• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Samar Wa Kotunan Korafe-korafen Zabe Kudaden Gudanarwa

by Leadership Hausa
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Bukatar Samar Wa Kotunan Korafe-korafen Zabe Kudaden Gudanarwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A daidai lokacin dababban zaben kasa na shekarar 2023 ke karatowa, kusan saura wata biyar a halin yanzu. Ana sa ran zuwa yanzu dukkan abubuwan da suka shafi harkar zaben duk an kammala su don tabbatar da gudanar da zaben tare da fuskanta da kuma warware dukkan matsalolin da za su iya tasowa daga zabukan daza a yi.

A kan wannan nemuke matukar damuwa a bisa yadda zuwa yanzu gwamnatin tarayya ba ta samar da kudade ba ga kotuna sauraron kararrakin zaben da ka iya tasowa a zaben 2023, musamman ganin tuni aka kafa kotunana fadin tarayyar kasar nan gaba daya.

  • Firaministan Habasha Ya Kaddamar Da Dakin Adana Kayan Kimiyya Da Fasaha Da Kasar Sin Ta Samar
  • Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Shafe Kwanaki 12 A Birtaniya

Bayanin da muka samu ya nuna cewa, shirye-shiryen da suka shafi horas da manyan masu shari’a, shugabannin kotuna na musamman da sauran ma’aikatan kotunan ya tsaya saboda rashin isasashen kudade wanda gwamnati ta kasa samarwa.

Shugaban Kotun Daukaka Kara, ya yi wannan koken inda ya kara da cewa, kotunan musammnan da ake da su a halin yanzu duk sun cinye kudaden da hukumar ta tanada.

Ya kuma sanar da cewa, a halin yanzu babu wani kudi a asusun hukumar da za a iya kafawa tare da gudanar da kotunan sauraron kararrakin zaben. Kotunan sauraron korafe-korafen zabe na da muhimmanci a harkokin gudanar da zabe, su ne ke sauraro korafe-korafen da ke tasowa tun daga lokacin da ake tantance masu kada kuri’a har zuwa lokacin daza a sanar da wanda ya lashe zaben gaba daya.

Labarai Masu Nasaba

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

Hakan na da matukar muhimmanci don kare aukuwar rikice-rikicen da ka iya tasowa bayan zabe tare da tabbatar da cikakken zaman lafiya a kasa. Hakki ne na Kotun Daukaka Kara kafa Kotunan sauraron kararrakin zabe, ana kuma kafa su ne tare da la’akari da tanade-tanaden sashi na 285 (2) na kundin tsarin mulkin shekarar1999 (kamar yadda aka yi wa sashi na 9 na dokar kwaskwarima a shekarar 2010).

A ka’ida, Kotun Daukaka Kara ta Tarayyya ce daga ita sai kotun koli a tsarin kotunan Nijeriya. Amma kuma Kotun Daukaka Kara ce ke tsara yadda za a gudanar da shari’un dauka kakara a tsarin shari’ar kasar nan, haka kuma hukumar kula da harkokin shari’a ce ke zabo masu shari’a a wadannan kotunan su mika wa shugaban kasa daga nan kuma majalisar Dattawa ta amince da su.

Dole masu shari’a na kotuna daukaka karar su zama suna da kwarewar gudanar da ayyukansun a Nijeriya sun kuma yi aiki a matsayin masu shari’a a Nijeriya na fiye da shekara 12.

Tsarin mulkin ya kuma tanadi cewa, masu shari’ar za su ajiye aiki in har suka kai shekara 65 a duniya. A saboda haka ya kamata a fahimci cewa, kotunan na da matukar muhimmanci a tsarin gudanar da harkokin dimokradiyya.

Kotunan na bayar da dama ga wanda yake da korafi ya tafi kai tsaye gaban kotun don mika korafinsa don neman a warware masa matsalolin da ya hango a yayin gudanar da zabukka.

Babu wani bangare na gwamnati da ke da irin wannan karfin, wannan alakar yana daga cikin zuciya da ginshikin harkar dimokradiyya. Yana da matukar muhimmanci a fahimci cewa, yin cikakken shiri a dukkan harkokin rayuwa yana tattare ne da isasshen kudi na gudanar da harkokin lamarin.

A saboda haka samar da kudi na da muhimmanci in har ana son kotunan su gudanar da ayyukansu yadda ya kamata. A kan haka muna kira ga hukumomin da ke da ruwa da tsaki da su gaggauta samar da kudaden da suka kamata ga kotunan zabe don a samu nasarar da ya kamata a zaben 2023 da ke tafe.

Tabbatar da tsayayyiyar bangaren shari’a na da matukar muhimmanci ga kokarin tabbatar da aldaci da sahihin zabe a harkar dimokracdiyya, dole a tabbatar da ana yin adalci tare da ganin adalcin a bayyane, kuma hakan ga zai taba yiwu ba har sai an samar wa da bangaren shari’a isasshen kudaden gudanar da aiki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Korafe-KorafeKotunaKudadeZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Kashe Wata Mata A Ebonyi

Next Post

Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe

Related

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

3 hours ago
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

6 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

10 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

13 hours ago
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

22 hours ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

1 day ago
Next Post
Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe

Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

September 16, 2025
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.