• English
  • Business News
Saturday, May 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Binciken Ra’ayoyi Na CGTN: Matasan Sin Da Amurka Sun Ba Da Amsa Kan Alakar Kasashen Biyu

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Binciken Ra’ayoyi Na CGTN: Matasan Sin Da Amurka Sun Ba Da Amsa Kan Alakar Kasashen Biyu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“A matsayinsu na manyan kasashe, Sin a bangaren masu tasowa da Amurka a bangaren masu ci gaba a duniya a yau, dukkan kasashen biyu za su dade a wannan duniyar, don haka dole ne su zauna tare cikin lumana.” Irin haka ne mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, kuma ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya bayyana ma’anar dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka, yayin wani taron manema labarai a game da taken diflomasiyya na manyan tarukan kasar Sin guda biyu. 

To, shin yaya dangantakar Sin da Amurka? Batun mutunta juna da cin gajiyar juna dai su ne galibi ra’ayoyin masu ba da amsa suka zo daya a kai, kamar yadda wani bincike da kafar yada labarai ta CGTN mallakin hukumar rukunin gidajen rediyo da talabijin ta kasar Sin ta gudanar a tsakanin matasa 4,003 masu shekaru 18 zuwa 45 a kasashen Sin da Amurka.

  • Kotu A Kano Ta Yanke Wa Wata Mata Hukunci Kan Safarar Maƙudan Kuɗaɗe
  • Karin Kudin Lantarki Da Na Kira: Kungiyar Kwadago Ta Yi Barazanar Shirya Zanga-zanga A Fadin Nijeriya

A wurin taron manema labarun, yayin da ake kimanta takaddamar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka, Wang Yi ya tambayi Amurka cewa, “Mece ce ribar da za ta samu daga yakin haraji da kuma yakin cinikayya? Shin gibin ciniki yana karuwa ne ko raguwa? Shin masana’antu sun matsa kaimin yin gasa ko kuma gwiwarsu ta yi sanyi? A cikin binciken ra’ayoyin, matasan da suka amsa tambayoyi daga kasashen biyu sun yi imanin cewa, cin gajiyar juna, shi ne tushen warware batutuwan da suka shafi tattalin arziki da cinikayya, kuma kashi 87.3 cikin dari na Sinawa da kashi 78.5 na matasan Amurkawa sun amince da wannan ra’ayi.

A yayin da ake kimanta dangantakar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka, kashi 66.4 cikin dari na matasan kasar Sin da suka bayyana ra’ayoyi sun zabi “hadin kai da gasa”, kuma kashi 17.7 cikin dari daga cikinsu suna tunanin “gasa ce” ta fi. Sai kuma kashi 43.1 cikin dari na matasan Amurka da suka amsa cewa sun zabi “dorewar hadin gwiwa da gasa”, kuma kashi 22.7 daga cikinsu suka zabi “alaka ta yin gasa.” Masu bayyana ra’ayoyin sun yi kira ga kasashen biyu da su natsu su kalli tsarin matsalolin da ake fuskanta a dangantakar tattalin arziki da cinikayya, kana su tsayu a kan tattaunawa tare da warware su yadda ya kamata.

CGTN da jami’ar Renmin ta kasar Sin ne suka gudanar da wannan bincike na ra’ayoyi ta hannun Cibiyar Nazarin Sadarwa ta Duniya A Sabon Zamani, da niyyar gudanar da binciken a tsakanin matasa masu shekaru 18 zuwa 45 daga Sin da Amurka. Samfurin tambayoyi da aka yi ya dace da shekaru da jinsi na yawan matasan da aka tambaya masu shekaru 18 zuwa 45 a kasashen biyu. Binciken ya karade dukkan jihohi 50 na Amurka da birnin Washington D.C., kuma a kasar Sin, ya karade manyan birane 16 na yankuna bakwai, da suka hada da Beijing, da Shanghai, da Guangzhou, da Chengdu, da Xi’an. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Labarai Masu Nasaba

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu A Kano Ta Yanke Wa Wata Mata Hukunci Kan Safarar Maƙudan Kuɗaɗe

Next Post

‘Yan Majalisun Nijeriya: An Bar Jaki Ana Bugun Taiki!

Related

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu
Daga Birnin Sin

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

30 minutes ago
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali
Daga Birnin Sin

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

3 hours ago
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

3 hours ago
Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo
Daga Birnin Sin

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

21 hours ago
Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi
Daga Birnin Sin

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

22 hours ago
Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani
Daga Birnin Sin

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

23 hours ago
Next Post
‘Yan Majalisun Nijeriya: An Bar Jaki Ana Bugun Taiki!

‘Yan Majalisun Nijeriya: An Bar Jaki Ana Bugun Taiki!

LABARAI MASU NASABA

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

May 10, 2025

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

May 10, 2025
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

May 10, 2025
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

May 10, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

May 10, 2025
Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

May 10, 2025
Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

May 10, 2025
Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

May 10, 2025
Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci

May 10, 2025
Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2

Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.