ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Majalisun Nijeriya: An Bar Jaki Ana Bugun Taiki!

by Muktar Anwar
1 year ago
Majalisun

Babu shakka, da yawan jama’ar kasa, ba su da masaniyar sashen gwamnati da ya kere kowane sashi karfin-iko karkashin wannan tsari na Dimukradiyya.

A matakin jiha ne, ko a matakin kasa!. Da jama’ar kasa sun fahimci wannan tare da rike-wuta, watakil, da yanzu lamura sun sassautu, wajen samun sa’ida a rayuwa.

  • Sojoji Sun Kashe Ƙwararren Mai Haɗa Wa Boko Haram Bam A Borno
  • Shugaban NAN:Muna Iya Ganin Basirar Sin Ta Manyan Taruka Biyu Da Take Gudanarwa Yanzu

Mutum, ko shi ne Plato (428-348 BCE), ko Aristotle (384-322 BCE) koko shi ne Confucius (551-479 BCE), ba zai fadi wani bangare na gwamnati, karkashin tsarin mulki irin na dimukradiyya, wanda za a bugi-kirji ace ya fi bangaren “yan majalisu karfin-iko (na jiha ne su, koko na kasa). Tasa wannan bangare gaba, tare da urusta masa wajen samun sawaba cikin wannan rayuwa, shi ne zai gaggauta samun nasarar kaiwa gaci, sama da bugewa maganar gwamna ko shugaban kasa.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, wadannan “yan majalisu, na jiha da na kasa, sune kusa da mu a ko da yaushe, ba su da wuyar gani, da za a kwatanta ganinsu, da ganin gwamna ko ganin shugaban kasa. Duk wata rawa mai kyau, ko mara kyawo da za a ga gwamna na takawa a matakin jiha, sai da sahalewar akasarin wadannan “yan majalisun da kuke haduwa da su ne a cikin makabartu, da wuraren daurin aure da sauransu. Shi ma shugaban kasa, duk taurin-kansa, dole ne ya yi rawa da bazar zauren majalisar dattijai da ta wakilai ta kasa.

An bar mutane ne cikin kangin fatara da duhun jahilci da gangan, sai hakan ya ja su zuwa ga barcin kaza bisa dami. Ga inda za su buga a ji kukan gwazarma, amma inda suke naushi daban. Shugaban kasa da ke yawo cikin jiniya da mugun ayarin jamian tsaro, koko wani gwamna, ba a nan ne gizo ke sakar ba, gizo na yin sakarsa ne tattare da “yan majalisun jiha da na taraiya, ko mun sani, ko ba mu sani ba. Duk irin rashin sani da mai karatu ke da shi game da yanayin tsarin Dimukradiyya a wannan kasa, ya kwana da sanin cewa, “yan majalisun jiha, na da wata dama ta cire gwamnan jiha, bisa wata dama da kundin tsarin mulkin kasa ya ba su. Haka ma yake da masaniyar irin wancan iko da “yan majalisun taraiya ke da shi, na tsige tare da yin fatali da kujerar shugaban kasa. Ko da kuwa a teburin maishayi ne, ina ka ta6a ji ance gwamna ko shugaban kasa, na da ikon tsige wani dan majalisa?.

LABARAI MASU NASABA

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

Su Wa Ke Fatattakar Obi Da Kwankwaso?

Ya zama wajibi a tarihance cewa, a duk sa’adda aka tasamma furta asalin samuwar kunshin “yan majalisun taraiya a wannan kasa, a faro daga Jihar Legas, wadda ake yi wa take da “cunkus dakin tsumma, makarinki sai an dawo”. Kasantuwar, daga can ne suka samo asali.

Mai karatu ya fahimta cewa, wannan rubutu da alama zai ja zarensa ne har zuwa wani lokaci, cikin gabatar da mabanbantan bayanai game da “yan majalisunmu na Kasa, hada da na jihohi. Fede irin karfin iko da tsarin mulkin Kasa ya ba su, tare da yin jinjina ga wasu cikin cokali daga cikinsu, sai kuma fyadar “ya”yan kadanya ga asarinsu, duba da irin burus da suka yi da kwamacalar shugabanni (shugaban kasa da gwamnoni) a kasa, duk da irin mummunan yanayi na tabarbarewar daukacin lamuran rayuwa da aka samu, musamman ga asarin jama’ar kasa da suke talakawa raunana!!!.

Cikin wannan rubutu, akwai yunkurin fakakar da al’umar kasa muhimmancin titse “yan majalisun, tare da neman suma, su titse gwamna da shugaban kasa, don rayuwar jama’ar mazabunsu su kyautata. Sabanin haka kuwa, zaben da suka yi musu, kwata-kwata bai yi wata rana ba. A rubutun, ana iya gabatar da wasu daga zakwakuran “yan majalisun (sai dai tsirari ne ainun), wadanda a aikace da baki, sun damu da ci gaban mutanensu, tare da yaba musu. Yabon da ya dace, ba yabo irin na banbadanci ba!!!.

