• Leadership Hausa
Monday, January 30, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Wasanni

Buguwar Zuciya: Me Ya Sa Take Faruwa Da ‘Yan Kwallo Ana Tsaka Da Wasa?

by Abba Ibrahim Wada
2 weeks ago
in Wasanni
0
Buguwar Zuciya: Me Ya Sa Take Faruwa Da ‘Yan Kwallo Ana Tsaka Da Wasa?

Bugawar zuciya a lokacin da dan wasa yake tsaka da wasa dai ba sabon abu bane ga ‘yan wasa da likitoci da su kansu masu kallon kwallon kafa kuma a ko ina a fadin duniya.

Damar Hamlin, shahararren dan wasan kwallon kafar Amurka ne, shi ne dan wasa na baya-bayan nan da ya gamu da matsalar bugun zuciya yayin buga wasan kwallon kafa.

  • NIS Ta Kafa Tarihin Horas Da Jami’ai Inda Ta Yaye 1,800 Lokaci Guda A Kano 

Dan wasan mai shekara 24 a duniya ya fadi kasa lokacin da ake buga wasa bayan da suka yi karo da wani dan wasa mintoci kadan a tashi wasa kuma likitoci sun tabbatar da cewa ya gamu da bugun zuciya – wanda hakan ke nufin zuciyarsa ta daina bugawa yadda ya kamata na samar wa wasu sassan jikin jini sannan likitocin sun yi kokari wajen ganin sun ceto rayuwarsa a cikin filin kuma yanzu haka yana kwance cikin mawuyacin hali a asibiti.

Amma likitocin da suke jinyarsa ba su bayyana tatamaimen matsalar da take damunsa ba sai dai wani abu da ke janyo bugawar zuciya shi ne kaduwa wanda ake kira da commotio cordis.

A wannan yanayi, idan wani abu ya bugi kirji, hakan zai iya janyo bugawar zuciya, inda zuciya ba za ta yi aiki yadda ya kamata ba sannan wannan wani na’u’in bugun zuciya ne na daban wanda ke faruwa idan jijiyoyi suka daina samar da jini wanda hakan kan janyo matsala ga zuciya saboda nauyin bugu.

Labarai Masu Nasaba

Benzema Ya Karya Tarihin Raul Gonzalez

Da Gaske Arteta Ya Kawo Gyara A Arsenal?

Ba’a dai san irin raunuka da Hamlin ya samu ba a cikin zuciyarsa daga karon da ya yi da wani dan wasa sannan ko zuciyar sa ta samu matsala amma wata matsala ta zuciya da ‘yan wasa ke fuskanta shi ne cuta ta zuciya da ke shafar jijiyoyi.

Mutane da ke da irin wannan matsala za a iya ganinsu cikin koshin lafiya ba tare da wasu alamu da ke nuna cewa suna fama da wata lalura ba sai dai yanayi ne da ke sanya jijiyoyin zuciya kara girma, inda hakan ke sakawa da wuya jini ya kai zuwa zuciya, wanda hakan ke nuna akwai wata matsala a kasa.

Masu gwagwarmayar adawa da rigakafi a kafofin sada zumunta sun dora laifin matsalar bugun zuciyar Hamlin kan alluran cutar korona duk da cewa ba su bayar da wata hujja ba.

Sun kuma tattara alkaluman ‘yan wasan da suka mutu domin karfafa hujjarsu sai dai, a cewar wani bincike da aka yi a shekarar 2016, akwai akalla mutane 100 zuwa 150 da ke mutuwa a Amurka sakamakon bugun zuciya a kowace shekara ya yin buga wasanni.

A watan Maris din shekarar 2022, hukumar shirya gasar kwallon kafa ta Amurka, ta ce an yi wa kashi 95 na ‘yan wasan rigakafin cutar korona kuma Hamlin dai ba shi ne dan wasa na farko ba da ya yanke jiki ya fadi ana tsaka da wasa.

Domin shi ma dan wasan kasar Denmark, Christain Eriksen, ya gamu da bugun zuciya a shekarar 2020 da ta gabata yayin buga wasa a gasar Euro 2020, inda ya kusa rasa ransa.
Likitoci sun yi amfani da wata na’ura domin farfado da zuciyarsa, inda ta dawo aiki yadda ya kamata kuma tun daga wancan lokaci aka samar da wata karamar na’ura mai suna ICD domin ci gaba da duba zuciyarsa.

Eriksen ya ce babu ko da wani a cikin iyalansa da ya taba gamuwa da matsalar bugun zuciya, saboda ana yi masa gwaji iya rayuwarsa ta kwallo kamar sauran manyan ‘yan wasa.

A shekarar 2012, wani dan wasa mai suna Fabrice Muamba, ya yanke jiki ya fadi a cikin fili a lokacin da zuciyarsa ta daina aiki sannan an samar da na’urori 15 domin farfado da zuciyarsa.

