• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cire Tallafin Fetur: Ma’aikata Mazauna Abuja Sun Koka Kan Tsadar Rayuwa Da Wutar Lantarki

by Muhammad
2 years ago
in Labarai
0
Farashin Ɗanyen Man Fetur Ya Yi Tashin Da Ba A Taɓa Irinsa Ba Cikin Watanni 10
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da cire tallafin man fetur ke ci gaba da kawo cikas ga rayuwar ‘yan Nijeriya, mazauna babban birnin tarayya Abuja sun ce akwai bukatar gwamnati ta kara duba yanayin da suke ciki.

Mazauna garin sun bayyana haka ne a wata hira da suka yi da kafofin yada labaran Nijeriya a Abuja ranar Lahadi.

  • Cire Tallafin Fetur: Gwamna Makinde Ya Yi Wa Ma’aikata Karin Naira N25,000 Kan Albashinsu. 
  • Radadin Cire Tallafin Man Fetur: Kwan-gaba Kwan-baya Tsakanin Gwamnati Da Kungiyar Kwadago

Wasu mazauna yankin sun ce galibin kudaden shigar da suke samu ana kashe su ne wajen siyan mai, wanda hakan ya sa su ke rike ragowar ‘yan kudade kadan don biyan wasu bukatu.

LEADERSHIP HAUSA ta rawaito cewa, Shugaban Nijeriya, Bola Tinubu, ya sanar da cire tallafin man fetur a ranar 29 ga watan Mayu yayin da yake gabatar da jawabinsa a taron rantsar da shi a matsayin sabon shugaban kasa.

Bayan da shugaban ya bayyana haka, farashin man fetur ya tashi daga N195 a kowace lita, kuma a halin yanzu ana sayar da shi tsakanin N637 zuwa N660.

Labarai Masu Nasaba

Ƴan Arewa Za Su Yi Murna Idan Na Zama Shugaban Ƙasa — Peter Obi

AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate

Ganin farashin man fetur din na kwanan nan na Oktoba 2023 da Hukumar Kididdiga ta Kasa (NBS) ta fitar ta ce matsakaicin farashin litar man fetur ya karu daga N195.29 a watan Oktoban 2022 zuwa N630.63 a watan Oktoban 2023.

NBS ta ce, farashin N630.63 na watan Oktoba na shekarar 2023 ya nuna karin kashi 222.92 cikin dari na N195.29 a watan Oktobar 2022.

Karin farashin man fetur din ya haifar da tashin gwauron zabin kayayyakin abinci da sufuri da sauran kayayyaki fadin kasar.

Joanna Madu, wata ma’aikaciyar gwamnati ce da ta ce, cire tallafin na cinye mafi yawan albashin da take karba wanda ya gaza biya mata bukatunta da dama, inda ta bayyana lamarin a matsayin mai tsanani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbujaCire Tallafin feturTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Barawo Ne, Sun Kwato Dabbobi 90 A Kaduna

Next Post

Muna Roƙon Tinubu Da Ya Sake Naɗa Ministan Da Zai Maye Gurbin Lalong Daga Filato Ta Tsakiya – Komsol

Related

Ƴan Arewa Za Su Yi Murna Idan Na Zama Shugaban Ƙasa — Peter Obi
Labarai

Ƴan Arewa Za Su Yi Murna Idan Na Zama Shugaban Ƙasa — Peter Obi

1 hour ago
AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate
Ilimi

AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate

2 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
Da ɗumi-ɗuminsa

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

14 hours ago
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a
Labarai

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

15 hours ago
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson
Labarai

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

16 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

19 hours ago
Next Post
Muna Roƙon Tinubu Da Ya Sake Naɗa Ministan Da Zai Maye Gurbin Lalong Daga Filato Ta Tsakiya – Komsol

Muna Roƙon Tinubu Da Ya Sake Naɗa Ministan Da Zai Maye Gurbin Lalong Daga Filato Ta Tsakiya - Komsol

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Arewa Za Su Yi Murna Idan Na Zama Shugaban Ƙasa — Peter Obi

Ƴan Arewa Za Su Yi Murna Idan Na Zama Shugaban Ƙasa — Peter Obi

July 7, 2025
AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate

AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate

July 7, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.