• English
  • Business News
Friday, September 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Binciken Ra’ayoyi Na CGTN: Matasan Sin Da Amurka Sun Ba Da Amsa Kan Alakar Kasashen Biyu

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Binciken Ra’ayoyi Na CGTN: Matasan Sin Da Amurka Sun Ba Da Amsa Kan Alakar Kasashen Biyu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“A matsayinsu na manyan kasashe, Sin a bangaren masu tasowa da Amurka a bangaren masu ci gaba a duniya a yau, dukkan kasashen biyu za su dade a wannan duniyar, don haka dole ne su zauna tare cikin lumana.” Irin haka ne mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, kuma ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya bayyana ma’anar dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka, yayin wani taron manema labarai a game da taken diflomasiyya na manyan tarukan kasar Sin guda biyu. 

To, shin yaya dangantakar Sin da Amurka? Batun mutunta juna da cin gajiyar juna dai su ne galibi ra’ayoyin masu ba da amsa suka zo daya a kai, kamar yadda wani bincike da kafar yada labarai ta CGTN mallakin hukumar rukunin gidajen rediyo da talabijin ta kasar Sin ta gudanar a tsakanin matasa 4,003 masu shekaru 18 zuwa 45 a kasashen Sin da Amurka.

  • Kotu A Kano Ta Yanke Wa Wata Mata Hukunci Kan Safarar Maƙudan Kuɗaɗe
  • Karin Kudin Lantarki Da Na Kira: Kungiyar Kwadago Ta Yi Barazanar Shirya Zanga-zanga A Fadin Nijeriya

A wurin taron manema labarun, yayin da ake kimanta takaddamar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka, Wang Yi ya tambayi Amurka cewa, “Mece ce ribar da za ta samu daga yakin haraji da kuma yakin cinikayya? Shin gibin ciniki yana karuwa ne ko raguwa? Shin masana’antu sun matsa kaimin yin gasa ko kuma gwiwarsu ta yi sanyi? A cikin binciken ra’ayoyin, matasan da suka amsa tambayoyi daga kasashen biyu sun yi imanin cewa, cin gajiyar juna, shi ne tushen warware batutuwan da suka shafi tattalin arziki da cinikayya, kuma kashi 87.3 cikin dari na Sinawa da kashi 78.5 na matasan Amurkawa sun amince da wannan ra’ayi.

A yayin da ake kimanta dangantakar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka, kashi 66.4 cikin dari na matasan kasar Sin da suka bayyana ra’ayoyi sun zabi “hadin kai da gasa”, kuma kashi 17.7 cikin dari daga cikinsu suna tunanin “gasa ce” ta fi. Sai kuma kashi 43.1 cikin dari na matasan Amurka da suka amsa cewa sun zabi “dorewar hadin gwiwa da gasa”, kuma kashi 22.7 daga cikinsu suka zabi “alaka ta yin gasa.” Masu bayyana ra’ayoyin sun yi kira ga kasashen biyu da su natsu su kalli tsarin matsalolin da ake fuskanta a dangantakar tattalin arziki da cinikayya, kana su tsayu a kan tattaunawa tare da warware su yadda ya kamata.

CGTN da jami’ar Renmin ta kasar Sin ne suka gudanar da wannan bincike na ra’ayoyi ta hannun Cibiyar Nazarin Sadarwa ta Duniya A Sabon Zamani, da niyyar gudanar da binciken a tsakanin matasa masu shekaru 18 zuwa 45 daga Sin da Amurka. Samfurin tambayoyi da aka yi ya dace da shekaru da jinsi na yawan matasan da aka tambaya masu shekaru 18 zuwa 45 a kasashen biyu. Binciken ya karade dukkan jihohi 50 na Amurka da birnin Washington D.C., kuma a kasar Sin, ya karade manyan birane 16 na yankuna bakwai, da suka hada da Beijing, da Shanghai, da Guangzhou, da Chengdu, da Xi’an. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu A Kano Ta Yanke Wa Wata Mata Hukunci Kan Safarar Maƙudan Kuɗaɗe

Next Post

‘Yan Majalisun Nijeriya: An Bar Jaki Ana Bugun Taiki!

Related

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

10 hours ago
An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

11 hours ago
Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara
Daga Birnin Sin

Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

12 hours ago
Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin
Daga Birnin Sin

Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

13 hours ago
Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo

14 hours ago
Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un

15 hours ago
Next Post
‘Yan Majalisun Nijeriya: An Bar Jaki Ana Bugun Taiki!

‘Yan Majalisun Nijeriya: An Bar Jaki Ana Bugun Taiki!

LABARAI MASU NASABA

Manzon Allah

Muna Murna Da Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (1)

September 5, 2025
Bukatar Dakatar Da Karuwar Hare-hare A Kan Likitoci – Ra’ayinmu

Barazanar Yajin Aiki: Likitoci Sun Bai Wa Gwamnati Wa’adin Kwana 10

September 5, 2025
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Ministan Tsaro

Dawowar Matsalar Tsaro: Ta Haifar Da Cece-kuce Kan Daukar Matakin Kare Kai

September 5, 2025
Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

September 4, 2025
An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

September 4, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

September 4, 2025
Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

September 4, 2025
Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

September 4, 2025
Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

September 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.