• Leadership Hausa
Tuesday, February 7, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Yadda Za A Kula Da Tafin Kafa Lokacin Hunturu

by Bilkisu Tijjani
2 months ago
in Labarai
0
Yadda Za A Kula Da Tafin Kafa Lokacin Hunturu

Masu karatu da ke jimirin bibiyarmu a wannan shafi mai farin jinni na Ado Da Kwalliya ina muku gaisuwa ta ban girma assalamu alaikum. Ina fata kowa yana nan cikin koshin lafiya amin.

Kamar yadda aka sani, a duk lokacin da hunturu ya shigo, ana samun tamukewar fata ta yadda wani lokaci abin kan kai da fashewa a samu faso.

  • Yadda Qatar Ta Zo Da Sabon Salo Na Ba-zata A Gasar Cin Kofin Duniya
  • Tsoma Baki Da Lalata Tsarin Samar Da Kayayyaki Da Amurka Ke Yi Bai Samu Karbuwa Ba

Saboda mihimmancin kula da tsaftar kafa a wannan lokaci ya sa muka dauko wannan batu mai muhimmanci a wannan makon.

Dole ne mu kula da tafukan kafafunmu. Mata da dama na mantawa wajen kula da kafa a duk lokacin da suke kwalliya. Lallai idan aka yi hakan kamar an yi tuya an manta da albasa ce.

Abin kunya ne a ce mace idan ta taka mutum sai ya ji kamar kaya saboda tsabagen kaushi da faso da ke tafin kafarta. Akwai hanyoyi da dama da za a bi don kula da tafukan kafarmu kamar haka:

Labarai Masu Nasaba

Yadda Aka Yi Wa ‘Yan Nijeriya 16 Kisan Gilla A Burkina Faso

Tinubu Ya Bai Wa Iyalan Wadanda ‘Yan Bindiga Suka Kashe Kyautar 100m A Katsina

Kamar yadda bayanai daga Manhajar Kwalliya Da Gyaran Jikin Mata suka nuna, abu na farko da za a yi shi ne, a samu man glycerin da gishirin Epsom (ana samunsu a manyan kantuna da ake sayar da kayan kwalliya) da man tee tree da kuma man peppermint a zuba su a ruwa sannan a jika kafafun na tsawon minti 15 zuwa 20 sannan a dauko dutsen goge kafa a diddirza, za a ga canji.

Na biyu kuma, za a iya amfani da baking soda (ana samunsa a inda ake sayar da kayan hada kek) da man tea tree da man lafinta sannan a zuba a ruwan dumi a gauraya su sai a tsoma kafa na minti 20 sannan a dirza da dutsen goge kafa. Yin hakan na rage fitowar kaushi da faso a tafin kafa.

Hanya ta uku ita ce, a samo Man lafinta da sea salt da ruwan aloe bera da man Rosemary a hada su a ruwa sannan a tsoma kafa na tsawon minti 20 sannan a dirza kafa har sai ta fita tsaf.

Bayan haka, sai a busar da kafa ko a goge da tawul. Sannan a shafa man glycerin da na lafinta a fatar kafa da tafin kafa. Sannan sai a yanka farce a gyara su.

Wadda ke fama da matsalar kaushi lallai ne ta dage wajen yin amfani da safar kafa idan da dama a shafa man basilin a tafin kafar kafin a kwanta a kullum. Sannan a sanya fatar kafar yin laushi da kuma rage shi daga tsagewa.

Dutsen goge kafa na taka rawar gani wajen tabbatar da samun tafin kafa mai sulbi da kuma cire kaushin kafa. Ya kasance kafa ta jiku kafin a yi amfani da dutsen goge kafa domin samun sakamako mai matukar amfani.

Muna fata za a kara kula sosai da tsaftar kafa domin a wannan lokaci galibin inda ya fi samun matsala ke nan a wannan lokaci na hunturu a jikin Dan’adam.

