ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Brazil Ta Cire Sunan Antony Daga Tawagarta Saboda Zargin Dukan Budurwarsa

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Brazil

Tawagar kwallon kafa ta kasar Brazil ta ajiye dan kwallon Manchester United, Antony daga tawagarta, wanda ake zargi da cin zarafin tsohuwar budurwarsa a birnin Soa Paulo. Hukumar kwallon kafa Brazil ta ce dan wasan mai shekara 23 ba zai buga mata karawar ba, bayan da ake zarginsa, wanda kawo yanzu tuni aka fara bincike akan zargin.

Ranar Litinin wata jarida ta Brazil ta wallafa labarin zargin cin zarafin da Anthony ya yi wa tsohuwar budurwarsa kuma tuni ‘yansanda a Sao Paulo da na Greater Manchester na bincikar lamarin, yayin da dan kwallon ke musanta zargin.

  • Shugaban Kasar Sin Ya Yi Tattaki Zuwa Wani Karamin Kauyen Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa
  • Neymar Ya Zarce Pele A Matsayin Wanda Yafi Zurawa Kasar Brazil Kwallaye

Ana zargin Antony da farwa tsohuwar budurwarsa, Gabriela Caballin wacce ya yi wa gware da ka a wani otal a Manchester ranar 15 ga watan Janairun wannan shekarar da muke ciki. Hakan ya sa ta ji ciwo a kanta da ta kai likitoci suka yi mata aiki sannan ta kuma yi zargin cewa ya naushe ta a kirji da ta kai ya yi mata illa da sai da aka yi mata aiki a cewarta.

ADVERTISEMENT

Antony ya bayyana a wata sanarwa cewar alakarsa da tsohuwar budurwarsa sun saba yin hatsaniya, amma bai taba dukanta ko cin zarafinta ba, sannan ya taba fitar da wata sanarwa a cikin watan Yuni cewar tsohuwar budurwarsa na yi masa zargin karya na cin zarafi.

Manchester United ta ce babu abin da za ta ce kan batun, sai dai lamarin Antony ya taso ne bayan da kungiyarta sanar da cewar dan wasanta Mason Greenwood zai bar kungiyar, bayan wata shida da aka zarge shi da cin zarafi.

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

Cikin zargin da aka soke kan Greenwood har da batun fyade da cin zarafi, sai dai tuni dan wasan mai shekara 21 a duniya ya koma Getafe ta Sifaniya da zai yi mata wasannin aro.

Brazil ta maye gurbin Antony da dan kwallon Arsenal, Gabriel Jesus, wanda ya dawo daga jinya a wasan neman gurbin shiga gasar kofin duniya da za ta kara da kasashen Bolibia da kuma Peru.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe
Wasanni

Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

November 14, 2025
Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati
Wasanni

Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

November 14, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
Manyan Labarai

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
Next Post
Gwamna Idris Ya Nada Dan Marigayi Sheikh Giro Mukami A Hukumar Alhazai Ta Kebbi

Gwamna Idris Ya Nada Dan Marigayi Sheikh Giro Mukami A Hukumar Alhazai Ta Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah 

Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah 

November 14, 2025
Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma: Martani

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma: Martani

November 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

November 14, 2025
Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

November 14, 2025
Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

November 14, 2025
Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

November 14, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

November 14, 2025
Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

November 14, 2025
Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

November 14, 2025
Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.