• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CITAD Ta Horas Da Yan Mata Kan Fasahar Zamani

by Leadership Hausa
1 year ago
in Ilimi
0
CITAD Ta Horas Da Yan Mata Kan Fasahar Zamani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Cibiyar Bunkasa Fasahar Sadarwa (CITAD), ta horas da yan mata ashirin da biyar da aka zakulo daga sassan Nijeriya kan yadda za su shiga a dama da su wajen fasahar sadarwar zamani da jagoranci.

Da take magana da yan jarida a yayin horon na kwanaki biyu da ya gudana a Bauchi makon jiya, jamiar kula da bangaren jinsi na CITAD, Zainab Aminu, ta ce, an zabo matan ne kuma an ba su horo na musamman a bangarorin shugabanci ta yadda za su shiga a dama da su a bangaren fasahar sadarwa tare da fuskantar kalubalen da mata ke fuskanta dangane da mu’amala da fasahar zamani.

  • CITAD Ta Bai Wa ‘Yan Jarida 10 Tallafi Don Gudanar Da Bincike Game Da Cin Hanci
  • Manyan Kalubalen Da Ke Durkusar Da Kiwon Kifi A Nijeriya

Ta ce, matan sun kuma samu horon yadda za su rungumi bangaren ICT domin shawo kan wariyar da ake yi wa mata a wannan fannin da kuma basu damar shiga a dama da su a bangaren fasahar sadarwa, hadi da tsare-tsaren da suka shafi kyautata harkokin jinsi.

Jamiar ta kara da cewa bangarorin da horon ya kuma maida hankali sun hada da tsare-tsaren fasahar sadarwa, matakan amfani da yanar gizo, hanyoyin da ake amfani da kafafen sadarwa ba tare da wani musgunawa ko cin zarafinsu ba, hadi da tsare-tsaren yadda za su samu damar kirkirar abubuwa tare da samar da damarmaki ga mata.

Zainab Aminu ta kara da cewa, lokaci ya yi da mata za su amfana da dukkanin damarmakin da ke cikin fasahar zamani ba tare da tsangwama ba.

Labarai Masu Nasaba

Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China

Makafi 37 Sun Zana Jarabawar JAMB A Bauchi

Wannan horaswar ta jagoranci na da manufar wayar da kan mata kan yadda za su samu damar shiga a dama da su kan tsare-tsare da yadda za su shiga a yi da su a bangaren ICT da kuma dabarun yadda za su samu ilimi kan sauye-sauye, ta shaida.

Ita ma da take magana, daraktan cibiyar kere-kere ta Bloom, Hannah Kabrang, ta ce, horaswar zai taimakesu wajen kara samun damarmakin yadda za su fuskanci tsare-tsaren fasahar sadarwa da kuma yadda za su taimaki mata su shiga a dama da su wajen amfanuwa da zamani.

Ita ma Sadiya Lawan, daliba a jamiar Dutsin-Ma, da ta kasance mahalarciyar taron, ta ce, sun samu gogewar yadda za su fuskanci kowani irin kalubalen da ke fuskantar mata a kafafen sadarwar zamani da kuma fasahar zamani gaba daya.

Tana mai cewa an kuma basu horon ta yadda su ma za su koyar da wasu yadda za su fuskanci wadannan matsalolin da mata ke fuskanta musamman a kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CitadFasahar Zamanikano
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hadarin Mota: NIS Ta Tabbatar Da Mutuwar Jamianta 4, 7 Sun Ji Rauni A Kano

Next Post

Amfanin Danyen Kwai Wajen Magance Kurajen Fuska

Related

Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
Ilimi

Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China

2 weeks ago
Makafi 37 Sun Zana Jarabawar JAMB A Bauchi
Ilimi

Makafi 37 Sun Zana Jarabawar JAMB A Bauchi

2 weeks ago
Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026
Ilimi

Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026

2 weeks ago
Nijeriya Ta Biya Bashin Ɗaliban Da Ke Karatu A Ƙasashen Waje
Ilimi

Nijeriya Ta Biya Bashin Ɗaliban Da Ke Karatu A Ƙasashen Waje

3 weeks ago
Dalilai 12 Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmanci Ga Al’umma (2)
Ilimi

Dalilai 12 Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmanci Ga Al’umma (2)

4 weeks ago
Fursunoni 62 Sun Rubuta Jarrabawar NECO da MBAIS A Kano
Labarai

Fursunoni 62 Sun Rubuta Jarrabawar NECO da MBAIS A Kano

4 weeks ago
Next Post
Amfanin Danyen Kwai Wajen Magance Kurajen Fuska

Amfanin Danyen Kwai Wajen Magance Kurajen Fuska

LABARAI MASU NASABA

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.