ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mene Ne Shirin Nukiliya Na Iran Kuma Me Amurka Ke So Ta Yi?

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Nukiliya

Amurka da Iran na shirin fara tattaunawa a ranar Asabar karon farko cikin tsawon shekaru da zimmar kulla sabuwar yarjejeniya kan shirin nukiliyar Iran din.

Shugaba Donald Trump ne ya cire Amurka daga yarjejeniyar da suka kulla tsakanin Iran da kasashen duniya a 2018, kuma ya saka mata takunkumai, abin da ya harzuka Iran.

  • Kwararru Sun Yi Musayar Ra’ayoyi Dangane Da Wayewar Kan Sin Da Afirka 
  • Fursunoni 62 Sun Rubuta Jarrabawar NECO da MBAIS A Kano

Trump ya yi barazanar daukar kai hare-hare kan Iran idan aka gaza cim ma yarjejeniya.

ADVERTISEMENT

Me ya sa aka hana Iran mallakar nukiliya?

Iran ta ce shirin nukiliyarta ba na kera makami ba ne, na samar da makamashi ne kawai.

LABARAI MASU NASABA

Nijar Da Canada Sun Ƙulla Yarjejeniyar Gina Sabuwar Matatar Mai A Jihar Dosso

Kotun ICC Ta Yi Watsi Da Sabbin Takunkuman Amurka Kan Jami’anta

Ta nanata cewa ba neman hada bam din nukiliya take yi ba, amma wasu kasashe – da kuma hukumar kula da makaman nukiliya ta duniya International Atomic Energy Agency (IAEA) – ba su yarda ba.

An fara zargin Iran ne game da shirin nata bayan an gano wasu boyayyun wuraren binciken nukiliya a 2002.

Hakan ya jawo karyewar wata yarjejeniya da ake kira Nuclear Non-Proliferation Treaty (NPT), wadda Iran ta kulla da wasu kasashe, wadda ta ke hana yaduwar makaman nukiliya a duniya.

NPT kan bai wa kasashe damar yin amfani da fasahar nukiliya wajen ayyukan lafiya, da noma ban da hada makamin nukiliya.

 

Yaya ci gaban shirin nukiliyar Iran yake?

Tun bayan ficewar Amurka daga yarjejeniyar da aka kira Joint Comprehensibe Plan of Action or JCPOA a 2018, Iran ta karya ka’idojinta a matsayin martani, wanda ya sa aka sake kakaba mata takunkumai.

Ta kara zuba dubban na’urorin tace ma’adanin Uranium wanda yarjejeniyar JPCOA ta haramta.

Hada makamin nukiliya na bukatar a inganta ma’adanin uranium zuwa kashi 90 cikin 100. A karkashin yarjejeniyar, an bai wa Iran damar inganta kashi 3.67 ne kawai ko kuma zuwa nauyin kilogiram 300 – wanda zai iya ba da damar ayyukan bincike amma bai kai na hada makami ba.

Amma zuwa watan Maris na 2024, hukumar IAEA ta ce Iran na da uranium kusan kilogiram 275 da ta inganta zuwa kashi 60 cikin 100. Hakan zai iya ba ta damar hada bam kamar shida idan ta kara inganta shi.

Jami’ai a Amurka sun ce sun yi imanin Iran za ta iya mayar da shi zuwa makami daya a cikin mako daya. Amma kuma sun ce Iran sai ta yi kamar shekara daya zuwa wata 18 kafin ta iya samar da cikakken makamin nukiliya.

Amma wasu kwararru na cewa za a iya gina karamin makamin cikin wata shida ko kasa da haka.

 

Me ya sa Trump ya cire Amurka daga yarjejeniyar?

Amurka da Majalisar Dinkin Duniya da Tarayyar Turai sun saka wa Iran takunkuman tattalin arziki daga 2010 saboda zargin cewa tana shrin hada nukiliya.

