ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Binciken Ra’ayoyi Na CGTN: Matasan Sin Da Amurka Sun Ba Da Amsa Kan Alakar Kasashen Biyu

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
CGTN

“A matsayinsu na manyan kasashe, Sin a bangaren masu tasowa da Amurka a bangaren masu ci gaba a duniya a yau, dukkan kasashen biyu za su dade a wannan duniyar, don haka dole ne su zauna tare cikin lumana.” Irin haka ne mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, kuma ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya bayyana ma’anar dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka, yayin wani taron manema labarai a game da taken diflomasiyya na manyan tarukan kasar Sin guda biyu. 

To, shin yaya dangantakar Sin da Amurka? Batun mutunta juna da cin gajiyar juna dai su ne galibi ra’ayoyin masu ba da amsa suka zo daya a kai, kamar yadda wani bincike da kafar yada labarai ta CGTN mallakin hukumar rukunin gidajen rediyo da talabijin ta kasar Sin ta gudanar a tsakanin matasa 4,003 masu shekaru 18 zuwa 45 a kasashen Sin da Amurka.

  • Kotu A Kano Ta Yanke Wa Wata Mata Hukunci Kan Safarar Maƙudan Kuɗaɗe
  • Karin Kudin Lantarki Da Na Kira: Kungiyar Kwadago Ta Yi Barazanar Shirya Zanga-zanga A Fadin Nijeriya

A wurin taron manema labarun, yayin da ake kimanta takaddamar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka, Wang Yi ya tambayi Amurka cewa, “Mece ce ribar da za ta samu daga yakin haraji da kuma yakin cinikayya? Shin gibin ciniki yana karuwa ne ko raguwa? Shin masana’antu sun matsa kaimin yin gasa ko kuma gwiwarsu ta yi sanyi? A cikin binciken ra’ayoyin, matasan da suka amsa tambayoyi daga kasashen biyu sun yi imanin cewa, cin gajiyar juna, shi ne tushen warware batutuwan da suka shafi tattalin arziki da cinikayya, kuma kashi 87.3 cikin dari na Sinawa da kashi 78.5 na matasan Amurkawa sun amince da wannan ra’ayi.

ADVERTISEMENT

A yayin da ake kimanta dangantakar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka, kashi 66.4 cikin dari na matasan kasar Sin da suka bayyana ra’ayoyi sun zabi “hadin kai da gasa”, kuma kashi 17.7 cikin dari daga cikinsu suna tunanin “gasa ce” ta fi. Sai kuma kashi 43.1 cikin dari na matasan Amurka da suka amsa cewa sun zabi “dorewar hadin gwiwa da gasa”, kuma kashi 22.7 daga cikinsu suka zabi “alaka ta yin gasa.” Masu bayyana ra’ayoyin sun yi kira ga kasashen biyu da su natsu su kalli tsarin matsalolin da ake fuskanta a dangantakar tattalin arziki da cinikayya, kana su tsayu a kan tattaunawa tare da warware su yadda ya kamata.

CGTN da jami’ar Renmin ta kasar Sin ne suka gudanar da wannan bincike na ra’ayoyi ta hannun Cibiyar Nazarin Sadarwa ta Duniya A Sabon Zamani, da niyyar gudanar da binciken a tsakanin matasa masu shekaru 18 zuwa 45 daga Sin da Amurka. Samfurin tambayoyi da aka yi ya dace da shekaru da jinsi na yawan matasan da aka tambaya masu shekaru 18 zuwa 45 a kasashen biyu. Binciken ya karade dukkan jihohi 50 na Amurka da birnin Washington D.C., kuma a kasar Sin, ya karade manyan birane 16 na yankuna bakwai, da suka hada da Beijing, da Shanghai, da Guangzhou, da Chengdu, da Xi’an. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 
Daga Birnin Sin

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia
Daga Birnin Sin

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana
Daga Birnin Sin

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Next Post
‘Yan Majalisun Nijeriya: An Bar Jaki Ana Bugun Taiki!

‘Yan Majalisun Nijeriya: An Bar Jaki Ana Bugun Taiki!

LABARAI MASU NASABA

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma: Martani

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma: Martani

November 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

November 14, 2025
Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

November 14, 2025
Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

November 14, 2025
Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

November 14, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

November 14, 2025
Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

November 14, 2025
Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

November 14, 2025
Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025
Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.