• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Soki Gwamnoni Kan Karkatar Da Kudaden Kananan Hukumomi

by Abubakar Abba
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Buhari Ya Soki Gwamnoni Kan Karkatar Da Kudaden Kananan Hukumomi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaba Muhammadu Buhari, ya soki gwamnonin kasar nan bisa karkatar da kudaden da ake tura wa kananan hukumomi da ke a daukacin fadin kasar.

Buhari ya yi wannan sukar ne a jawabinsa a gurin taron kwas na manyan jami’an cibiyar NIPSS karo na 44 na shekarar 2022, da ya gudana a dakin taro na fadar shugaban kasa da ke Abuja.

  • Da Dumi-Duminsa: Kotu Ta Tabbatar Da Adebutu A Matsayin Dan Takarar Gwamnan PDP A Ogun
  • An Garkame Dalibin Da Ya Soki Aisha Buhari A Gidan Yari

Shugaban wanda ya sanar da hakan a yau Alhamis, ya bayyana cewa, kowa zai yi makakin yadda gwamnonin ke karbar kudade kananan hukumomin da ke a jihohinsu da sunansu, amma a karshe gwamnonin sai su rike su.

Ya kara da cewa, irin wannan halin na gwamnonin ke kara haifar da cin hanci da rashawa a kasar nan.

Jaridar LEADERSHIP ta ruwaito cewa, wannan furucin na Buhari kan gwamonin, na zuwa ne bayan awa 24 da majalisar zartarwa ta kasa ta dora alhakkin karuwar talauci a kasar nan, musamman saboda gazawar gwamnonin wajen na bayar da ta su gudunmawar ta samar da ci gaba.

Labarai Masu Nasaba

An San Masu ÆŠaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Karamin ministan kudi da tsare-tsaren kasa, Clement Agba, ne ya sanar da hakan ga manema labarai a fadar shugaban kasa a jiya Laraba, jim kadan bayan kammala taron majalisar zartarwa, wanda shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jagoranta.

Jaridar LEADERSHIP ta ruwaito cewa, hukumar kididdigar ta kasa NBS, a kwanan baya ta sanar da cewa, ‘yan Nijeriya miliyan 133 ne ke fama da talauci.

Agba ya sanar da hakan a martanin da ya mayar na tambayar da manema labarai suka yi masa na cewa, shi da ministar kudi da tsare-tsaren kasa, Zainab Ahmed wane kokari suke yi don a rage wa akasarin ‘yan Nijeriya radadin talaucin da suke fuskanta a yanzu.

A cewarsa, gwamnatin tarayya ta hanyar shirinta na samar da saukin rayuwa ga ‘yan Nijeriya, na ci gaba da zuba kudade domin a rage wa ‘yan Nijeriya halin kuncin ruwa da suke fuskanta, inda ya bayyana cewa, kashi 72 na talaucin da ake fuskanta, ana samun hakan ne a kananan hukumomi, saboda gwamnonin su, sun yi watsi da al’ummar da ke karkara.

Agba ya kara da cewa, akasarin gwamonin, sun karkatar da yin ayyukansu ne a birane, musamman wajen gina manyan gadoji, gyaran filin jirgin sama da kuma gudanar da wasu manyan ayyuka, maimakon mayar da hankulinsu wajen raya karkara da jama’a.

Ya shawarci gwamnonin da su mayar da hankulinsu wajen samar da shirye-shiyen da za su inganta rayuwar akasarin ‘yan Nijeriya, domin a tsamo su daga cikin radadin talaucin da suke fuskanta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariGwamnoniKananan HukumomiKudadeTalauci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Gudanar Da Taron Tunawa Da Jiang Zemin A Ranar Talata Mai Zuwa

Next Post

Xi Jinping Ya Yi Shawarwari Da Shugaban Majalisar Zartaswar Turai

Related

An San Masu ÆŠaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu ÆŠaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

2 hours ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

5 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

6 hours ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

14 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

18 hours ago
Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka
Manyan Labarai

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

24 hours ago
Next Post
Xi Jinping Ya Yi Shawarwari Da Shugaban Majalisar Zartaswar Turai

Xi Jinping Ya Yi Shawarwari Da Shugaban Majalisar Zartaswar Turai

LABARAI MASU NASABA

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

August 22, 2025
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

August 22, 2025
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

August 22, 2025
An San Masu ÆŠaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

An San Masu ÆŠaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

August 22, 2025
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

August 22, 2025
Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

August 22, 2025
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

August 22, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

August 22, 2025
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.