• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bullar Cutar Da Ke Lalata Citta Ta Sa Farashinta Ya Sake Karuwa A Karo Na Shida

by Abubakar Abba
7 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Bullar Cutar Da Ke Lalata Citta Ta Sa Farashinta Ya Sake Karuwa A Karo Na Shida
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bullar cutar da ke lalata Citta, ya sa farashinta ya karu har sau shida; cikin shekaru biyu kacal, ana sayar da duk buhu guda a kan Naira 50,000 a 2023, inda yanzu kuma farashin ya tashi zuwa Naira 300,000.

Manoman cittar, sun alakanta karin farashinta nata, sakamakon bullar wannan mummunar cuta da ke harbin ta ‘Blight’, wadda ta bulla a   2023, ta kuma jawo wa manoman asarar kimanin Naira biliyan 12.

  • Nazarin CGTN: Tsauraran Manufofin Amurka Na Shan Suka
  • Asibitin Aminu Kano Ya Musanta Cire Mahaifar Mara Lafiya Ba Tare Da Izini Ba

Ita dai wannan cuta, tana harbin jijiyar Cittar da aka shuka ne, sannan kuma tana yaduwa zuwa sauran sassan jikinta.

Har ila yau, wannan mummunar cuta, ba karamar illa take yi wa gonakin da ake yin noman wannan Citta ba, musamman a Jihar Kaduna da wasu sauran jihohin wannan kasa, wanda hakan ya yi sanadiyar sama da kashi 90 na gonakin tabka mummunar asara.

Jihar Kaduna dai, ta kasance kan gaba wajen noman Citta a fadin Nijeriya baki-daya.

Labarai Masu Nasaba

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

Wata manomiyar wannan Citta, mai suna Joy Bauna da ke Karamar Hukumar Jema’a ta Jihar Kaduna, ta koka kan irin asarar da ta tabka sakamakon wannan annobar, inda ta sanar da cewa, “Cutar ta lalata mana daukacin Cittar da muka shuka, domin kuwa duk ta rube, inda na yi asarar sama da Naira 200,000.”

“Na gaza sake yin wani noman a 2024, domin kuwa ba ni da ingantaccen Irin da zan sake shukawa”,  in ji Joy.

“Wasu daga cikinmu, ba su samu wani taimako daga wurin gwamnati ba, wanda hakan ya sa muka gaza sake yin wani noman, idan har fadin da ake yi na cewa, duk farashin buhu guda yanzu ya kai Naira 300,000, babu shakka lamarin ya munana, sai dai idan gwamnati ta taimaka mana da Iri, musamman mu kananan manoma, wannan ne zai ba mu damar sake yin wani noman a kakar bana”, a cewar Joy.

Karamin Ministan Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci, Aliyu Sabi Abdullahi ya sanar da cewa, a 2023 bayan bullar wannan cuta, manoma sun yi asarar kudi kimanin Naira biliyan 12.

Ya bayyana cewa, manoman da suka yi inshorar amfanin ne kadai, suka samu kudin dauki daga kamfanonin inshorar.

Hukumar Kula da Samar da Abinci ta Duniya (FOA) ta bayyana cewa, Nijeriya ce kan gaba wajen noman Citta a duniya, domin kuwa tana noma Cittar da yawanta ya kai kimanin tan 523,000 a duk shekara.

Kazalika, Hukumar Kula da Fitar da Kaya zuwa kasashen waje (NEPC) ta sanar da cewa, Nijeriya na da kashi 14 cikin 100 a kasuwar duniya na yawan Cittar da ake hada-hadar kasuwancinta.

“Ana fitar da kimanin kashi 90 a cikin 100 na wannan Citta, domin kuwa wadda ake nomawa a kasar nan, ta sha ban-ban da sauran wadda ake nomawa a sauran kasashe, sakamakon irin kyan da take da shi”, in ji NEPC.

Babban Shugaba, kuma Babban Sakare na Gidauniyar Bunkasa Aikin Noma ta Kasa (NADF), Mohammed Ibrahim ya bayyana cewa, a lokacin da cutar ta bulla a 2023, kimanin manoma 5,000 da ke kanannan hukumomi bakwai na Jihar Kaduna, gwamnatin tarayyya ta taimakawa da kayan noman Cittar a 2023.

Ya ce, kananan hukumomin sun hada da; Kachia, Zango-Kataf, Kaura, Kagarko, Jema’a, Jabba da kuma Sanga.

“Duk a cikin daukin bayar da kudi, gidauniyar ta NADF ta kuma taimaka wa Masa’antar Sarrafa Citta, ta ‘Illaj Ginger Factory’ da ke Jihar Kaduna, wanda hakan na daya daga cikin kokarin shirin farfado da nomanta a fadin wannan kasa”, in ji Ibrahim.

Kazalika ya sanar da cewa, an kuma kaddamar da shirin dakile yaduwar cutar, ta hanyar kirkiro da Jami’an GBECT.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CittaKiwoNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gudanar Da Shirye-Shiryen Musammam Na CMG A Spaniya Da Brazil Gabanin Bikin Bazara

Next Post

Rikicin Sudan: Gwamna Lawal Ya Bayar Da Aiki Kai Tsaye Ga Ɗaliban Zamfara 16 Da Suka Kammala Karatun Aikin Jinya

Related

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

5 hours ago
Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

2 days ago
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje
Noma Da Kiwo

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

6 days ago
Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir
Noma Da Kiwo

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

1 week ago
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

2 weeks ago
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

2 weeks ago
Next Post
Rikicin Sudan: Gwamna Lawal Ya Bayar Da Aiki Kai Tsaye Ga Ɗaliban Zamfara 16 Da Suka Kammala Karatun Aikin Jinya

Rikicin Sudan: Gwamna Lawal Ya Bayar Da Aiki Kai Tsaye Ga Ɗaliban Zamfara 16 Da Suka Kammala Karatun Aikin Jinya

LABARAI MASU NASABA

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

August 9, 2025
Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

August 9, 2025
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

August 9, 2025
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

August 9, 2025
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.