Tags: HunturuKafa
Previous Post

An Shirya Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Matasan Sin Da Afirka Karo Na Biyu Ta Kafar Bidiyo

Next Post

Sin Ta Kara Baiwa Zimbabwe Allurar Rigakafin COVID-19

Related

Yadda Aka Yi Wa ‘Yan Nijeriya 16 Kisan Gilla A Burkina Faso
Labarai

Yadda Aka Yi Wa ‘Yan Nijeriya 16 Kisan Gilla A Burkina Faso

18 mins ago
Tinubu Ya Bai Wa Iyalan Wadanda ‘Yan Bindiga Suka Kashe Kyautar 100m A Katsina
Manyan Labarai

Tinubu Ya Bai Wa Iyalan Wadanda ‘Yan Bindiga Suka Kashe Kyautar 100m A Katsina

53 mins ago
Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Shugaban EFCC A Gidan Yarin Kuje 
Manyan Labarai

Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Shugaban EFCC A Gidan Yarin Kuje 

2 hours ago
EFCC Ta Cafke Manajan Banki Kan Daukar Sabbin Kudi Da Bayar Da Su A Abuja
Labarai

EFCC Ta Cafke Manajan Banki Kan Daukar Sabbin Kudi Da Bayar Da Su A Abuja

12 hours ago
Sauya Takardun Kuɗi: Jam’iyyu Siyasa 13 A Nijeriya Sun Yi Barazanar Ƙaurace Wa Zaɓen 2023
Labarai

Sauya Takardun Kuɗi: Jam’iyyu Siyasa 13 A Nijeriya Sun Yi Barazanar Ƙaurace Wa Zaɓen 2023

16 hours ago
Rikicin ‘Yan Bindiga: Adadin Mutanen Da Aka Kashe Ya Karu Sama Da Mutum 100 A Katsina
Labarai

Rikicin ‘Yan Bindiga: Adadin Mutanen Da Aka Kashe Ya Karu Sama Da Mutum 100 A Katsina

19 hours ago
Next Post
Sin Ta Kara Baiwa Zimbabwe Allurar Rigakafin COVID-19

Sin Ta Kara Baiwa Zimbabwe Allurar Rigakafin COVID-19

LABARAI MASU NASABA

Yadda Aka Yi Wa ‘Yan Nijeriya 16 Kisan Gilla A Burkina Faso

Yadda Aka Yi Wa ‘Yan Nijeriya 16 Kisan Gilla A Burkina Faso

February 7, 2023
Tinubu Ya Bai Wa Iyalan Wadanda ‘Yan Bindiga Suka Kashe Kyautar 100m A Katsina

Tinubu Ya Bai Wa Iyalan Wadanda ‘Yan Bindiga Suka Kashe Kyautar 100m A Katsina

February 7, 2023
Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Shugaban EFCC A Gidan Yarin Kuje 

Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Shugaban EFCC A Gidan Yarin Kuje 

February 7, 2023
Hadin Gwiwar BRICS Ya Nuna Halin Ci Gaba Mai Kyau

Hadin Gwiwar BRICS Ya Nuna Halin Ci Gaba Mai Kyau

February 7, 2023
Kotu Ta Yanke Wa Wani Tsoho Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Har Abada Kan Laifin Fyade A Jigawa

Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Dakatar Da CBN Da Buhari Ƙara Wa’adin Maye Tsoffin Kuɗi

February 6, 2023
EFCC Ta Cafke Manajan Banki Kan Daukar Sabbin Kudi Da Bayar Da Su A Abuja

EFCC Ta Cafke Manajan Banki Kan Daukar Sabbin Kudi Da Bayar Da Su A Abuja

February 6, 2023
An Samar Da Damar Dawo Da Zirga-zirga A Dukkan Fannoni A Tsakanin Hong Kong Da Babban Yankin Kasar Sin

An Samar Da Damar Dawo Da Zirga-zirga A Dukkan Fannoni A Tsakanin Hong Kong Da Babban Yankin Kasar Sin

February 6, 2023
Shugaban Kasar Sin Ya Mika Sakon Jaje Ga Takwarorinsa Na Turkiyya Da Syria Bisa Ibtila’in Girgizar Kasa Da Ya Shafi Sassan Kasashen Biyu

Shugaban Kasar Sin Ya Mika Sakon Jaje Ga Takwarorinsa Na Turkiyya Da Syria Bisa Ibtila’in Girgizar Kasa Da Ya Shafi Sassan Kasashen Biyu

February 6, 2023
Tawagogin Sinawa Masu Yawon Shakatawa Sun Sake Fara Ziyara A Ketare

Tawagogin Sinawa Masu Yawon Shakatawa Sun Sake Fara Ziyara A Ketare

February 6, 2023
Ana Gaggauta Raya Manyan Ayyukan Ban Ruwa A Sassan Kasar Sin

Ana Gaggauta Raya Manyan Ayyukan Ban Ruwa A Sassan Kasar Sin

February 6, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.