• English
  • Business News
Friday, August 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Gaza Gudanar Da Sahihin Zabe A 2023 – Kwankwaso

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, Sanata Rabi’u Kwankwaso ya zargi Shugaban kasa Muhammadu Buhari da gaza gudanar da sahihin zabe a 2023.

Ya ce shugaban kasar bai yi abin da ya dace ba don ganin an gudanar da sahihin zabe.
Ya kuma zargi jam’iyyar APC mai mulki da yin magudin zabe a wasu jihohi, musamman zaben shugaban kasa.

  • Shugaban Jam’iyyar NNPP Na Kasa, Ya Yi Murabus Daga Mukaminsa

Kwankwaso ya yi zargin cewa sakamakon zaben da aka kammala ba zabin ‘yan Nijeriya ba ne.

Da yake magana a taron farko bayan zaben 2023 na majalisar zartaswar jam’iyyar NNPP ta kasa, tsohon ministan tsaro kuma tsohon gwamnan Jihar Kano har sau biyu ya koka da yadda ‘yan Nijeriya ba su sami damar cin moriyar canji mai kyau da suke nema ba.

Ya kuma bayyana cewa ‘yan Nijeriya sun gaji da jam’iyya mai mulki, domin ya ci gaba da cewa APC ta koma sayen kuri’u da kudaden gida da na waje, da kuma yin amfani da ‘yan daba wajen murkushe ‘yancin zabe.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Sanata Kwankwaso ya yi kira na musamman ga Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Ganduje, wanda ya zarga da shigo da ‘yan daba daga jihohi da kasashe makwabta, kamar yadda ya kuma yi nuni cewa akwai sa hannun wasu jami’an tsaro a tashe-tashen hankula da suka shafi zabe.

A yayin da yake zargin ‘yan siyasa da cewa da gangan suke talauta ‘yan Nijeriya domin su sayi kuri’a a lokacin zabe, ya yi gargadin a guji cin nasara ko ta halin kaka, domin ya koka da yadda rashin adalci ke haifar da ‘yan fashi, Boko Haram, da sauran rikice-rikicen da suka addabi kasar nan.

Jagoran NNPP na kasa ya yi nadamar cewa akwai abubuwa da yawa da ke damun dimokuradiyyar Nijeriya. Inda ya ce mutane kalilan ne ke amfana da tsarin.

Yayin da yake gargadin cewa, “Nijeriya tamu ce kuma babu wanda ya isa ya kore mu a ciki “, jagoran ya bayyana fatansa cewa bangaren shari’a ya kasance wuri mafi kyau a gare mu duka.”

Ya yi kira ga shugabannin jam’iyyar NNPP da su yi amfani da damar da aka ba su kafin zaben 2027, su zage-dantse wajen gudanar da ayyukan da suka dace a mazabarsu.

Hakan na zuwa ne yayin da ya yi kira ga Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) da ta inganta harkokinta wajen gudanar da zabuka a nan gaba, inda ya koka da yadda ba a buga tambarin jam’iyyar a kan takardun zabe ba, don haka ya sa jam’iyyarsa ta rasa kuri’an magoya bayanta a wasu wurare.

Ya bayyana cewa hatta wasu masu sa ido na kasa da kasa sun kasa tantance tambarin jam’iyyar NNPP da ke cikin takardun zabe.

Don haka, ya yaba wa jam’iyyar bisa nasarorin da suka samu, inda ya bayyana cewa mutane da dama ne ke neman shiga kafin zaben 2027.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kungiyar Mawallafa Labarai Ta Zariya Ta Mika Ta’aziyyarta Ga Editan LEADERSHIP Bisa Rasuwar Mahaifinsa

Next Post

‘Yan Majalisu Tara Da Ke Zawarcin Kujerar Gbajabiamila

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

2 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

2 weeks ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

3 weeks ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

3 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

4 weeks ago
Next Post
‘Yan Majalisu Tara Da Ke Zawarcin Kujerar Gbajabiamila

'Yan Majalisu Tara Da Ke Zawarcin Kujerar Gbajabiamila

LABARAI MASU NASABA

Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa

Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa

August 8, 2025
Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

August 8, 2025
Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

August 8, 2025
GORON JUMA’A 8-8-2025

GORON JUMA’A 8-8-2025

August 8, 2025
Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno

Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno

August 8, 2025
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

August 8, 2025
Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu

Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu

August 8, 2025
Mamakon Ruwan Sama A Wasu Jihohi Na Barazana Ga Harkokin Yau Da Kullum

Mamakon Ruwan Sama A Wasu Jihohi Na Barazana Ga Harkokin Yau Da Kullum

August 8, 2025
Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 

Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 

August 8, 2025
Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.