• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Dama Ce Ga Kasashen Afirka

by Bello Wang
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Dama Ce Ga Kasashen Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau Talata, firaministan kasar Sin Li Qiang ya gabatar da rahoton ayyukan gwamnati a taron shekara-shekara na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin, wanda ya nuna cewa, da ma a farkon bara, kasar Sin ta sanya burin samun karuwar ma’aunin tattalin arizki na GDP ta kashi 5%, da samar da karin guraben aikin yi kimanin miliyan 12, sa’an nan an ga yadda kasar ta cika burinta, inda a karshen bara, karuwar GDPn ta ta kai kashi 5.2%, gami da samar da sabbin guraben aikin yi miliyan 12 da dubu 440.

Alkaluma na sauran fannoni su ma sun shaida cewa, tattalin arzikin kasar na ta karuwa cikin wani yanayi na daidaituwa, kana kasar ta cimma dukkan burikan da ta sanya gaba a bara. Wannan albishiri ne ga mutanen kasar Sin, kana labari mai kyau ne ga jama’ar kasashen Afirka.

Ko me ya sa na fadi haka? Saboda da farko, a matsayinta na kasa mafi karfin tattalin arizki ta biyu a duniya, yadda kasar Sin ke iya kiyaye karuwar tattalin arizkinta yadda take bukata, da tabbatar da dorewar manufofinta na raya kasa, wani abu ne mai kyau, wanda ke haifar da yanayi na tabbas ga tattalin arzikin duniya, da karfafa gwiwar dimbin abokan hulda na kasar Sin, musamman ma kasashe masu tasowa.

Ba kamar wata babbar kasa ba, wadda ta dinga kara ruwan da ake karba kan kudin rance a bankuna, lamarin da ya haddasa hauhawar farashin kayayyaki mai tsanani a kasashen Afirka. Misali, a kasar Najeriya, tun daga watan Janairun shekarar 2022, darajar Naira kan dalar Amurka ta ragu da kashi 74%. Sakamakon haka, iyalin da ke iya kai yara zuwa jami’a wasu shekaru 2 da suka wuce, yanzu sai ya ga yana fama da yunwa. Abin takaici ne ganin yadda babbar kasar ta ki sauke nauyin dake rataya a wuyanta.

  • Sin: Kalaman Da Amurka Ta Yi Wata Alama Ce Ta Siyasantar Da Harkokin Tattalin Arziki Da Cinikayya

Sa’an nan, dalili na biyu, shi ne ci gaban kasar Sin ya kan haifar da ci gaba a kasashen Afirka.

Labarai Masu Nasaba

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Kasar Sin kawar kasashen Afirka ce wadda ta fi yin ciniki da su. Kana ta kiyaye wannan matsayi cikin shekaru 15 da suka wuce. Ban da haka, kasar Sin tana kan gaba a cikin kasashe masu tasowa, ta fuskar yawan jarin da ake zubawa kasashen Afirka. Ma iya cewa, alakar hadin kai mai karfi ta riga ta hada makomar kasar Sin da kasashen Afirka waje guda.

Bari in dauki manufar raya tattalin arziki ba tare da gurbata muhalli ba a matsayin misali. Wannan manufa tana cikin manyan tsare-tsaren raya kasa na kasar Sin. Kana rahoton ayyukan gwamnatin kasar ya nuna cewa, karfin kasar na samar da wutar lantarki ta makamashin da ake iya sabuntawa ya wuce karfinta na samar da wuta ta makamashin gargajiya a karon farko a shekarar 2023, inda yawan sabbin tashoshin samar da wutar lantarki da makamashi masu tsabta da ta kafa cikin shekarar ya kai fiye da rabin adadin sabbin tashoshin na duk duniya.

Ko da yake kasar Sin ta samu ci gaba a wannan fanni, amma ko za ta manta da taimakon kasashen Afirka?

Ba zai yiwu ba. Kasar Sin ta farko ce daga cikin manyan kasashen da suka kulla yarjejeniyar hadin kai ta fuskar tinkarar sauyin yanayi tare da nahiyar Afirka, wanda ya aiwatar da daruruwan ayyukan samar da wutar lantarki da makamashi mai tsabta da tsare-tsaren jigilar wutar lantarki a kasashen Afirka, irinsu tashar samar da wutar lantarki ta karfin ruwa ta Zungeru dake Najeriya, da tashar samar da wutar lantarki ta karfin iska ta De Aar dake kasar Afirka ta Kudu, da tashar samar da wuta ta zafin rana ta Garissa dake Kenya, da dai makamantansu.

Zan ba da wani misali na daban. Cikin rahoton ayyukan gwamnati da kasar Sin ta gabatar a wannan karo, an ambaci manufar kasar ta raya tattalin arziki mai alaka da fasahar sadarwa ta zamani. To, a wannan fanni ma, ci gaban kasar Sin shi ma ya haifar da ci gaba na bai daya a nahiyar Afirka.

Stephanie Arnold, masaniya ce dake aiki a jami’ar Bologna ta kasar Italiya. Ta rubuta wani bayani a kwanan nan, inda ta ce tun daga shekarar 2010 har zuwa ta 2023, yawan mutanen kasashen Afirka masu yin amfani da hidimar fasahar sadarwa ta 3G ya karu daga kashi 22% zuwa kashi 83%, kana masu yin amfani da Mobile Broadband wato wayoyin sadarwa na tafi-da-gidanka sun karu daga kasa da kashi 2% zuwa kashi 48%. A cewarsa, “kasashen Afirka sun samu ci gaba sosai, kana kasar Sin ta taka muhimmiyar rawa a ciki.” Saboda a kalla kasashe 38 dake nahiyar Afirka sun zabi kamfanonin kasar Sin a matsayin abokan hadin gwiwa, a kokarinsu na gina wayoyin aika sako ta haske, da cibiyoyin sadarwa, da sauran kayayyakin more rayuwa, gami da horar da ma’aikata masu fasaha.

Ta hakan muna iya ganin yadda ci gaban tattalin arzikin kasar Sin a sa’i daya ya zama dama ga kasashen Afirka na raya tattalin arizkin kansu.

Masu iya magana su kan ce, “ Tafiya mutum daya kadai na da sauri, amma tafiya tare da abokai za ta kai wuri mai nisa”. Ina sa ran ganin abokai na kasashen Afirka da kasar Sin, da suke tafiya tare kan turbar samun ci gaba, su isa wurin da suka dosa, komai nisansa. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfirkaLantarkiNomaRahotoShekaraSinTattalin Arziki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Daga Bisani Dai Ta Tabbata Dubai Ta Ɗage Haramcin Biza Ga ‘Yan Nijeriya

Next Post

Xi Jinping Ya Halarci Taron Tattaunawa A Yayin Taron Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin

Related

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

1 day ago
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
Ra'ayi Riga

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

3 days ago
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Ra'ayi Riga

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

1 week ago
Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
Ra'ayi Riga

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

1 week ago
Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
Ra'ayi Riga

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

1 week ago
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

2 weeks ago
Next Post
Xi Jinping Ya Halarci Taron Tattaunawa A Yayin Taron Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin

Xi Jinping Ya Halarci Taron Tattaunawa A Yayin Taron Majalisar Wakilan Jama'ar Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

June 27, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2

June 27, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador

Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador

June 27, 2025
Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

June 27, 2025
WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

June 27, 2025
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

June 27, 2025
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

June 27, 2025
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

June 27, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

June 27, 2025
Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.