• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

China Na Neman Ƙasashe Su  Haɗe Wa Amurka Kai Sakamakon Ƙarin Haraji

by Abubakar Sulaiman
4 months ago
in Kasashen Ketare
0
China Na Neman Ƙasashe Su  Haɗe Wa Amurka Kai Sakamakon Ƙarin Haraji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jakadan ƙasar China a Nijeriya, Yu Dunhai, ya yi kira ga al’ummar duniya da su haɗa kai don yaƙi da yawan haraji da Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ke ƙara wa ƙasashe da dama, yana gargadin cewa wannan mataki na iya janyo koma baya ga tattalin arziƙin duniya tare da illoli masu tsanani musamman ga Afrika.

A lokacin taron manema labarai da ya yi a Abuja ranar Juma’a, jakadan ya jaddada cewa matakan Amurka sun take haƙƙin ƙasashe da dama, sun saɓa dokokin yarjejeniyar kasuwanci ta duniya (WTO), suna kuma kawo matsala ga tsarin ciniki na ƙasa da ƙasa da zai iya haifar da rushewar tsarin tattalin arzikin duniya.

  • Trump Ya Dakatar da Harajin Da Sanya Wa Ƙasashen Duniya, Ya Ƙi Cire Wa China
  • EFCC Ta Gurfanar Da Ɗan China A Kotu Kan Bayar Da Bayanan Ƙarya

Ya bayyana cewa, “Al’ummar duniya dole ne su haɗa kai su yaƙi wannan zalunci domin kare abubuwan da suka shafi al’umma baki ɗaya. Ya ƙalubalanci amfani da haraji a matsayin abin cin fuska ko tirsasawa daga Amurka da nufin tsayawa kan daidaito da gaskiya da kuma adalci.”

Shugaban Amurka ya ƙara tsananta haraji ga ƙasashe da dama, China tana cikin waɗanda suka fi fuskantar ƙarin haraji mai yawa, da 145% na kayan China da sazu shiga kasuwar Amurka, yayin da Beijing ta mayar da martani da haraji na 125% kan kayan Amurka.

Ƙasashe da dama ciki har da Tarayyar Turai (EU) sun ɗora haraji a kan Amurka, wanda ya sa gwamnatin Trump ta dakatar da aiwatar da sabon tsarin haraji na kwanaki 90 domin buɗe damar tattaunawa.

Jakada Dunhai ya ƙara da cewa wannan tsarin haraji yana keta ƙa’idar tattalin arziƙi da dokokin kasuwanci, da ƙin la’akari da cewa Amurka ta daɗe tana cin riba daga kasuwanci na ƙasa da ƙasa.

Labarai Masu Nasaba

An Tsare Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Cin Hanci Da Rashawa

An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati

“Amfani da haraji a matsayin makami don matsin lamba da son rai yana nuni da tsarin siyasa na rashin haɗin kai da kare tattalin arziƙi da kuma zambar tattalin arziƙi. Wannan ba abu ne na adalci ba ko mai kyau – yana nufin zaman ‘Amurka da tafi kowa’ da kuma ƙaruwar ƙarfin Amurka,” in ji shi.

Jakadan ya kuma yi gargadi cewa ƙasashe masu tasowa za su fi shan wahala daga wannan tsarin haraji, kuma hakan zai fi cutar da ƙasashen Afrika, ciki har da Nijeriya.

Ya bayyana cewa, “Amurka ta ɗauki mataki mara son Rai, na cewa ‘ samun ribar kasuwanci sai an yi zamba’ wanda ya kai ga kai wa ƙasashen Afrika haraji mai yawa, wanda ya saɓa wa ƙa’idojin WTO na bayar da kulawa ta musamman ga ƙasashen masu tasowa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfricaAmericaChinaNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dantsoho Ya Bukaci ‘Yan Kasuwa Su Yi Amafani Da Damar Fitar Da Kaya Zuwa Ketare

Next Post

Mene Ne Shirin Nukiliya Na Iran Kuma Me Amurka Ke So Ta Yi?

Related

An Tsare Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Cin Hanci Da Rashawa
Kasashen Ketare

An Tsare Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Cin Hanci Da Rashawa

2 days ago
An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati
Kasashen Ketare

An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati

1 week ago
Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka
Kasashen Ketare

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

2 weeks ago
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?
Kasashen Ketare

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

3 weeks ago
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa
Kasashen Ketare

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

3 weeks ago
Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza
Kasashen Ketare

Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

3 weeks ago
Next Post
Mene Ne Shirin Nukiliya Na Iran Kuma Me Amurka Ke So Ta Yi?

Mene Ne Shirin Nukiliya Na Iran Kuma Me Amurka Ke So Ta Yi?

LABARAI MASU NASABA

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

August 21, 2025
Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

August 21, 2025
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

August 21, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

August 21, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

August 21, 2025
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

August 21, 2025
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.