

Zainab Danyaya

Toh Alhamdulillah Allah ya sa ya zame mana alkhairi

Baban Khairat

Wannan labari abin farin ciki ne ga al’umma yankin Arewa, amma inda gizo ke saka shi ne a cikin watanni nawa ne aikin zai kammalu? Ki duba aikin hanyar Abuja zuwa Kano har yanzu ba a gama ba, Allah ya bada Ikon yi abinda ya dace fatanmu kenan,

Yusuf Muhammad Jalingo

Muna matukar farin ciki da wannan yunkuri na shugaban kasa shi dai ya yi nashi saura kuma sanatoci da wanda abin ya shafa su cigaba da bibiyar abubuwan kamar yadda ‘yan kudu suke yi kuma kada susa son zuciya wajen kula da kuma yin aikin. Muna fatan Allah ya sa ya amfani Arewa dama Nijeriya baki daya.

Man Fetur
Aisha Seyoji
+ postsBio
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Mata Mu Kara Hakuri A Zamantakewar Aure -Aisha Seyoji
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Ra’ayoyinku A Kan Ba Da Bashi Ga Daliban Manyan Makarantu
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Abin Haushi, Mata Sun Mayar Da Maza Tamkar Bola

MASU ALAKA

Man Fetur
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
Man Fetur
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
Ban Taba Nadamar Shiga Harkar Fim Ba -Hussain Bacci

Ban Taba Nadamar Shiga Harkar Fim Ba -Hussain Bacci

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.