• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buguwar Zuciya: Me Ya Sa Take Faruwa Da ‘Yan Kwallo Ana Tsaka Da Wasa?

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
in Wasanni
0
Buguwar Zuciya: Me Ya Sa Take Faruwa Da ‘Yan Kwallo Ana Tsaka Da Wasa?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bugawar zuciya a lokacin da dan wasa yake tsaka da wasa dai ba sabon abu bane ga ‘yan wasa da likitoci da su kansu masu kallon kwallon kafa kuma a ko ina a fadin duniya.

Damar Hamlin, shahararren dan wasan kwallon kafar Amurka ne, shi ne dan wasa na baya-bayan nan da ya gamu da matsalar bugun zuciya yayin buga wasan kwallon kafa.

  • NIS Ta Kafa Tarihin Horas Da Jami’ai Inda Ta Yaye 1,800 Lokaci Guda A Kano 

Dan wasan mai shekara 24 a duniya ya fadi kasa lokacin da ake buga wasa bayan da suka yi karo da wani dan wasa mintoci kadan a tashi wasa kuma likitoci sun tabbatar da cewa ya gamu da bugun zuciya – wanda hakan ke nufin zuciyarsa ta daina bugawa yadda ya kamata na samar wa wasu sassan jikin jini sannan likitocin sun yi kokari wajen ganin sun ceto rayuwarsa a cikin filin kuma yanzu haka yana kwance cikin mawuyacin hali a asibiti.

Amma likitocin da suke jinyarsa ba su bayyana tatamaimen matsalar da take damunsa ba sai dai wani abu da ke janyo bugawar zuciya shi ne kaduwa wanda ake kira da commotio cordis.

A wannan yanayi, idan wani abu ya bugi kirji, hakan zai iya janyo bugawar zuciya, inda zuciya ba za ta yi aiki yadda ya kamata ba sannan wannan wani na’u’in bugun zuciya ne na daban wanda ke faruwa idan jijiyoyi suka daina samar da jini wanda hakan kan janyo matsala ga zuciya saboda nauyin bugu.

Labarai Masu Nasaba

Osimhen Ya Kammala Komawa Galatasaray

Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta

Ba’a dai san irin raunuka da Hamlin ya samu ba a cikin zuciyarsa daga karon da ya yi da wani dan wasa sannan ko zuciyar sa ta samu matsala amma wata matsala ta zuciya da ‘yan wasa ke fuskanta shi ne cuta ta zuciya da ke shafar jijiyoyi.

Mutane da ke da irin wannan matsala za a iya ganinsu cikin koshin lafiya ba tare da wasu alamu da ke nuna cewa suna fama da wata lalura ba sai dai yanayi ne da ke sanya jijiyoyin zuciya kara girma, inda hakan ke sakawa da wuya jini ya kai zuwa zuciya, wanda hakan ke nuna akwai wata matsala a kasa.

Masu gwagwarmayar adawa da rigakafi a kafofin sada zumunta sun dora laifin matsalar bugun zuciyar Hamlin kan alluran cutar korona duk da cewa ba su bayar da wata hujja ba.

Sun kuma tattara alkaluman ‘yan wasan da suka mutu domin karfafa hujjarsu sai dai, a cewar wani bincike da aka yi a shekarar 2016, akwai akalla mutane 100 zuwa 150 da ke mutuwa a Amurka sakamakon bugun zuciya a kowace shekara ya yin buga wasanni.

A watan Maris din shekarar 2022, hukumar shirya gasar kwallon kafa ta Amurka, ta ce an yi wa kashi 95 na ‘yan wasan rigakafin cutar korona kuma Hamlin dai ba shi ne dan wasa na farko ba da ya yanke jiki ya fadi ana tsaka da wasa.

Domin shi ma dan wasan kasar Denmark, Christain Eriksen, ya gamu da bugun zuciya a shekarar 2020 da ta gabata yayin buga wasa a gasar Euro 2020, inda ya kusa rasa ransa.
Likitoci sun yi amfani da wata na’ura domin farfado da zuciyarsa, inda ta dawo aiki yadda ya kamata kuma tun daga wancan lokaci aka samar da wata karamar na’ura mai suna ICD domin ci gaba da duba zuciyarsa.

Eriksen ya ce babu ko da wani a cikin iyalansa da ya taba gamuwa da matsalar bugun zuciya, saboda ana yi masa gwaji iya rayuwarsa ta kwallo kamar sauran manyan ‘yan wasa.

A shekarar 2012, wani dan wasa mai suna Fabrice Muamba, ya yanke jiki ya fadi a cikin fili a lokacin da zuciyarsa ta daina aiki sannan an samar da na’urori 15 domin farfado da zuciyarsa.

Idan aka bai wa mutum agajin lafiya ta gaggawa ya kan samu sauki amma ba ko yaushe ake samun nasarar ceto rayuwar mutum ba kuma a cewar binciken gidauniyar Cardiac Risk in the Young, mutum 12 ‘yan kasa da shekara 35 ke mutuwa a Birtaniya a kowane mako sakamakon bugun zuciya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Haramta Amfani Da Cokali Da Farantin Soso A Ingila

Next Post

Kungiyar APOSUN Ta Ziyarci Ofishin Babban Sufeton ‘Yansandan Nijeriya

Related

Osimhen Ya Kammala Komawa Galatasaray
Wasanni

Osimhen Ya Kammala Komawa Galatasaray

1 day ago
Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta
Wasanni

Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta

2 days ago
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United
Wasanni

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

3 days ago
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON
Wasanni

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

4 days ago
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

5 days ago
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu
Wasanni

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

6 days ago
Next Post
Kungiyar APOSUN Ta Ziyarci Ofishin Babban Sufeton ‘Yansandan Nijeriya

Kungiyar APOSUN Ta Ziyarci Ofishin Babban Sufeton ‘Yansandan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

August 2, 2025
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

August 2, 2025
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

August 2, 2025
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

August 2, 2025
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

August 2, 2025
Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50

Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50

August 2, 2025
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

August 2, 2025
Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa

Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa

August 2, 2025
An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo

An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.