ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Batutuwan Dake Janyo Hankalin Sin Da Afirka

by CGTN Hausa
3 years ago
Sin

A farkon sabuwar shekarar da muke ciki, ministan wajen kasar Sin ya sake kai ziyara nahiyar Afirka.

Jiya, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya kai ziyarar aiki a kasar Masar. Daga bisani, zai ziyarci kasashen Tunisia, da Togo, da Kodibwa. Hakan nan shekaru 34 a jere ke nan da ministan wajen kasar Sin ya fara kai ziyara nahiyar Afirka a farkon kowace shekara. Dangane da wannan batu, jaridar Al Akhbar ta kasar Masar ta rubuta wani sharhi cewa, hakan ya nuna “yadda kasar Sin take dora muhimmanci kan huldarta da kasashen Afirka, gami da kyakkyawar dangantakar dake tsakanin bangarorin 2, mai zurfi da daddaden tarihi.” Sai dai, bayan da abokan 2, wato Sin da Afirka, suka gana da juna a farkon sabuwar shekara, wadanne abubuwa za su tattauna a kai?

  • Yadda Aikin Gine-gine Na Kasar Sin Suka Taimaka Wajen Gudanar Da Gasar Cin Kofin Afirka
  • Ofishin Kula Da Harkokin Taiwan Na Majalisar Gudanarwa Da Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Sun Yi Tsokaci Kan Sakamakon Zabukan Taiwan

Da farko, za su tattauna batun zaman lafiya. A yayin da yake kasar Masar, ministan harkokin wajen kasar Sin ya gana da takwaransa na kasar Masar, da shugaban kasar, inda suka fi mai da hankali kan yanayin da ake ciki a zirin Gaza, gami da nuna buri da karfin hali, a fannin kare zaman lafiya da tabbatar da adalci. A wajen taron maneman labaru da ya gudana bayan ganawar, Wang Yi ya jaddada ra’ayin kasar Sin dangane da wannan batu, wato neman tsagaita bude wuta nan da nan, da ba da damar kai dauki ga masu bukata, da aiwatar da shirin kafa kasashe guda 2 a shiyyar don tabbatar da adalci ga Falasdinawa. Wannan ra’ayi na kasar Sin ya zama dai-dai da na kasar Masar, abin da ya sa kasashen 2 gabatar da wata hadaddiyar sanarwa a wannan karo.

ADVERTISEMENT

Ban da haka, wani abin da ya kamata a lura da shi shi ne, a nata bangare, kasar Afirka ta Kudu ta kai kara gaban kotun kasa da kasa a kwanakin baya, inda take zargin kasar Isra’ila da aikata kisan kare dangi kan Falasdinawa a zirin Gaza, da bukatar kotun da ta umarci Isra’ila ta tsagaita bude wuta nan take. Bayan haka kuma, kasar Namibia ita ma ta nuna goyon baya kan matakin da Afirka ta Kudu ta dauka. Ta haka za mu fahimci cewa, kasashen Afirka da kasar Sin tare suke, a kokarin tabbatar da zaman lafiya da adalci a duniya.

Ban da bukatar samun zaman lafiya, an kuma mai da hankali kan maganar raya kasa da neman samun ci gaban tattalin arziki, yayin ziyarar Wang Yi a nahiyar Afirka a wannan karo. Kamar yadda jami’in ya gaya ma shugaba Abdel Fattah al Sisi na kasar Masar cewa, “Yayin da kasar Masar ke neman raya kanta, za ta iya dogaro kan daddadiyar huldar dake tsakaninta da kasar Sin.” Sai dai a hakika, Masar da sauran kasashen da Malam Wang Yi zai kai ziyara a wannan karo, tuni sun kasance abokan huldar kasar Sin, ta fuskar hadin gwiwa a fannin raya kasa. Misali, a kasar Masar, wani yankin hadin gwiwa na cinikayya, da bangarorin Sin da Masar suka kafa tare, ya riga ya janyo kamfanoni fiye da 140, wadanda suka bude rassansu a yankin, tare da samar da guraben aikin yi ga jama’ar kasar fiye da dubu 50. Kana a kasar Tunisia, kasar Sin ta ba da tallafin wani asibiti, da wani kwalejin horar da jami’an diplomasiyya, da wata cibiyar wasan motsa jiki ga kasar, kana kamfanonin kasar Sin na kokarin gina wasu manyan ayyukan more rayuwa a can, ciki har da wata babbar madatsar ruwa.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Sa’an nan a arewacin kasar Togo, wasu kwararru na kasar Sin masu fasahar aikin gona sun gudanar da gwaje-gwaje kan wani sabon nau’in shinkafa, wanda ya dace da yanayin lokacin rani, kuma ya samar da mafi yawan ’ya’ya fiye da nau’ika na baya. Yayin da a birnin Abidjan na kasar Kodivwa, wata sabuwar gadar da wani kamfanin Sin ya gina ta saukaka matsalar cunkuson ababen hawa. Bisa tushen wadannan abubuwan da suka shaida nagartacciyar huldar hadin kai tsakanin Sin da Afirka, ziyarar da Wang Yi ya kai nahiyar Afirka a wannan karo, za ta iya samar da karin nasarori.

Dalilin da ya sa ake samun kaunar juna tsakanin abokai, shi ne domin suna da tunani iri daya. Kana tunani na bai daya da kasar Sin da kasashen Afirka suke da shi, shi ne, yunkurin tabbatar da zaman lafiya da neman ci gaba. Yayin da ake ci gaba da fama da ra’ayi na babakere da nuna fin karfi, da yin mummunar takara ba tare da sanin ya kamata ba, gami da yin fito na fito, a sauran wurare daban daban na duniyarmu, kasar Sin da kasashen Afirka suna kokarin hadin gwiwa da juna, bisa burinsu da tunaninsu na bai daya, inda suke samar da gudunmow a kai a kai, don tabbatar da kyakkyawar makoma ga daukacin dan Adam. (Bello Wang)

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Kasar Nauru Na Son Maido Da Huldar Diplomasiyya Da Sin

Kasar Nauru Na Son Maido Da Huldar Diplomasiyya Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.