Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya biya dukkannin basussukan kudaden da ba a biya Hukumomin Jarabawa biyu wadanda ake bin gwamnatocin da suka yi mulki, wannan ma yasa aka kai ga sakin sakamakon Jarabawar daliban da suka rubuta rubutar jarabawar kammala makaranta ta SSCE na shekaru biyar.
Gwamnatocin da suka gabata a Jihar sun kasa biyan kudaden jarabawa na NECO tun daga shekarar 2014 zuwa 2018 sai kuma na(WAEC) daga shekarar 2018 zuwa 2022.
- Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu
- Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar
Sulaiman Bala Idris jami’in hulda da jama’a na gwamna Dauda Lawal shi ne ya bayyana hakan ranar Lahadi ta makon daya gabata, cewar an biya Hukumomin jarabawar biyu kudaden da suke,shi ma yasa suka saki sakamakon jarabawar da suka rike tun daga shekarar 2018 zuwa 2022.
Bayanin ya kara da cewar rwamnatin da take kan mulki yanzu kokarinta shi ne ta biya duk wadansu basussukan da aka bi,a matsayin wani tsari ne na wanda ya yi kama da irin hobbasan da yake yi domin aiwatar da dokar ta baci a bangaren ilimi.
Bugu da kari kuma kamar yadda yayi karin bayani, “Rashin biyan kudaden jarabawa na WAEC da NECO ba karamin koma – baya ya samar bag a makarantun gwamnati gaba dayan Jihar Zamfara, wanda hakan ya ci gaba ta maida ta baya idan ana maganar ilimi a fadi Nijeriya.
“Gane amfanin lamarin da ya shafi ilimi shi yasa, Gwamna Lawal ya kaddamar da dokar ta baci a bangaren ilimi a watan Nuwamba 2023,matakin da aka dauka an yi sa’a ya haifar da da mai ido a bangaren ilimi a Jihar Zamfara.
“Fiye da makarantu 500 aka y masu kwaskwarima da samar masu abubuwan da suka kamata tun lokacin da aka kaddamar da dokar ta bacin.An horar da Malaman makarantun gwamnati,ana kuma ci gaba dayin hakan.
“Saurin biyan kudaden bashi da Hukumomin WAEC da NECO ya kawo kwanciyar hankali ga daliban da suka kammala makaranta da rubiuta jarabawa, sai dai basu samu ci gaba da karatu ba saboda Hukumomin jarabawar sun rike masu sakamakon jarabawar da suka yi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp