ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Rogo A Duk Shekara A Nijeriya Ya Kai  Tan Miliyan 300,000, Cewar Masana

by Abubakar Abba
2 years ago
Rogo

Wasu masana a fannin noman Rogo a kasar nan, sun bayyana cewa,  bukatar da ake da ita ta Rogo don sarrafa shi zuwa sauran nau’ukan abinci ya kai tan miliyan  300,000 a duk shekara.

Sun bayyana hakan ne a lokacin wani taron masu ruwa da tsaki a fannin da suka gudanar a babban birinin tarayyar Abuja.

  • Rikicin Nijar: Tinubu Ya Aika Janar Abdulsalami, Sultan Na Sokoto Zuwa Yamai
  • Chelsea Ta Dauki Mai Tsaron Raga Daga Brighton

A cewarsu,  samar da shi ya kai kasa da tan 10,000 tonnes; haka ana kara bukatar Rogon wajen sarrafa magunguna da suka kai sama da tan 350,000.

ADVERTISEMENT

Sun kara da cewa, karin bukatar da ake da ita ta man da ake samu da ake kiransa a turance ethanol da ake yin amfani da shi wajen girki da kuma wanda ake sanya wa ababen hawa wato a kasar nan ya karu zuwa lita biliyan daya.

“Samar  da shi ya kai kasa da tan 10,000 tonnes; haka ana kara bukatar Rogon wajen sarrafa magunguna da suka kai sama da tan 350,000.”

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

Masanan sun ci gaba da cewa,  sama da kadada miliyan 24 ake noman Rogo a kasashe 106, inda suka bayyana cewa,  Nijeriya ke a kan gaba wajen samar da shi.

Kazalika, a cewarsu, amfanin  ya kasance daya daga cikin amfanin gona da ke kara karfafa tattalin arzikin duniya.

Sun sanar da cewa, bincike ya nuna cewa, Nijeriya a matsayinta ce take kan gaba wajen noman Rogo, inda  suka ce, kasar na samar da kimanin tan miliyan 53 na Rogo a duk shekarar.

Sun kara da cewa, kasr na kuma  samar da akalla tan  7.7 ako wacce kadada daya.

Sun  bayyana cewa, bisa wata kididdigar da aka fitar a kwnan baya, ta bayyana cewa, daga cikin tan miliyan 53 na Rogon da ake noma wa a Nijeriya a duk shekara.

Kazalika sun bayyana cewa, sama da kashi 90 a cikin dari  ana sarrafa Rogon zuwa sauran wasu nau’ukan abinci, inda kuma masana’antun da ke sarrafa shi a kasar suke ci gaba da nuna bukatarsa.

Hakazalika, fannin na noman Rogon ya taimaka wajen samar wa da  miliyoyin ‘yan Nijeriya aikin yi idan kuma aka inganta fannin, zai samar fiye da hakan.

“Kashi 90 a cikin dari  ana sarrafa Rogon zuwa sauran wasu nau’ukan abinci, inda kuma masana’antun da ke sarrafa shi a kasar suke ci gaba da nuna bukatarsa.”

Wasu daga cikin manoman da suka halarci taron na masu ruwa da tsaki a fannin na noman Rogon a kasar nan sun bayyana cewa, akwai bukatar gwamnatin tarayya ta kara bunkasa fannin ganin cewa, fanni ne da ke kara  bunkasa tattalin arzikin Nijeriya.

 “Nijeriya ta kasance a kan gaba wajen fitar da Rogo zuwa kasar waje, inda kuma hakan ke kara habaka mata kudaden ta ajiya a asusun kasar waje.”

Sun kuna nuna bacin ransu akan yadda  Nijeriya ke shigo da Rogon da ya kai na sama da dala miliyan 600 a duk shekara.

“Fannin na noman Rogon a kasar nan sun bayyana cewa, akwai bukatar gwamnatin tarayya ta kara bunkasa fannin ganin cewa, fanni ne da ke kara  bunkasa tattalin arzikin Nijeriya.”

Sun yi nuni da cewa, akwai matukar bukatar a samo masu zuba dimbin jarinsu a fannin, musamman don a cike gibin bukatar da ake da shi da kuma tura shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Noma Da Kiwo

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Next Post
Majalisa Ta Ki Amincewa Da Shirin Tinubu Na Daukar Matakin Soji A Kan Nijar

Majalisa Ta Ki Amincewa Da Shirin Tinubu Na Daukar Matakin Soji A Kan Nijar

LABARAI MASU NASABA

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

November 17, 2025
Tsohuwar Firaministan Bangaladesh Sheikha Hasina,

An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

November 17, 2025
Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

November 17, 2025
Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

November 17, 2025
Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.