• English
  • Business News
Tuesday, October 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CMG Ya Gudanar Da Tattaunawa Kan “Zurfafa Gyare-Gyare A Sin Dama Ce Ga Duniya” A kasashen Najeriya Da Afirka Ta Kudu Da Zambiya

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
CMG

A ran 25 ga wata, an gudanar da tattaunawa kan “Zurfafa gyare-gyare a Sin dama ce ga duniya” a cibiyar al’adun kasar Sin dake birnin Abuja a Najeriya, wanda rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin CMG da cibiyar raya al’adu ta kasar Sin suka shirya. Taron ya jawo manyan baki da masana wadanda suka gabatar da fahimta mai zurfi game da gyare-gyaren da kasar Sin ke yi da kuma tasirinsu a duniya.

 

An bude taron ne da jawabin mataimakin ministan yada manufofin JKS, kuma shugaban CMG Mista Shen Haixiong, inda ya jaddada muhimmancin ci gaba da yin hadin gwiwa tare da nuna godiya ga mahalarta taron.

  • Masana Sun Bayyana Alfanun Manufar Gyare-gyaren Kasar Sin A Sabon Zamani A Abuja
  • Sin Ta Shawarci Kasashen Da Suka Mallaki Makaman Nukiliya Kada Su Yi Amfani Da Shi Wajen Kaiwa Juna Hari 

Muhimman jawabai sun hada da bayani mai zurfi kan tasirin kasar Sin ga tattalin arzikin duniya, da muhimmiyar gudummawar da take bayarwa ga yanayin tattalin arzikin Najeriya daga bakin malama Fa’iza Mustapha. Yayin da Misis Patricia Naria, wacce ta wakilci mai girma ministan ma’aikatar yawon bude ido ta tarayya Najeriya, ta mayar da hankali kan bunkasa harkokin yawon bude ido a Najeriya da karfafa gwiwar matasa domin dakile kaura daga karkara zuwa birane.

 

LABARAI MASU NASABA

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

Taron ya kasance dandalin tattaunawa da mu’amala mai karfi, inda ya bayyana irin gyare-gyaren da kasar Sin ke aiwatarwa, da tasirinsu a duniya, wanda ya nuna muhimmancin ci gaba da yin hadin gwiwa tsakanin Sin da Najeriya, wajen cimma muradun ci gaba na bai daya.

 

Bugu da kari, a ranar 24 ga watan Yuli agogon kasar Afirka ta Kudu, CMG ta gudanar da irin wannan taro a birnin Johannesburg, inda shugaban CMG Shen Haixiong ya gabatar da jawabi ta kafar bidiyo.

 

Shen Haixiong ya bayyana cewa, kwanan nan aka yi nasarar kammala cikakken zama karo na uku na kwamitin kolin JKS karo na 20 a birnin Beijing, wanda ya jawo hankalin duniya baki daya.

 

Wannan wani gagarumin ci gaba ne ga kasar Sin a sabon zamani. CMG ya himmatu wajen ba da labaran gyare-gyaren kasar Sin da bude kofa ga waje, da ba da labaran zamanantarwa irin ta kasar Sin, da yin aiki tukuru wajen gina gada ta cudanya da mu’amala, da tattaunawa, da fahimtar juna, da tuntubar juna tsakanin Sin da kasashen duniya.

 

Kazalika a wannan rana, CMG ya yi nasarar gudanar da taron tattaunawar a birnin Lusaka na kasar Zambiya. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025
Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta
Daga Birnin Sin

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

October 13, 2025
Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin
Daga Birnin Sin

Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

October 13, 2025
Next Post
Wasu Ɓata-gari Na Iya Amfani Da Zanga-zanga Domin Tada Zaune Tsaye – Minista

Wasu Ɓata-gari Na Iya Amfani Da Zanga-zanga Domin Tada Zaune Tsaye - Minista

LABARAI MASU NASABA

Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

October 14, 2025
Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

October 13, 2025
Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

October 13, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025
Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

October 13, 2025
NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

October 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet

October 13, 2025
Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

October 13, 2025
Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA

Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA

October 13, 2025
Barazanar Amurka Ta Kara Haraji Game Da Batun Ma’adanan Farin Karfe Ba Hanya Ce Mai Bullewa Ba

Barazanar Amurka Ta Kara Haraji Game Da Batun Ma’adanan Farin Karfe Ba Hanya Ce Mai Bullewa Ba

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.