ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karin Kudin Lantarki Da Na Kira: Kungiyar Kwadago Ta Yi Barazanar Shirya Zanga-zanga A Fadin Nijeriya

by Khalid Idris Doya
1 year ago
Lantarki

Kungiyar kwadago ta kasa ta yi shirin yin zanga – zanga ta kasa baki daya saboda lamarin daya shafi karin kudin wutar lantarki da na kira, musamman ma kudin lantarkin da ake son a bar amfani da mafi arha /sauki da ake kira da suna (Band A).

Hakanne ya sa kungiyar ta yi kira da abokan gwagwarmayar su kasance cikin shirin kota- kwana na yin zanga- zanga da zata shafi kasa baki daya saboda karin kudin wutar lantarki dana kira.

  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 92, Sun Kubutar Da Mutane 75 A Cikin Mako Guda – DHQ
  • Shugaban NAN:Muna Iya Ganin Basirar Sin Ta Manyan Taruka Biyu Da Take Gudanarwa Yanzu

An dauki shi matakin ne bayan taron da aka yi na Shugabannin kungyar a Yola hedikwatar Jihar Adamawa.

ADVERTISEMENT

Halin da ake ciki dai yanzu ya nuna kungiyar ta yi shakkun idan gwamnatin tarayya za ta iya aiwatar da yarjeniyar da ta cimmawa da ita, da aka uyi ranar 25 ga watan Fabrairu 2025, lokacin da kwamitin mutum 10 wanda ya rage karin kudin da za a biya daga kashi 50 zuwa kashi 35.

Kungiyar kwadagon ta ja kunne inda ta ce ba za ta yi kasa a gwiwa ba, matukar idan aka fara aikin da karin bai yi daidai da na kashi 35 ba, da take tsammani ba,za ta dauki matakin da ta yi niyyar.

LABARAI MASU NASABA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

Kungiyar ta yi tir da tsarin da hukumar kulawa wutar lantarki ta yi,wanda take neman ta ba masu amfani da wuta, nau’i- nau’in da suke ko ta kai su,ba domin komai ba don wata magana ta kara bunkasa samun wutar lantarki fiye da irin halin da ake ciki yanzu.

Kamar dai yadda kungiyar tace tsarin Hukumar wani kokari ne na karin kudin wutar lantarki na sauyawa masu amfani da wuta daga tsarin da suka saba amfani da shi mai sauki zuwa ga wanda zai kasance wanda yake mai tsada.

A sanarwar da aka fitar Shugaban kungiyar da Sakatarenta Kwamrade Joe Ajaero Komrade Emmanuel Ugboaja wadda ta ce tsarin da ake shirin yi tamkar “yin laifi ne ga tattalin arzikin kasa.”

Kungiyar NLC ta ga laifin ita hukumar NERC da ma’aikatar wutar lantarki da shirin gallazawa ‘yan Nijeriya wadanda suke rayuwa ta hannu baka- hannu kwarya.

Bugu da kari kungiyar ta kara da cewa muddin aka yi wani karin kudin wutar lantarki dana kira, hakan zai sa Talakawa sun yi zanga- zanga ta kasa baki daya. Domin kuwa ma’aikata da Talakawa ba za su iya hakurin irin tsaren tsaren takura na gwamnati ba.

Ga dai yadda sanarwar take: “Kwamitin zartarwa na kungiyar kwadago ya yanke shawarar daukar mataki idan aka kasa amfani matsayar da aka cimmawa ranar 1 ga Maris 2025, ba ayi hakan ba, ba tare da bata lokaci ba an sai kwamitin zartarwa na kasa da aka dorawa alhakin daukar mataki kamar dai lamarin yake abin yake a ranar10 ga Fabrairu 2025.

“Kan shirin komawa tsarin karin kudin wutar lantarkin, majalisar zartarwar kungiyar kwadago ta yi watsi da duk wani shirin da Hukumar (NERC), yadda ake neman tursasawa masu amfani da tsarin (B) su koma tsarin (A) a karkashin wani tsarin wayo da ake kiran shi domin a kara bunkasa samar da wutar lantarki, bayan kuwa maganar gaskiya ana shiri ne na gallazawa masu amfani da wutar lantarki.

“Tsarin shirin ma’aikatar wutar lantarki ba wani abu bane illa kamar kokarin da ake yi ne na gallazawa da takurawa Talakawa wadanda suke kokarin tafiyar da rayuwarsu cikin halin kunci.”

Daga karshe kwamitin zartarwa na kungiyar kwadago koda wane lokaci cikin shirin shi yake na kare al’umma daga duk wata irin takurawa, nuna fifiko,don haka ta yi kira ga dukkan kungiyoyin da suke karkashinta, da masu da’awar ci gaba, su zama a cikin shirin kota-kwana, na shiga zanga-zanga ko nuna rashin amincewa da duk wani tsari na kuntatawa na manufofi ko tsare-tsare masu takurawa.

Lantarki
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

MASU ALAKA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Next Post
An Fara Gangamin Babban Taron LEADERSHIP Da Karrama Gwarazan 2024

An Fara Gangamin Babban Taron LEADERSHIP Da Karrama Gwarazan 2024

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.