• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Batutuwan Dake Janyo Hankalin Sin Da Afirka

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Batutuwan Dake Janyo Hankalin Sin Da Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A farkon sabuwar shekarar da muke ciki, ministan wajen kasar Sin ya sake kai ziyara nahiyar Afirka.

Jiya, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya kai ziyarar aiki a kasar Masar. Daga bisani, zai ziyarci kasashen Tunisia, da Togo, da Kodibwa. Hakan nan shekaru 34 a jere ke nan da ministan wajen kasar Sin ya fara kai ziyara nahiyar Afirka a farkon kowace shekara. Dangane da wannan batu, jaridar Al Akhbar ta kasar Masar ta rubuta wani sharhi cewa, hakan ya nuna “yadda kasar Sin take dora muhimmanci kan huldarta da kasashen Afirka, gami da kyakkyawar dangantakar dake tsakanin bangarorin 2, mai zurfi da daddaden tarihi.” Sai dai, bayan da abokan 2, wato Sin da Afirka, suka gana da juna a farkon sabuwar shekara, wadanne abubuwa za su tattauna a kai?

  • Yadda Aikin Gine-gine Na Kasar Sin Suka Taimaka Wajen Gudanar Da Gasar Cin Kofin Afirka
  • Ofishin Kula Da Harkokin Taiwan Na Majalisar Gudanarwa Da Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Sun Yi Tsokaci Kan Sakamakon Zabukan Taiwan

Da farko, za su tattauna batun zaman lafiya. A yayin da yake kasar Masar, ministan harkokin wajen kasar Sin ya gana da takwaransa na kasar Masar, da shugaban kasar, inda suka fi mai da hankali kan yanayin da ake ciki a zirin Gaza, gami da nuna buri da karfin hali, a fannin kare zaman lafiya da tabbatar da adalci. A wajen taron maneman labaru da ya gudana bayan ganawar, Wang Yi ya jaddada ra’ayin kasar Sin dangane da wannan batu, wato neman tsagaita bude wuta nan da nan, da ba da damar kai dauki ga masu bukata, da aiwatar da shirin kafa kasashe guda 2 a shiyyar don tabbatar da adalci ga Falasdinawa. Wannan ra’ayi na kasar Sin ya zama dai-dai da na kasar Masar, abin da ya sa kasashen 2 gabatar da wata hadaddiyar sanarwa a wannan karo.

Ban da haka, wani abin da ya kamata a lura da shi shi ne, a nata bangare, kasar Afirka ta Kudu ta kai kara gaban kotun kasa da kasa a kwanakin baya, inda take zargin kasar Isra’ila da aikata kisan kare dangi kan Falasdinawa a zirin Gaza, da bukatar kotun da ta umarci Isra’ila ta tsagaita bude wuta nan take. Bayan haka kuma, kasar Namibia ita ma ta nuna goyon baya kan matakin da Afirka ta Kudu ta dauka. Ta haka za mu fahimci cewa, kasashen Afirka da kasar Sin tare suke, a kokarin tabbatar da zaman lafiya da adalci a duniya.

Ban da bukatar samun zaman lafiya, an kuma mai da hankali kan maganar raya kasa da neman samun ci gaban tattalin arziki, yayin ziyarar Wang Yi a nahiyar Afirka a wannan karo. Kamar yadda jami’in ya gaya ma shugaba Abdel Fattah al Sisi na kasar Masar cewa, “Yayin da kasar Masar ke neman raya kanta, za ta iya dogaro kan daddadiyar huldar dake tsakaninta da kasar Sin.” Sai dai a hakika, Masar da sauran kasashen da Malam Wang Yi zai kai ziyara a wannan karo, tuni sun kasance abokan huldar kasar Sin, ta fuskar hadin gwiwa a fannin raya kasa. Misali, a kasar Masar, wani yankin hadin gwiwa na cinikayya, da bangarorin Sin da Masar suka kafa tare, ya riga ya janyo kamfanoni fiye da 140, wadanda suka bude rassansu a yankin, tare da samar da guraben aikin yi ga jama’ar kasar fiye da dubu 50. Kana a kasar Tunisia, kasar Sin ta ba da tallafin wani asibiti, da wani kwalejin horar da jami’an diplomasiyya, da wata cibiyar wasan motsa jiki ga kasar, kana kamfanonin kasar Sin na kokarin gina wasu manyan ayyukan more rayuwa a can, ciki har da wata babbar madatsar ruwa.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Sa’an nan a arewacin kasar Togo, wasu kwararru na kasar Sin masu fasahar aikin gona sun gudanar da gwaje-gwaje kan wani sabon nau’in shinkafa, wanda ya dace da yanayin lokacin rani, kuma ya samar da mafi yawan ’ya’ya fiye da nau’ika na baya. Yayin da a birnin Abidjan na kasar Kodivwa, wata sabuwar gadar da wani kamfanin Sin ya gina ta saukaka matsalar cunkuson ababen hawa. Bisa tushen wadannan abubuwan da suka shaida nagartacciyar huldar hadin kai tsakanin Sin da Afirka, ziyarar da Wang Yi ya kai nahiyar Afirka a wannan karo, za ta iya samar da karin nasarori.

Dalilin da ya sa ake samun kaunar juna tsakanin abokai, shi ne domin suna da tunani iri daya. Kana tunani na bai daya da kasar Sin da kasashen Afirka suke da shi, shi ne, yunkurin tabbatar da zaman lafiya da neman ci gaba. Yayin da ake ci gaba da fama da ra’ayi na babakere da nuna fin karfi, da yin mummunar takara ba tare da sanin ya kamata ba, gami da yin fito na fito, a sauran wurare daban daban na duniyarmu, kasar Sin da kasashen Afirka suna kokarin hadin gwiwa da juna, bisa burinsu da tunaninsu na bai daya, inda suke samar da gudunmow a kai a kai, don tabbatar da kyakkyawar makoma ga daukacin dan Adam. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alakar sinbda AfirkaAmurkaRasha
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ranar Tunawa Da Jarumai: Gwamnatin Kano Za Ta Kafa Gidauniyar Tallafawa Iyalan Sojojin Da suka Rasu

Next Post

Kasar Nauru Na Son Maido Da Huldar Diplomasiyya Da Sin

Related

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

17 hours ago
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu
Daga Birnin Sin

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

18 hours ago
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

19 hours ago
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere
Daga Birnin Sin

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

20 hours ago
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

21 hours ago
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa
Daga Birnin Sin

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

22 hours ago
Next Post
Kasar Nauru Na Son Maido Da Huldar Diplomasiyya Da Sin

Kasar Nauru Na Son Maido Da Huldar Diplomasiyya Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

July 1, 2025
Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

July 1, 2025
Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

July 1, 2025
Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

July 1, 2025
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

July 1, 2025
Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.