• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Kawo Karshen Rushewar Gine-gine A Nijeriya (Ra’ayinmu)

by Sulaiman
3 years ago
in Rahotonni
0
Bukatar Kawo Karshen Rushewar Gine-gine A Nijeriya (Ra’ayinmu)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani abu mai tayar da hankali a bangaren gine-gine a Nijeriya a wannan lokacin yanzu wanda a lokutan-baya sai dai a ji labari dai-dai amma yanzu al’amarin ya zama ruwan dare, shi ne annobar rushewar gine-gine, wanda hakan ke nuna irin matsalar da bangaren gine-gine na Nijeriya ya shiga.

Rahotanni daga sassan kasar nan suna nuna yadda ake samun rugujewar gine-gine abin da ke kai ga asarar rayukar al’umma da dukiyoyin mutane da dama, mutane sun zura ido ga gwamnagti don ta samu musu mafita na yadda masu ruwa da tsaki da harkar gine-gine za su tabbatar da bin doka da oda a harkokinsu.

  • DA DUMI-DUMI: Wani Gini Mai Hawa 7 Ya Rushe A Legas

Zuwa yanzu rushewar gine-ginen da aka samu a baya ba mu ji labarin gwamnati ta dauki matakin hukunta masu hannu a kan faruwar lamarin ba, da kuma jami’an gwamnati wadanda su ke bayar da izinin yin gine-ginen da kaya marasa inganci.

Idan za a iya tunawa, a watan Satumba, mutum biyu sun mutu yayin da ma’aikata 4 suka makale a karkashin baraguzai a yayin da wani bene mai hawa 2 ya rushe a unguwar Oba Abiodun Oniru a yankin rukunin gidaje na Oniru, a Lekki ta Jihar Legas.

Yakamata ya yi a lura da cewa, Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Legas, LASEMA, ta bayyana cewa, gidaje 30 suka rushe a sassa daban-daban na Jihar Legas a tsakanin watan Janairu zuwa Yuli na 2022.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Kididdiga ta baya bayan nan, kamar yadda Babban Sakataren Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Legas, Dakta Femi Oke-Osanyitolu ya nuna, ya ce, daga cikin kiran gaggawa 973 da aka yi musu mafi yawa na rugujewar gine-gine ne, an kuma fi samun wadannan kiraye-kiraye na gaggawan ne daga karamar hukumar Alimosho inda aka samu gidaje 24 da suka ruguje gaba daya da gidaje 6 da wani bangare nasu ya ruguje da kuma wani gida da yake dab da rushewa.

Hakanan kuma, rahotanni daga kafafen watsa labarai na nuna cewa, akalla mutum 84 suka rasa rayukansu a cikin gidaje 18 da suka rushe a Jihar Legas a cikin shekara 2 da suka wuce.

Kusan mako 4 kenan da rushewar wani bene mai hawa 4 a yankin Bodija da ke Ibadan a Jihar Oyo sai kuma gashi wani bene mai hawa 2 ya sake rushewa a yankin da ake magana a daren ranar Lahadin da ta wuce.

A watan da ya gabata, wani bene mai hawa 4 ya rushe a Uyo, babbar birnin Jihar Akwa Ibom inda mutane da dama suka makale a cikin baraguzan ginin.

A watan Agusta kuma, wani mutum ya mutu bayan da wani bene mai tsawo ya rushe a garin Kano inda wasu da dama suka makale. An tabbatar da mutuwar mutum biyu a watan Agusta a yayin da wani bene mai hawa 3 ya rushe a garin Kubwa da ke yankin babban birnin tarayya Abuja.

A ra’ayin wannan jaridar, muna iya cewa, a halin yanzu muna fuskantar annobar rushewar gine-gine ne a kasar nan. Abin takaicin kuma shi ne, daga shekarar 1974 zuwa watan Yuli na shekarar 2021, kididdiga ta nuna cewa, gidaje 461 suka rushe a Nijeriya inda fiye da mutum 1,090 suka mutu wasu kuma suka rasa rayukansu.

A ‘yan shekarun nan an samu rushewar gini 295 a Jihar Legas, Abuja 16, Oyo, 16, Anambra 15, Kano 9, Ondo 10, Abia 9, Kwara 8, Ribers 8, Delta 8, Enugu 7, Ogun 7, Plateau 6, Kaduna 6, Edo 6, Imo 5, Osun 5, Benue 3, Adamawa 3, a Jihar Ebonyi kuma guda 3. An samu rushewar gini 2 a Neja, Kebbi 2, Ekiti 2, Cross Riber 2, Sokoto 1, Bauchi 1, Akwa-Ibom, Kogi 1, Jihar Katsina kuma gini 1.

Masana sun dora alhakin yawan rushewar gine-ginen kan yadda ake amfani da kayan aiki marasa inganci da rashin bin ainihin taswirar da aka samar don ginin da kuma rashin yin binciken da ya kamata a a kan yanayin kasar da za a yi ginin a kai, bugu da kari kuma amfani da baragurbin ma’aikata wadanda ba su da kwarewar da ta kamata na haifar da irin wannan matsalar ta rushewar gine-gine.

Muna kira da gwamnati da a tabbatar da an gano tare da hukunta dukkan kwararrun da ke da hannu a gidajen da suka rushe da wadanda suka zuba jari a harkar ginin da ya rushe, wannan zai zama darasi ga masu daukar aikin da ya rataya a kan da muhimmanci.

Ya kuma kamata gwamnati ta tabbatar da bin dokoki da ka’idojin da ke tattare da gine-gine a Nijeriya tare da hukunta duk wani jami’in da aka samu yana sakosako da ayyukansa wanda hakan ya kai ga rushewar gini a fadin tarayyar Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

DA DUMI-DUMI: An Sanya Wa ‘Yan Nijeriya Dokar Hana Samun Izinin Shiga Dubai

Next Post

Wakilan Amurka Da Rasha Sun Tattauna Kan Batun Yakin Ukraine

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2 weeks ago
Gine-gine
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

3 weeks ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

3 weeks ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

4 weeks ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

4 weeks ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 month ago
Next Post
Wakilan Amurka Da Rasha Sun Tattauna Kan Batun Yakin Ukraine

Wakilan Amurka Da Rasha Sun Tattauna Kan Batun Yakin Ukraine

LABARAI MASU NASABA

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne ÆŠantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne ÆŠantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Shahararren ÆŠan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Shahararren ÆŠan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

June 28, 2025
Hoton Tallan Taliyar Indomie

Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’

June 28, 2025
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.