ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Za A Kula Da Tafin Kafa Lokacin Hunturu

by Bilkisu Tijjani
4 years ago
Kafa

Masu karatu da ke jimirin bibiyarmu a wannan shafi mai farin jinni na Ado Da Kwalliya ina muku gaisuwa ta ban girma assalamu alaikum. Ina fata kowa yana nan cikin koshin lafiya amin.

Kamar yadda aka sani, a duk lokacin da hunturu ya shigo, ana samun tamukewar fata ta yadda wani lokaci abin kan kai da fashewa a samu faso.

  • Yadda Qatar Ta Zo Da Sabon Salo Na Ba-zata A Gasar Cin Kofin Duniya
  • Tsoma Baki Da Lalata Tsarin Samar Da Kayayyaki Da Amurka Ke Yi Bai Samu Karbuwa Ba

Saboda mihimmancin kula da tsaftar kafa a wannan lokaci ya sa muka dauko wannan batu mai muhimmanci a wannan makon.

ADVERTISEMENT

Dole ne mu kula da tafukan kafafunmu. Mata da dama na mantawa wajen kula da kafa a duk lokacin da suke kwalliya. Lallai idan aka yi hakan kamar an yi tuya an manta da albasa ce.

Abin kunya ne a ce mace idan ta taka mutum sai ya ji kamar kaya saboda tsabagen kaushi da faso da ke tafin kafarta. Akwai hanyoyi da dama da za a bi don kula da tafukan kafarmu kamar haka:

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Kamar yadda bayanai daga Manhajar Kwalliya Da Gyaran Jikin Mata suka nuna, abu na farko da za a yi shi ne, a samu man glycerin da gishirin Epsom (ana samunsu a manyan kantuna da ake sayar da kayan kwalliya) da man tee tree da kuma man peppermint a zuba su a ruwa sannan a jika kafafun na tsawon minti 15 zuwa 20 sannan a dauko dutsen goge kafa a diddirza, za a ga canji.

Na biyu kuma, za a iya amfani da baking soda (ana samunsa a inda ake sayar da kayan hada kek) da man tea tree da man lafinta sannan a zuba a ruwan dumi a gauraya su sai a tsoma kafa na minti 20 sannan a dirza da dutsen goge kafa. Yin hakan na rage fitowar kaushi da faso a tafin kafa.

Hanya ta uku ita ce, a samo Man lafinta da sea salt da ruwan aloe bera da man Rosemary a hada su a ruwa sannan a tsoma kafa na tsawon minti 20 sannan a dirza kafa har sai ta fita tsaf.

Bayan haka, sai a busar da kafa ko a goge da tawul. Sannan a shafa man glycerin da na lafinta a fatar kafa da tafin kafa. Sannan sai a yanka farce a gyara su.

Wadda ke fama da matsalar kaushi lallai ne ta dage wajen yin amfani da safar kafa idan da dama a shafa man basilin a tafin kafar kafin a kwanta a kullum. Sannan a sanya fatar kafar yin laushi da kuma rage shi daga tsagewa.

Dutsen goge kafa na taka rawar gani wajen tabbatar da samun tafin kafa mai sulbi da kuma cire kaushin kafa. Ya kasance kafa ta jiku kafin a yi amfani da dutsen goge kafa domin samun sakamako mai matukar amfani.

Muna fata za a kara kula sosai da tsaftar kafa domin a wannan lokaci galibin inda ya fi samun matsala ke nan a wannan lokaci na hunturu a jikin Dan’adam.

Kafa
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Sin Ta Kara Baiwa Zimbabwe Allurar Rigakafin COVID-19

Sin Ta Kara Baiwa Zimbabwe Allurar Rigakafin COVID-19

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.