ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Batun Kare Martabar Kyawawan Al’adun Hausawa

by Rabi'u Ali Indabawa
4 years ago
Hausawa

Fili na musamman domin makaranta, wanda zai rika ba wa kowa damar tofa albarkacin bakinsa kan abin da ya dame shi cikin zuciya, na rayywar yau da kullum, ko makamancin haka.

Filin namu na yau yana tafe da bayanin Abba Abubakar Yakubu, dangane da abin da ya dame shi cikin zuciya. Inda ya fara da cewa:

  • Ra’ayoyinku A Kan Batun Hako Man Fetur A Yankin Bauchi Da Gombe
  • Yadda Za A Kula Da Tafin Kafa Lokacin Hunturu

“Al’adun da kuke kyama, yanzu sun zama abin kwalliyar ku, saura ku karbi addininmu!”. Wadannan wasu kalamai ne na izgili da wani wanda ba musulmi ba ya rubuta a kasan jikin wani hoton wasu ma’aurata sabbin aure, wato Ango da Amarya, wanda aka dauka lokacin wani shagalin bikin aure.

ADVERTISEMENT

Yanayin hoton ya nuna Angon cikin shigar kananan kaya ya sa kwat da wando da madaurin wuya, yayin da ita kuma Amaryar ta sanya farar rigar leshi da siffar dinkin Amaren turawa, kai ka ce dai bikin na wadanda ba musulmi ba ne.

Ba su kadai ba, hatta ga sauran abokai da kawayen Amarya ma duk irin wannan shiga ta kananan kaya suka yi, wasu ma kansu babu kallabi. Sai dai mai yiwuwa ka yi mamakin jin cewa, wannan Amarya da Ango ‘Ya’yan Musulmi ne, kuma ma cikakkun Hausawa ne, Amina da Bashir.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

Ko da yake da gani ka san biki ne na wasu ‘ya’yan masu hannu da shuni, ‘yan siyasa ko wasu hamshakan ‘yan boko, saboda irin yadda aka kawata wajen bikin da kuma irin manyan mawakan da aka gayyata daga kudancin kasar nan.

Ba ina nufin yin irin wannan shigar ta sabawa koyarwar addini ba ne, wannan hakkin malamai ne su inganta ko su tsawatar a kai, amma ni abin da ya fi daukar hankalina shi ne; kayan da suka sa sun sabawa bikin aure na al’adar Bahaushe. Idan mun lura, saboda sabawar ce ma har wani yake ganin, saura kiris a ajiye addinin ma a gefe.

Na fara rubutu na da wannan salo ne domin nuna mana irin lalacewar da al’adun Malam Bahaushe suka samu kansu a ciki, musamman a bangaren bikin aure, kuma abin takaici masu fada a ji daga cikin al’ummar Arewa na daga wadanda ke kara angiza irin wannan lalacewar tarbiyya da al’ada.

Abin takaici ne yau ka je wajen bikin ‘ya’yan manyan kasar nan ka ga irin bidi’o’in da aka shirya da abubuwan da ake gudanarwa da sunan biki, wadanda ko kusa ba su yi kama da na Hausawa ba, kuma ma ba su dace da koyarwar addini ba.

Idan mai karatu ya lura da kalaman da na rubuta a farkon wannan sharhin na san zai yi tunanin lallai sauran abokan zaman mu su kansu suna mamakin yadda garin kwaikwayonsu da muke yi har mun kusa wuce makadi da rawa.

Kalaman da aka yi amfani da su a farkon wannan rubutu ba kirkira ba ne, tabbas! haka wani ya rubuta a shafin Instagram na wasu masu biki da suka sa hotunan auren su.

Ashe kenan idan har wadanda ba Hausawa ba za su rika mamakin yadda rayuwar mu ta canza, muka manta da namu kyawawan al’adun muka koma kwaikwayon wasu, za mu yi takaici da cizon yatsa kan wasu abubuwan da ke faruwa a rayuwar akasarin Hausawa ko ‘yan Arewa, ba kawai a sha’anin biki ba, har ma da sauran harkokin mu na rayuwa.

Matasa da iyayensu sun rungumi wasu halaye da suka saba da asalin tarbiyya, yakana, kunya da mutunta kai da aka san Hausawa da su.

Haka mutum zai yi ta ganin wasu abubuwan takaici da ke faruwa, tsakanin masu shirin aure, wanda ake kira hotunan kafin biki (Pre-Wedding Pictures), wani salon daukar hoto na ‘yan zamani.

Yadda za ka ga masoyan ko masu shirin auren na rungumar junansu, sumbatar juna da wasu sassan jikinsu, za ka rantse ma’aurata ne, sun yi aure tuni, ba wai shirin auren suke yi ba. To, in ma auren suka yi, haka addinin Musulunci da al’adar mu ta koyar a rika yi, don bayyana soyayya da burge mutane?.

Wasa a hankali muna kara yin baya baya da tarbiyyar mu ta addini da wanda iyaye da magabatan mu na kwarai suka dora mu a kai.

Muna rungumar wasu al’adu da ba su dace ba, kuma wata rana za mu ji kunyar a danganta mu da su, musamman idan yaran mu suka taso suka ga abubuwan da muka aikata a lokacin kuruciyar mu. Wanne abin koyi muke bar musu? Wacce rayuwa muke fatan su yi nan gaba, a matsayin su na manyan gobe?

Daga Abba Abubakar Yakubu.

Hausawa
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
An Rantsar Da Ademola Adeleke A Matsayin Gwamnan Osun Na 6

An Rantsar Da Ademola Adeleke A Matsayin Gwamnan Osun Na 6

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.