ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buguwar Zuciya: Me Ya Sa Take Faruwa Da ‘Yan Kwallo Ana Tsaka Da Wasa?

by Abba Ibrahim Wada
4 years ago
Buguwar zuciya

Bugawar zuciya a lokacin da dan wasa yake tsaka da wasa dai ba sabon abu bane ga ‘yan wasa da likitoci da su kansu masu kallon kwallon kafa kuma a ko ina a fadin duniya.

Damar Hamlin, shahararren dan wasan kwallon kafar Amurka ne, shi ne dan wasa na baya-bayan nan da ya gamu da matsalar bugun zuciya yayin buga wasan kwallon kafa.

  • NIS Ta Kafa Tarihin Horas Da Jami’ai Inda Ta Yaye 1,800 Lokaci Guda A Kano 

Dan wasan mai shekara 24 a duniya ya fadi kasa lokacin da ake buga wasa bayan da suka yi karo da wani dan wasa mintoci kadan a tashi wasa kuma likitoci sun tabbatar da cewa ya gamu da bugun zuciya – wanda hakan ke nufin zuciyarsa ta daina bugawa yadda ya kamata na samar wa wasu sassan jikin jini sannan likitocin sun yi kokari wajen ganin sun ceto rayuwarsa a cikin filin kuma yanzu haka yana kwance cikin mawuyacin hali a asibiti.

ADVERTISEMENT

Amma likitocin da suke jinyarsa ba su bayyana tatamaimen matsalar da take damunsa ba sai dai wani abu da ke janyo bugawar zuciya shi ne kaduwa wanda ake kira da commotio cordis.

A wannan yanayi, idan wani abu ya bugi kirji, hakan zai iya janyo bugawar zuciya, inda zuciya ba za ta yi aiki yadda ya kamata ba sannan wannan wani na’u’in bugun zuciya ne na daban wanda ke faruwa idan jijiyoyi suka daina samar da jini wanda hakan kan janyo matsala ga zuciya saboda nauyin bugu.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

Ba’a dai san irin raunuka da Hamlin ya samu ba a cikin zuciyarsa daga karon da ya yi da wani dan wasa sannan ko zuciyar sa ta samu matsala amma wata matsala ta zuciya da ‘yan wasa ke fuskanta shi ne cuta ta zuciya da ke shafar jijiyoyi.

Mutane da ke da irin wannan matsala za a iya ganinsu cikin koshin lafiya ba tare da wasu alamu da ke nuna cewa suna fama da wata lalura ba sai dai yanayi ne da ke sanya jijiyoyin zuciya kara girma, inda hakan ke sakawa da wuya jini ya kai zuwa zuciya, wanda hakan ke nuna akwai wata matsala a kasa.

Masu gwagwarmayar adawa da rigakafi a kafofin sada zumunta sun dora laifin matsalar bugun zuciyar Hamlin kan alluran cutar korona duk da cewa ba su bayar da wata hujja ba.

Sun kuma tattara alkaluman ‘yan wasan da suka mutu domin karfafa hujjarsu sai dai, a cewar wani bincike da aka yi a shekarar 2016, akwai akalla mutane 100 zuwa 150 da ke mutuwa a Amurka sakamakon bugun zuciya a kowace shekara ya yin buga wasanni.

A watan Maris din shekarar 2022, hukumar shirya gasar kwallon kafa ta Amurka, ta ce an yi wa kashi 95 na ‘yan wasan rigakafin cutar korona kuma Hamlin dai ba shi ne dan wasa na farko ba da ya yanke jiki ya fadi ana tsaka da wasa.

Domin shi ma dan wasan kasar Denmark, Christain Eriksen, ya gamu da bugun zuciya a shekarar 2020 da ta gabata yayin buga wasa a gasar Euro 2020, inda ya kusa rasa ransa.
Likitoci sun yi amfani da wata na’ura domin farfado da zuciyarsa, inda ta dawo aiki yadda ya kamata kuma tun daga wancan lokaci aka samar da wata karamar na’ura mai suna ICD domin ci gaba da duba zuciyarsa.

Eriksen ya ce babu ko da wani a cikin iyalansa da ya taba gamuwa da matsalar bugun zuciya, saboda ana yi masa gwaji iya rayuwarsa ta kwallo kamar sauran manyan ‘yan wasa.

A shekarar 2012, wani dan wasa mai suna Fabrice Muamba, ya yanke jiki ya fadi a cikin fili a lokacin da zuciyarsa ta daina aiki sannan an samar da na’urori 15 domin farfado da zuciyarsa.

Idan aka bai wa mutum agajin lafiya ta gaggawa ya kan samu sauki amma ba ko yaushe ake samun nasarar ceto rayuwar mutum ba kuma a cewar binciken gidauniyar Cardiac Risk in the Young, mutum 12 ‘yan kasa da shekara 35 ke mutuwa a Birtaniya a kowane mako sakamakon bugun zuciya.

Buguwar zuciya
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Fara Kofin Zakarun Turai
  • Abba Ibrahim Wada
    Messi Ya Yi Ritaya A Argentina: Da Me Za Mu Iya Tuna Gwarzon Duniyar?
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye ‘Yan wasan Nijeriya Da Za Su Buga Gasar Firimiyar Ingila Ta Bana?
  • Abba Ibrahim Wada
    Chelsea A Ƙarƙashin Xavi Alonso

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
Kungiyar APOSUN Ta Ziyarci Ofishin Babban Sufeton ‘Yansandan Nijeriya

Kungiyar APOSUN Ta Ziyarci Ofishin Babban Sufeton ‘Yansandan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.