Idan aka bai wa mutum agajin lafiya ta gaggawa ya kan samu sauki amma ba ko yaushe ake samun nasarar ceto rayuwar mutum ba kuma a cewar binciken gidauniyar Cardiac Risk in the Young, mutum 12 ‘yan kasa da shekara 35 ke mutuwa a Birtaniya a kowane mako sakamakon bugun zuciya.

Previous Post

Za A Haramta Amfani Da Cokali Da Farantin Soso A Ingila

Next Post

Kungiyar APOSUN Ta Ziyarci Ofishin Babban Sufeton ‘Yansandan Nijeriya

Related

Benzema Ya Karya Tarihin Raul Gonzalez
Wasanni

Benzema Ya Karya Tarihin Raul Gonzalez

2 days ago
Da Gaske Arteta Ya Kawo Gyara A Arsenal?
Wasanni

Da Gaske Arteta Ya Kawo Gyara A Arsenal?

2 days ago
An Yi Gwanjon Rigar Da Pele Ya Buga Kofin Duniya Na Karshe Da Ita
Wasanni

An Yi Gwanjon Rigar Da Pele Ya Buga Kofin Duniya Na Karshe Da Ita

2 days ago
Arsenal Ta Kafa Tarihin Da Bata Taba Kafa Wa Ba
Wasanni

Arsenal Ta Kafa Tarihin Da Bata Taba Kafa Wa Ba

1 week ago
Ba Zan Bar Liverpool Ba Sai Dai A Kore Ni, Cewar Klopp
Wasanni

Ba Zan Bar Liverpool Ba Sai Dai A Kore Ni, Cewar Klopp

1 week ago
Barcelona Ta Dawo Cikin Hayyacinta – Cewar Laporta
Wasanni

Barcelona Ta Dawo Cikin Hayyacinta – Cewar Laporta

1 week ago
Next Post
Kungiyar APOSUN Ta Ziyarci Ofishin Babban Sufeton ‘Yansandan Nijeriya

Kungiyar APOSUN Ta Ziyarci Ofishin Babban Sufeton ‘Yansandan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Shawo Kan Amfani Da Karfin Tuwo Da Jami’an Tsaro Ke Yi Kan Fararen Hula

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Shawo Kan Amfani Da Karfin Tuwo Da Jami’an Tsaro Ke Yi Kan Fararen Hula

January 30, 2023
Sin: An Samu Karuwar Sayayyar Amfanin Gona Ta Yanar Gizo A 2022 

Sin: An Samu Karuwar Sayayyar Amfanin Gona Ta Yanar Gizo A 2022 

January 30, 2023
Wannan Sabuwar Tashar Jirgin Ruwa Ta Shaida Wani Tunani Mai Muhimmanci

Wannan Sabuwar Tashar Jirgin Ruwa Ta Shaida Wani Tunani Mai Muhimmanci

January 30, 2023
Ban Da Tyre Nichols, Wane Ne mutum Na Gaba Da ’Yan Sandan Amurka Za Su Yi Ajalinsa? 

Ban Da Tyre Nichols, Wane Ne mutum Na Gaba Da ’Yan Sandan Amurka Za Su Yi Ajalinsa? 

January 30, 2023
Gogewar Kasar Sin A Fannonin Ilimi Da Binciken Kimiyya, Abun Karfafa Gwiwa Ne Ga Kasashen Larabawa 

Gogewar Kasar Sin A Fannonin Ilimi Da Binciken Kimiyya, Abun Karfafa Gwiwa Ne Ga Kasashen Larabawa 

January 30, 2023
Babban Kwamatin Ayyuka Na Jam’iyyar PDP Na kasa Ya Gana Da ‘Yan Takarar Gwamna Na Jam’iyyar

‘Yan Majalisar Tarayya 3 Na Jam’iyyar APC Sun Koma Jam’iyyar PDP A Jihar Katsina

January 30, 2023
Kasar Sin Ta Tsawaita Wasu Dabarunta Na Kudi

Kasar Sin Ta Tsawaita Wasu Dabarunta Na Kudi

January 30, 2023
DSS Ta Kama Wasu Ma’aikatan Banki Masu Hada-hadar Sayar Da Sabbin Kudaden Naira

DSS Ta Kama Wasu Ma’aikatan Banki Masu Hada-hadar Sayar Da Sabbin Kudaden Naira

January 30, 2023
Tsohon Firaministan Kenya, Odinga, Ya Iso Nijeriya Don Halartar Taron LEADERSHIP Na 14

Tsohon Firaministan Kenya, Odinga, Ya Iso Nijeriya Don Halartar Taron LEADERSHIP Na 14

January 30, 2023
Jirgin Kasan Kaduna-Abuja Ya Dawo Aikin Jigilar Fasinjojinsa Bayan Hatsarin Da Ya Yi

Jirgin Kasan Kaduna-Abuja Ya Dawo Aikin Jigilar Fasinjojinsa Bayan Hatsarin Da Ya Yi

January 30, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.