• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Batutuwan Dake Janyo Hankalin Sin Da Afirka

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Batutuwan Dake Janyo Hankalin Sin Da Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A farkon sabuwar shekarar da muke ciki, ministan wajen kasar Sin ya sake kai ziyara nahiyar Afirka.

Jiya, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya kai ziyarar aiki a kasar Masar. Daga bisani, zai ziyarci kasashen Tunisia, da Togo, da Kodibwa. Hakan nan shekaru 34 a jere ke nan da ministan wajen kasar Sin ya fara kai ziyara nahiyar Afirka a farkon kowace shekara. Dangane da wannan batu, jaridar Al Akhbar ta kasar Masar ta rubuta wani sharhi cewa, hakan ya nuna “yadda kasar Sin take dora muhimmanci kan huldarta da kasashen Afirka, gami da kyakkyawar dangantakar dake tsakanin bangarorin 2, mai zurfi da daddaden tarihi.” Sai dai, bayan da abokan 2, wato Sin da Afirka, suka gana da juna a farkon sabuwar shekara, wadanne abubuwa za su tattauna a kai?

  • Yadda Aikin Gine-gine Na Kasar Sin Suka Taimaka Wajen Gudanar Da Gasar Cin Kofin Afirka
  • Ofishin Kula Da Harkokin Taiwan Na Majalisar Gudanarwa Da Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Sun Yi Tsokaci Kan Sakamakon Zabukan Taiwan

Da farko, za su tattauna batun zaman lafiya. A yayin da yake kasar Masar, ministan harkokin wajen kasar Sin ya gana da takwaransa na kasar Masar, da shugaban kasar, inda suka fi mai da hankali kan yanayin da ake ciki a zirin Gaza, gami da nuna buri da karfin hali, a fannin kare zaman lafiya da tabbatar da adalci. A wajen taron maneman labaru da ya gudana bayan ganawar, Wang Yi ya jaddada ra’ayin kasar Sin dangane da wannan batu, wato neman tsagaita bude wuta nan da nan, da ba da damar kai dauki ga masu bukata, da aiwatar da shirin kafa kasashe guda 2 a shiyyar don tabbatar da adalci ga Falasdinawa. Wannan ra’ayi na kasar Sin ya zama dai-dai da na kasar Masar, abin da ya sa kasashen 2 gabatar da wata hadaddiyar sanarwa a wannan karo.

Ban da haka, wani abin da ya kamata a lura da shi shi ne, a nata bangare, kasar Afirka ta Kudu ta kai kara gaban kotun kasa da kasa a kwanakin baya, inda take zargin kasar Isra’ila da aikata kisan kare dangi kan Falasdinawa a zirin Gaza, da bukatar kotun da ta umarci Isra’ila ta tsagaita bude wuta nan take. Bayan haka kuma, kasar Namibia ita ma ta nuna goyon baya kan matakin da Afirka ta Kudu ta dauka. Ta haka za mu fahimci cewa, kasashen Afirka da kasar Sin tare suke, a kokarin tabbatar da zaman lafiya da adalci a duniya.

Ban da bukatar samun zaman lafiya, an kuma mai da hankali kan maganar raya kasa da neman samun ci gaban tattalin arziki, yayin ziyarar Wang Yi a nahiyar Afirka a wannan karo. Kamar yadda jami’in ya gaya ma shugaba Abdel Fattah al Sisi na kasar Masar cewa, “Yayin da kasar Masar ke neman raya kanta, za ta iya dogaro kan daddadiyar huldar dake tsakaninta da kasar Sin.” Sai dai a hakika, Masar da sauran kasashen da Malam Wang Yi zai kai ziyara a wannan karo, tuni sun kasance abokan huldar kasar Sin, ta fuskar hadin gwiwa a fannin raya kasa. Misali, a kasar Masar, wani yankin hadin gwiwa na cinikayya, da bangarorin Sin da Masar suka kafa tare, ya riga ya janyo kamfanoni fiye da 140, wadanda suka bude rassansu a yankin, tare da samar da guraben aikin yi ga jama’ar kasar fiye da dubu 50. Kana a kasar Tunisia, kasar Sin ta ba da tallafin wani asibiti, da wani kwalejin horar da jami’an diplomasiyya, da wata cibiyar wasan motsa jiki ga kasar, kana kamfanonin kasar Sin na kokarin gina wasu manyan ayyukan more rayuwa a can, ciki har da wata babbar madatsar ruwa.

Labarai Masu Nasaba

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Sa’an nan a arewacin kasar Togo, wasu kwararru na kasar Sin masu fasahar aikin gona sun gudanar da gwaje-gwaje kan wani sabon nau’in shinkafa, wanda ya dace da yanayin lokacin rani, kuma ya samar da mafi yawan ’ya’ya fiye da nau’ika na baya. Yayin da a birnin Abidjan na kasar Kodivwa, wata sabuwar gadar da wani kamfanin Sin ya gina ta saukaka matsalar cunkuson ababen hawa. Bisa tushen wadannan abubuwan da suka shaida nagartacciyar huldar hadin kai tsakanin Sin da Afirka, ziyarar da Wang Yi ya kai nahiyar Afirka a wannan karo, za ta iya samar da karin nasarori.

Dalilin da ya sa ake samun kaunar juna tsakanin abokai, shi ne domin suna da tunani iri daya. Kana tunani na bai daya da kasar Sin da kasashen Afirka suke da shi, shi ne, yunkurin tabbatar da zaman lafiya da neman ci gaba. Yayin da ake ci gaba da fama da ra’ayi na babakere da nuna fin karfi, da yin mummunar takara ba tare da sanin ya kamata ba, gami da yin fito na fito, a sauran wurare daban daban na duniyarmu, kasar Sin da kasashen Afirka suna kokarin hadin gwiwa da juna, bisa burinsu da tunaninsu na bai daya, inda suke samar da gudunmow a kai a kai, don tabbatar da kyakkyawar makoma ga daukacin dan Adam. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alakar sinbda AfirkaAmurkaRasha
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ranar Tunawa Da Jarumai: Gwamnatin Kano Za Ta Kafa Gidauniyar Tallafawa Iyalan Sojojin Da suka Rasu

Next Post

Kasar Nauru Na Son Maido Da Huldar Diplomasiyya Da Sin

Related

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?
Daga Birnin Sin

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

17 hours ago
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

18 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

20 hours ago
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

20 hours ago
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya
Daga Birnin Sin

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

22 hours ago
Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC
Daga Birnin Sin

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

23 hours ago
Next Post
Kasar Nauru Na Son Maido Da Huldar Diplomasiyya Da Sin

Kasar Nauru Na Son Maido Da Huldar Diplomasiyya Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

August 27, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.