• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Gaza Gudanar Da Sahihin Zabe A 2023 – Kwankwaso

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, Sanata Rabi’u Kwankwaso ya zargi Shugaban kasa Muhammadu Buhari da gaza gudanar da sahihin zabe a 2023.

Ya ce shugaban kasar bai yi abin da ya dace ba don ganin an gudanar da sahihin zabe.
Ya kuma zargi jam’iyyar APC mai mulki da yin magudin zabe a wasu jihohi, musamman zaben shugaban kasa.

  • Shugaban Jam’iyyar NNPP Na Kasa, Ya Yi Murabus Daga Mukaminsa

Kwankwaso ya yi zargin cewa sakamakon zaben da aka kammala ba zabin ‘yan Nijeriya ba ne.

Da yake magana a taron farko bayan zaben 2023 na majalisar zartaswar jam’iyyar NNPP ta kasa, tsohon ministan tsaro kuma tsohon gwamnan Jihar Kano har sau biyu ya koka da yadda ‘yan Nijeriya ba su sami damar cin moriyar canji mai kyau da suke nema ba.

Ya kuma bayyana cewa ‘yan Nijeriya sun gaji da jam’iyya mai mulki, domin ya ci gaba da cewa APC ta koma sayen kuri’u da kudaden gida da na waje, da kuma yin amfani da ‘yan daba wajen murkushe ‘yancin zabe.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

Sanata Kwankwaso ya yi kira na musamman ga Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Ganduje, wanda ya zarga da shigo da ‘yan daba daga jihohi da kasashe makwabta, kamar yadda ya kuma yi nuni cewa akwai sa hannun wasu jami’an tsaro a tashe-tashen hankula da suka shafi zabe.

A yayin da yake zargin ‘yan siyasa da cewa da gangan suke talauta ‘yan Nijeriya domin su sayi kuri’a a lokacin zabe, ya yi gargadin a guji cin nasara ko ta halin kaka, domin ya koka da yadda rashin adalci ke haifar da ‘yan fashi, Boko Haram, da sauran rikice-rikicen da suka addabi kasar nan.

Jagoran NNPP na kasa ya yi nadamar cewa akwai abubuwa da yawa da ke damun dimokuradiyyar Nijeriya. Inda ya ce mutane kalilan ne ke amfana da tsarin.

Yayin da yake gargadin cewa, “Nijeriya tamu ce kuma babu wanda ya isa ya kore mu a ciki “, jagoran ya bayyana fatansa cewa bangaren shari’a ya kasance wuri mafi kyau a gare mu duka.”

Ya yi kira ga shugabannin jam’iyyar NNPP da su yi amfani da damar da aka ba su kafin zaben 2027, su zage-dantse wajen gudanar da ayyukan da suka dace a mazabarsu.

Hakan na zuwa ne yayin da ya yi kira ga Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) da ta inganta harkokinta wajen gudanar da zabuka a nan gaba, inda ya koka da yadda ba a buga tambarin jam’iyyar a kan takardun zabe ba, don haka ya sa jam’iyyarsa ta rasa kuri’an magoya bayanta a wasu wurare.

Ya bayyana cewa hatta wasu masu sa ido na kasa da kasa sun kasa tantance tambarin jam’iyyar NNPP da ke cikin takardun zabe.

Don haka, ya yaba wa jam’iyyar bisa nasarorin da suka samu, inda ya bayyana cewa mutane da dama ne ke neman shiga kafin zaben 2027.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kungiyar Mawallafa Labarai Ta Zariya Ta Mika Ta’aziyyarta Ga Editan LEADERSHIP Bisa Rasuwar Mahaifinsa

Next Post

‘Yan Majalisu Tara Da Ke Zawarcin Kujerar Gbajabiamila

Related

Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

12 hours ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 week ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
Buhari
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
Next Post
‘Yan Majalisu Tara Da Ke Zawarcin Kujerar Gbajabiamila

'Yan Majalisu Tara Da Ke Zawarcin Kujerar Gbajabiamila

LABARAI MASU NASABA

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Buhari

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.