• English
  • Business News
Tuesday, October 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CITAD Ta Bai Wa ‘Yan Jarida 10 Tallafi Don Gudanar Da Bincike Game Da Cin Hanci

bySadiq
3 years ago
inLabarai
0
CITAD Ta Bai Wa ‘Yan Jarida 10 Tallafi Don Gudanar Da Bincike Game Da Cin Hanci

Akalla ‘yan jarida 10 ne suka samu tallafin kudi don gudanar da bincike kan cin hanci da rashawa a tsakanin al’umma.

Cibiyar Fasaha da Ci Gaban Al’umma (CITAD) ce ta ba da tallafin tare da hadin gwiwar gidauniyar MacArthur.

  • Miyetti Allah Ta Maka Gwamna Ortom A Kotu Kan Kwace Wuraren Yin Kiwo A Jihar Benuwai
  • Daga Soyayyar Wata Yarinya Na Fara Waka —Abba Ganga

Babban Daraktan Cibiyar, Malam Yunusa Ya’u, wanda Buhari Abba ya wakilta, ya bayyana cewa tun farkon watan Yuni, CITAD ta bukaci ‘yan jarida da suka halarci taron bita na kwana biyu a jihar Bauchi, kan karamin tallafin bincike na yaki da cin hanci da rashawa.

Akalla mutane 15 ne suka shiga takarar neman tallafin.

Bayan da alkalai da masu ruwa da tsaki suka tantance, sun zabo ‘yan jarida 10 don ba su tallafin da za su yi amfani da shi wajen gudanar da bincike.

Labarai Masu Nasaba

Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga

Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

Babban Darakta na CITAD, Injiniya Y. Z. Ya’u, ya ce, tallafin wani hadin guiwa ne Gidauniyar Macarthur don bai wa ’yan jarida kwarin guiwa wajen yin bincike da kuma bayar da rahoton ayyukan cin hanci da rashawa a cikin al’umma ta hanyar jan hankalin gwamnati da masu ruwa da tsaki don yin gyara.

“CITAD ta dade tana aiki tare da ‘yan jarida don tabbatar da gaskiya da rikon amana a tsakanin jama’a kuma wannan tallafin zai zama na musamman duba da yanayin wadanda zasu yi binciken matasa ne masu sha’awar kawo canji a cikin al’umma.”

“Binciken ayyukan cin hanci da rashawa a cikin cibiyoyin gwamnati da masu zaman kansu zai inganta rayuwar jama’a musamman a cikin al’ummomin da ba su da murya don yaki da cin hancin.”

Wadanda suka yi nasara sun fito ne daga kafofin yada labarai daban-daban wadanda suka hada da:

1 – Auta Polycarp – Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN).

2 – Ismail Auwal Garba – Sahelian Times.

3 – Edwin Philip – Breeze FM Lafia, Nasarawa.

4 – Anibe Idajili – TheCable.

5 – Hauwa Kabir Lawal – Daily Reality Newspaper, Jihar Filato.

6 – Abbakar Muhammad Usman – Daily Trust.

7 – Rabiu Musa – Hot Pen, Kano.

8 – Abdulhafiz Sultan – Jasawa Times, Jihar Filato.

9 – Muhammad Auwal Ibrahim – Wikki Times, Jihar Gombe.

10 – Zaharaddeen S. Yakubu – Daily Trust, Jihar Kano.

Tags: 'Yan JaridaBincikeBuhari AbbaCibiyaCin Hanci Da RashawaHadin GuiwaMacArthurTalladiYZ Ya'u
ShareTweetSendShare
Sadiq

Sadiq

Related

Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga
Labarai

Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga

2 hours ago
Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

3 hours ago
Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa
Manyan Labarai

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

4 hours ago
Next Post
Sin: Cinikin Kayayyakin Abinci Zai Kara Amfanawa Jama’ar Sin Da Afirka

Sin: Cinikin Kayayyakin Abinci Zai Kara Amfanawa Jama'ar Sin Da Afirka

LABARAI MASU NASABA

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

October 7, 2025
Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga

Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga

October 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

October 7, 2025
Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

October 7, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Rage Kuɗin Aikin Hajjin 2026

October 7, 2025
Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

October 6, 2025
Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

October 6, 2025
Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

October 6, 2025
Karamin Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Legas Ya Yi Bikin Bunkasa Al’adu Na Bikin Tsakiyar Kaka

Karamin Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Legas Ya Yi Bikin Bunkasa Al’adu Na Bikin Tsakiyar Kaka

October 6, 2025
Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

October 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.