• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Dama Ce Ga Kasashen Afirka

by Bello Wang
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Dama Ce Ga Kasashen Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau Talata, firaministan kasar Sin Li Qiang ya gabatar da rahoton ayyukan gwamnati a taron shekara-shekara na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin, wanda ya nuna cewa, da ma a farkon bara, kasar Sin ta sanya burin samun karuwar ma’aunin tattalin arizki na GDP ta kashi 5%, da samar da karin guraben aikin yi kimanin miliyan 12, sa’an nan an ga yadda kasar ta cika burinta, inda a karshen bara, karuwar GDPn ta ta kai kashi 5.2%, gami da samar da sabbin guraben aikin yi miliyan 12 da dubu 440.

Alkaluma na sauran fannoni su ma sun shaida cewa, tattalin arzikin kasar na ta karuwa cikin wani yanayi na daidaituwa, kana kasar ta cimma dukkan burikan da ta sanya gaba a bara. Wannan albishiri ne ga mutanen kasar Sin, kana labari mai kyau ne ga jama’ar kasashen Afirka.

Ko me ya sa na fadi haka? Saboda da farko, a matsayinta na kasa mafi karfin tattalin arizki ta biyu a duniya, yadda kasar Sin ke iya kiyaye karuwar tattalin arizkinta yadda take bukata, da tabbatar da dorewar manufofinta na raya kasa, wani abu ne mai kyau, wanda ke haifar da yanayi na tabbas ga tattalin arzikin duniya, da karfafa gwiwar dimbin abokan hulda na kasar Sin, musamman ma kasashe masu tasowa.

Ba kamar wata babbar kasa ba, wadda ta dinga kara ruwan da ake karba kan kudin rance a bankuna, lamarin da ya haddasa hauhawar farashin kayayyaki mai tsanani a kasashen Afirka. Misali, a kasar Najeriya, tun daga watan Janairun shekarar 2022, darajar Naira kan dalar Amurka ta ragu da kashi 74%. Sakamakon haka, iyalin da ke iya kai yara zuwa jami’a wasu shekaru 2 da suka wuce, yanzu sai ya ga yana fama da yunwa. Abin takaici ne ganin yadda babbar kasar ta ki sauke nauyin dake rataya a wuyanta.

  • Sin: Kalaman Da Amurka Ta Yi Wata Alama Ce Ta Siyasantar Da Harkokin Tattalin Arziki Da Cinikayya

Sa’an nan, dalili na biyu, shi ne ci gaban kasar Sin ya kan haifar da ci gaba a kasashen Afirka.

Labarai Masu Nasaba

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

Kasar Sin kawar kasashen Afirka ce wadda ta fi yin ciniki da su. Kana ta kiyaye wannan matsayi cikin shekaru 15 da suka wuce. Ban da haka, kasar Sin tana kan gaba a cikin kasashe masu tasowa, ta fuskar yawan jarin da ake zubawa kasashen Afirka. Ma iya cewa, alakar hadin kai mai karfi ta riga ta hada makomar kasar Sin da kasashen Afirka waje guda.

Bari in dauki manufar raya tattalin arziki ba tare da gurbata muhalli ba a matsayin misali. Wannan manufa tana cikin manyan tsare-tsaren raya kasa na kasar Sin. Kana rahoton ayyukan gwamnatin kasar ya nuna cewa, karfin kasar na samar da wutar lantarki ta makamashin da ake iya sabuntawa ya wuce karfinta na samar da wuta ta makamashin gargajiya a karon farko a shekarar 2023, inda yawan sabbin tashoshin samar da wutar lantarki da makamashi masu tsabta da ta kafa cikin shekarar ya kai fiye da rabin adadin sabbin tashoshin na duk duniya.

Ko da yake kasar Sin ta samu ci gaba a wannan fanni, amma ko za ta manta da taimakon kasashen Afirka?

Ba zai yiwu ba. Kasar Sin ta farko ce daga cikin manyan kasashen da suka kulla yarjejeniyar hadin kai ta fuskar tinkarar sauyin yanayi tare da nahiyar Afirka, wanda ya aiwatar da daruruwan ayyukan samar da wutar lantarki da makamashi mai tsabta da tsare-tsaren jigilar wutar lantarki a kasashen Afirka, irinsu tashar samar da wutar lantarki ta karfin ruwa ta Zungeru dake Najeriya, da tashar samar da wutar lantarki ta karfin iska ta De Aar dake kasar Afirka ta Kudu, da tashar samar da wuta ta zafin rana ta Garissa dake Kenya, da dai makamantansu.

Zan ba da wani misali na daban. Cikin rahoton ayyukan gwamnati da kasar Sin ta gabatar a wannan karo, an ambaci manufar kasar ta raya tattalin arziki mai alaka da fasahar sadarwa ta zamani. To, a wannan fanni ma, ci gaban kasar Sin shi ma ya haifar da ci gaba na bai daya a nahiyar Afirka.

Stephanie Arnold, masaniya ce dake aiki a jami’ar Bologna ta kasar Italiya. Ta rubuta wani bayani a kwanan nan, inda ta ce tun daga shekarar 2010 har zuwa ta 2023, yawan mutanen kasashen Afirka masu yin amfani da hidimar fasahar sadarwa ta 3G ya karu daga kashi 22% zuwa kashi 83%, kana masu yin amfani da Mobile Broadband wato wayoyin sadarwa na tafi-da-gidanka sun karu daga kasa da kashi 2% zuwa kashi 48%. A cewarsa, “kasashen Afirka sun samu ci gaba sosai, kana kasar Sin ta taka muhimmiyar rawa a ciki.” Saboda a kalla kasashe 38 dake nahiyar Afirka sun zabi kamfanonin kasar Sin a matsayin abokan hadin gwiwa, a kokarinsu na gina wayoyin aika sako ta haske, da cibiyoyin sadarwa, da sauran kayayyakin more rayuwa, gami da horar da ma’aikata masu fasaha.

Ta hakan muna iya ganin yadda ci gaban tattalin arzikin kasar Sin a sa’i daya ya zama dama ga kasashen Afirka na raya tattalin arizkin kansu.

Masu iya magana su kan ce, “ Tafiya mutum daya kadai na da sauri, amma tafiya tare da abokai za ta kai wuri mai nisa”. Ina sa ran ganin abokai na kasashen Afirka da kasar Sin, da suke tafiya tare kan turbar samun ci gaba, su isa wurin da suka dosa, komai nisansa. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfirkaLantarkiNomaRahotoShekaraSinTattalin Arziki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Daga Bisani Dai Ta Tabbata Dubai Ta Ɗage Haramcin Biza Ga ‘Yan Nijeriya

Next Post

Xi Jinping Ya Halarci Taron Tattaunawa A Yayin Taron Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin

Related

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka
Ra'ayi Riga

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

13 hours ago
Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci
Ra'ayi Riga

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

4 days ago
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

6 days ago
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

6 days ago
Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba
Ra'ayi Riga

Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba

1 week ago
Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
Ra'ayi Riga

Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya

2 weeks ago
Next Post
Xi Jinping Ya Halarci Taron Tattaunawa A Yayin Taron Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin

Xi Jinping Ya Halarci Taron Tattaunawa A Yayin Taron Majalisar Wakilan Jama'ar Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.