• English
  • Business News
Thursday, July 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Brazil Ta Cire Sunan Antony Daga Tawagarta Saboda Zargin Dukan Budurwarsa

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
Brazil Ta Cire Sunan Antony Daga Tawagarta Saboda Zargin Dukan Budurwarsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tawagar kwallon kafa ta kasar Brazil ta ajiye dan kwallon Manchester United, Antony daga tawagarta, wanda ake zargi da cin zarafin tsohuwar budurwarsa a birnin Soa Paulo. Hukumar kwallon kafa Brazil ta ce dan wasan mai shekara 23 ba zai buga mata karawar ba, bayan da ake zarginsa, wanda kawo yanzu tuni aka fara bincike akan zargin.

Ranar Litinin wata jarida ta Brazil ta wallafa labarin zargin cin zarafin da Anthony ya yi wa tsohuwar budurwarsa kuma tuni ‘yansanda a Sao Paulo da na Greater Manchester na bincikar lamarin, yayin da dan kwallon ke musanta zargin.

  • Shugaban Kasar Sin Ya Yi Tattaki Zuwa Wani Karamin Kauyen Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa
  • Neymar Ya Zarce Pele A Matsayin Wanda Yafi Zurawa Kasar Brazil Kwallaye

Ana zargin Antony da farwa tsohuwar budurwarsa, Gabriela Caballin wacce ya yi wa gware da ka a wani otal a Manchester ranar 15 ga watan Janairun wannan shekarar da muke ciki. Hakan ya sa ta ji ciwo a kanta da ta kai likitoci suka yi mata aiki sannan ta kuma yi zargin cewa ya naushe ta a kirji da ta kai ya yi mata illa da sai da aka yi mata aiki a cewarta.

Antony ya bayyana a wata sanarwa cewar alakarsa da tsohuwar budurwarsa sun saba yin hatsaniya, amma bai taba dukanta ko cin zarafinta ba, sannan ya taba fitar da wata sanarwa a cikin watan Yuni cewar tsohuwar budurwarsa na yi masa zargin karya na cin zarafi.

Manchester United ta ce babu abin da za ta ce kan batun, sai dai lamarin Antony ya taso ne bayan da kungiyarta sanar da cewar dan wasanta Mason Greenwood zai bar kungiyar, bayan wata shida da aka zarge shi da cin zarafi.

Labarai Masu Nasaba

Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

Cikin zargin da aka soke kan Greenwood har da batun fyade da cin zarafi, sai dai tuni dan wasan mai shekara 21 a duniya ya koma Getafe ta Sifaniya da zai yi mata wasannin aro.

Brazil ta maye gurbin Antony da dan kwallon Arsenal, Gabriel Jesus, wanda ya dawo daga jinya a wasan neman gurbin shiga gasar kofin duniya da za ta kara da kasashen Bolibia da kuma Peru.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ronaldo Ba Zai Buga Wasa A Karawar Da Za Su Yi Da Kasar Luxembourg Ba

Next Post

Gwamna Idris Ya Nada Dan Marigayi Sheikh Giro Mukami A Hukumar Alhazai Ta Kebbi

Related

Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea
Wasanni

Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea

19 hours ago
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata
Wasanni

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

2 days ago
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari
Wasanni

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

3 days ago
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa
Wasanni

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

4 days ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Wasanni

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

5 days ago
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?
Wasanni

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

5 days ago
Next Post
Gwamna Idris Ya Nada Dan Marigayi Sheikh Giro Mukami A Hukumar Alhazai Ta Kebbi

Gwamna Idris Ya Nada Dan Marigayi Sheikh Giro Mukami A Hukumar Alhazai Ta Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

July 2, 2025
Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

July 2, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

July 2, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

July 2, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

July 2, 2025
Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

July 2, 2025
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

July 2, 2025
Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

July 2, 2025
Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

July 2, 2025
Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

July 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.