• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Kawo Karshen Rushewar Gine-gine A Nijeriya (Ra’ayinmu)

by Sulaiman
3 years ago
in Rahotonni
0
Bukatar Kawo Karshen Rushewar Gine-gine A Nijeriya (Ra’ayinmu)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani abu mai tayar da hankali a bangaren gine-gine a Nijeriya a wannan lokacin yanzu wanda a lokutan-baya sai dai a ji labari dai-dai amma yanzu al’amarin ya zama ruwan dare, shi ne annobar rushewar gine-gine, wanda hakan ke nuna irin matsalar da bangaren gine-gine na Nijeriya ya shiga.

Rahotanni daga sassan kasar nan suna nuna yadda ake samun rugujewar gine-gine abin da ke kai ga asarar rayukar al’umma da dukiyoyin mutane da dama, mutane sun zura ido ga gwamnagti don ta samu musu mafita na yadda masu ruwa da tsaki da harkar gine-gine za su tabbatar da bin doka da oda a harkokinsu.

  • DA DUMI-DUMI: Wani Gini Mai Hawa 7 Ya Rushe A Legas

Zuwa yanzu rushewar gine-ginen da aka samu a baya ba mu ji labarin gwamnati ta dauki matakin hukunta masu hannu a kan faruwar lamarin ba, da kuma jami’an gwamnati wadanda su ke bayar da izinin yin gine-ginen da kaya marasa inganci.

Idan za a iya tunawa, a watan Satumba, mutum biyu sun mutu yayin da ma’aikata 4 suka makale a karkashin baraguzai a yayin da wani bene mai hawa 2 ya rushe a unguwar Oba Abiodun Oniru a yankin rukunin gidaje na Oniru, a Lekki ta Jihar Legas.

Yakamata ya yi a lura da cewa, Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Legas, LASEMA, ta bayyana cewa, gidaje 30 suka rushe a sassa daban-daban na Jihar Legas a tsakanin watan Janairu zuwa Yuli na 2022.

Labarai Masu Nasaba

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

Kididdiga ta baya bayan nan, kamar yadda Babban Sakataren Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Legas, Dakta Femi Oke-Osanyitolu ya nuna, ya ce, daga cikin kiran gaggawa 973 da aka yi musu mafi yawa na rugujewar gine-gine ne, an kuma fi samun wadannan kiraye-kiraye na gaggawan ne daga karamar hukumar Alimosho inda aka samu gidaje 24 da suka ruguje gaba daya da gidaje 6 da wani bangare nasu ya ruguje da kuma wani gida da yake dab da rushewa.

Hakanan kuma, rahotanni daga kafafen watsa labarai na nuna cewa, akalla mutum 84 suka rasa rayukansu a cikin gidaje 18 da suka rushe a Jihar Legas a cikin shekara 2 da suka wuce.

Kusan mako 4 kenan da rushewar wani bene mai hawa 4 a yankin Bodija da ke Ibadan a Jihar Oyo sai kuma gashi wani bene mai hawa 2 ya sake rushewa a yankin da ake magana a daren ranar Lahadin da ta wuce.

A watan da ya gabata, wani bene mai hawa 4 ya rushe a Uyo, babbar birnin Jihar Akwa Ibom inda mutane da dama suka makale a cikin baraguzan ginin.

A watan Agusta kuma, wani mutum ya mutu bayan da wani bene mai tsawo ya rushe a garin Kano inda wasu da dama suka makale. An tabbatar da mutuwar mutum biyu a watan Agusta a yayin da wani bene mai hawa 3 ya rushe a garin Kubwa da ke yankin babban birnin tarayya Abuja.

A ra’ayin wannan jaridar, muna iya cewa, a halin yanzu muna fuskantar annobar rushewar gine-gine ne a kasar nan. Abin takaicin kuma shi ne, daga shekarar 1974 zuwa watan Yuli na shekarar 2021, kididdiga ta nuna cewa, gidaje 461 suka rushe a Nijeriya inda fiye da mutum 1,090 suka mutu wasu kuma suka rasa rayukansu.

A ‘yan shekarun nan an samu rushewar gini 295 a Jihar Legas, Abuja 16, Oyo, 16, Anambra 15, Kano 9, Ondo 10, Abia 9, Kwara 8, Ribers 8, Delta 8, Enugu 7, Ogun 7, Plateau 6, Kaduna 6, Edo 6, Imo 5, Osun 5, Benue 3, Adamawa 3, a Jihar Ebonyi kuma guda 3. An samu rushewar gini 2 a Neja, Kebbi 2, Ekiti 2, Cross Riber 2, Sokoto 1, Bauchi 1, Akwa-Ibom, Kogi 1, Jihar Katsina kuma gini 1.

Masana sun dora alhakin yawan rushewar gine-ginen kan yadda ake amfani da kayan aiki marasa inganci da rashin bin ainihin taswirar da aka samar don ginin da kuma rashin yin binciken da ya kamata a a kan yanayin kasar da za a yi ginin a kai, bugu da kari kuma amfani da baragurbin ma’aikata wadanda ba su da kwarewar da ta kamata na haifar da irin wannan matsalar ta rushewar gine-gine.

Muna kira da gwamnati da a tabbatar da an gano tare da hukunta dukkan kwararrun da ke da hannu a gidajen da suka rushe da wadanda suka zuba jari a harkar ginin da ya rushe, wannan zai zama darasi ga masu daukar aikin da ya rataya a kan da muhimmanci.

Ya kuma kamata gwamnati ta tabbatar da bin dokoki da ka’idojin da ke tattare da gine-gine a Nijeriya tare da hukunta duk wani jami’in da aka samu yana sakosako da ayyukansa wanda hakan ya kai ga rushewar gini a fadin tarayyar Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

DA DUMI-DUMI: An Sanya Wa ‘Yan Nijeriya Dokar Hana Samun Izinin Shiga Dubai

Next Post

Wakilan Amurka Da Rasha Sun Tattauna Kan Batun Yakin Ukraine

Related

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

1 day ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

7 days ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

7 days ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

2 weeks ago
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

2 months ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

2 months ago
Next Post
Wakilan Amurka Da Rasha Sun Tattauna Kan Batun Yakin Ukraine

Wakilan Amurka Da Rasha Sun Tattauna Kan Batun Yakin Ukraine

LABARAI MASU NASABA

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.