 

Daga Tarihin Lagos Da Samuwar “Yan Majalisun Kasa, 1874 – 1886 – 1914

Tarihi ya tabbatar da cewa, cikin Shekarar 1861 ce yankin Lagos ya fada karkashin ikon Sarauniyar Ingila, ko ace Masarautar Birtaniya. Haka lamura suka ci gaba da gudana har zuwa tsakanin Shekarun 1874 zuwa 1886, inda aka nada gwamna, wanda shi ke da ikon tafiyar da harkokin mulki, a wuraren dake karkashin mulkin Turawan Birtaniya a kafatanin kasashen yammacin Afurka. Sai dai wannan gwamna, na zaune ne a can yankin kasar da a yanzu ake kiranta da Sierra Leone. Kasar da akasarinmu ke kira da Salo.

Kamar yadda aka fara 6incinawa, a Shekarar da aka hade yankin Kudanci da na Arewacin wannan kasa (1914) ne, Turawan Birtaniya suka kyankyashe wasu dokoki guda uku (3), wadanda guda daga dokokin ne ta tabbatar da ikon kirkirar kunshin “yan majalisu na farko a tarihin siyasar Nijeriyar da take amsa sunanta na Nijeriya a jiya da yau. Ga kunshin wadancan dokoki uku kamar haka;

i- “The Nigeria Council Order-in-Council (1910)”.

ii- “The Letters Patent (1913)”, sannan

iii- “The Nigeria Protectorate Order-in-Council (1913)” (Constitutional Conference Report, 1995: 43). Kunshin doka ta biyu, wato” The Nigeria Council Order-in-Council (1910)” ita ce ta samar da “yan majalisun farko a wannan kasa tamu. Sannu a hankali, za a faiyacewa mai karatu irin karfin iko ko akasinsa, da wannan zaure na “yan majalisun ke da shi, a jiya da yau.

 

Dalilan Kirkirar “Yan Majalisun

Kamar yadda a baya aka fadi cewa, a farkon lamari, yankin gundumar Lagos ne kadai ke da kunshin “yan majalisu, gabanin hade kudanci da arewacin kasar, tare da rada masa sunan Nijeriya. Yayin da aka hade Kasar zuwa ga wani abu guda, ta tabbata a zahiri cewa, wancan kunshin tsaffin “yan majalisun Lagos na farko, taraiyar kasar sun yi musu dangangan, ko ace girma, wajen iya tafiyar da lamuranta baki daya. Wannan dalili, ya jaza kirkirar kunshin “yan majalisun, wadanda wakilcinsu zai ratsa ne zuwa ga sasannin kudanci da kuma na arewacin kasar. Dalili na biyu da ya bukatar da kafa “yan majalisun shi ne, ta tabbata cewa, muddin gwamna da gwamnatin Birtaniya ta samar da shi, karkashin kunshin dokar “The Letters Patent (1913)” na da muradin jin ra’ayoyin jama’ar kudanci da na arewacin Kasar da aka hade waje guda baki daya, to fa babu makawa, sai an samar da gungun “yan majalisun a duka bangarori biyu na kasar. A karkashin doka ta bai daya a kasa da aka samar, wadannan ne “yan majalisa na farko, wanda adadinsu ya riski mutum talatin da shida ne cifcif (36). Sai dai, shida (6) kacal daga cikinsu ne jama’ar Nijeriya ke da ikon zabowa, don wakiltar bangarorinsu (Fagge & Alabi, 2007: 53-54).

Yana da kyau mai karatu ya sani cewa, an mirgina matakai da yanayai iri daban-daban, gabanin “yan majalisun na jihohi da na tarayya musamman, su sami kaiwa ga mamakon ikon da suka riska a yau. Sai dai, shin, riskar ikon nasu a yau, yana yin tasiri mai kyau ga ci gaban jama’ar kasa ne koko a’a?. Cikin bayanai da za a kutsa can gaba, duk dan Nijeriya akili kuma managarci, zai kai ga fahimtar cikakkiyar amsar wannan tambaya.

Majalisun
Muktar Anwar
+ postsBio
  • Muktar Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/muktar-anwar/
    Budaddiyar Wasika Ga Gwamnan Kano Abba K. Yusuf
  • Muktar Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/muktar-anwar/
    Yaduwar Juyin Mulki A Afirka
  • Muktar Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/muktar-anwar/
    Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  • Muktar Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/muktar-anwar/
    Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

MASU ALAKA

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
obi
Bakon Marubuci

Su Wa Ke Fatattakar Obi Da Kwankwaso?

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Bakon Marubuci

Hanyoyin Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuradiyyar Nijeriya

May 10, 2026
Next Post
Wang Yi: Diflomasiyyar Kasar Sin Ta Samar Da Kwanciyar Hankalin Da Ake Bukata A Duniya Mai Cike Da Rikici

Wang Yi: Diflomasiyyar Kasar Sin Ta Samar Da Kwanciyar Hankalin Da Ake Bukata A Duniya Mai Cike Da Rikici

LABARAI MASU NASABA

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

June 5, 2026
Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 5, 2026
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

June 5, 2026
Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.