Sun hana Iran sayar da man fetur dinta a kasuwar duniya da kuma hana ta taba kudinta Dala biliyan 100 da ke kasashen waje. Tattalin arzikinta ya karye, kuma darajar kudinta ya yi ta karyewa, wanda ya jawo hauhawar farashi.

A 2015, Iran da manyan kasashen duniya shida – Amurka, Faransa, Rasha, Jamus, Birtaniya – suka kulla yarjejeniyar JCPOA.

Kasashen sun amince su dage wa Iran takunkumai bisa sharuddan yarjejeniyar.

An tsara yarjejeniyar za ta yi aiki tsawon shekara 15.

Lokacin da Donald Trump ya kama mulki ya fitar da Amurka daga yarjejeniyar a 2018, wadda babbar dirka ce a cikinta.

Ya ce yarjejeniyar ba ta da kyau saboda ba mai dorewa ba ce kuma ba ta yi magana kan shirin Iran na makamai masu linzami ba. Ya kara wa Iran takunkumai saboda ta dawo kan teburin tattaunawa.

Isra’ila ta yi ikirarin cewa Iran ta ci gaba da neman hada nukiliya a boye kuma za ta yi amfani da kudin da ta samu bayan cire tukunkumi wajen karfafa rundunar sojinta.

 

Me Amurka da Isra’ila ke so yanzu?

Da alama sanarwar da Trump ya bayar ta neman fara tattaunawa da Iran ta bai wa Isra’ila mamaki. Ya dade yana cewa zai iya kulla yarjejeniya mafi kyawu sama da JCPOA, amma har yanzu Iran ta yi watsi da bukatar.

Trump ya yi gargadi cewa idan Iran ba ta yarda da sabuwar yarjejeniya ba “zai kai musu hari”.

Mai bai shi shawara kan harkokin tsaro Mike Waltz ya ce Trump na son Iran ta “lalata baki dayan” shirin nukilyar tata, yana cewa: “Kamar ingantawa, ko hada makami, wato shirinta na makamai masu linzami.”

Duk da cewa Trump ya ce tattaunawar ta gaba da gaba ce, ministan harkokin Iran Abbas Araghchi ya ce tattaunawar da za a yi a Oman ba ta gaba da gaba ba ce. Ya ce a shirye suke su tattauna amma dole sai Trump ya amince cewa “babu maganar hari”.

Bayan sanarwar da Trump ya yi, Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce yarjejeniya daya da za su amince da ita ita ce wadda Iran za ta yarda da hakura da shirin nukiliya gaba daya.

Ya ce hakan na nufin: “Mu shiga mu tarwatsa masana’antun, mu lalata komai bisa sa ido da jagorancin Amurka.”

Abin da Isra’ila ke fargaba shi ne Trump zai iya yarda da wani abu kasa da lalata shirin na Iran gaba daya da zai yi kurin cim mawa a matsayin nasarar difilomasiyya.

Isra’ila da ba ta shiga yarjejeniyar NPT ba, ana ganin tana da makaman nukiliya, abin da ba ta taba amsawa ko karyatawa ba.

Isra’ila na ganin idan Iran ta samu nukiliya barazana ce a gare ta saboda har yanzu ba ta amince da ‘yancin Isra’ilar ba a matsayin kasa.

Nukiliya
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Nukiliya
Kasashen Ketare

Nijar Da Canada Sun Ƙulla Yarjejeniyar Gina Sabuwar Matatar Mai A Jihar Dosso

August 23, 2026
Nukiliya
Kasashen Ketare

Kotun ICC Ta Yi Watsi Da Sabbin Takunkuman Amurka Kan Jami’anta

August 23, 2026
Nukiliya
Kasashen Ketare

Rasha Da Ukraine Sun Zafafa Hare-hare Kan Juna Bayan Yaƙinsu Ya Ɗauki Sabon Salo

August 22, 2026
Next Post
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.