• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CMG Ya Gudanar Da Tattaunawa Kan “Zurfafa Gyare-Gyare A Sin Dama Ce Ga Duniya” A kasashen Najeriya Da Afirka Ta Kudu Da Zambiya

by Sulaiman and CGTN Hausa
10 months ago
in Daga Birnin Sin
0
CMG Ya Gudanar Da Tattaunawa Kan “Zurfafa Gyare-Gyare A Sin Dama Ce Ga Duniya” A kasashen Najeriya Da Afirka Ta Kudu Da Zambiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ran 25 ga wata, an gudanar da tattaunawa kan “Zurfafa gyare-gyare a Sin dama ce ga duniya” a cibiyar al’adun kasar Sin dake birnin Abuja a Najeriya, wanda rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin CMG da cibiyar raya al’adu ta kasar Sin suka shirya. Taron ya jawo manyan baki da masana wadanda suka gabatar da fahimta mai zurfi game da gyare-gyaren da kasar Sin ke yi da kuma tasirinsu a duniya.

 

An bude taron ne da jawabin mataimakin ministan yada manufofin JKS, kuma shugaban CMG Mista Shen Haixiong, inda ya jaddada muhimmancin ci gaba da yin hadin gwiwa tare da nuna godiya ga mahalarta taron.

  • Masana Sun Bayyana Alfanun Manufar Gyare-gyaren Kasar Sin A Sabon Zamani A Abuja
  • Sin Ta Shawarci Kasashen Da Suka Mallaki Makaman Nukiliya Kada Su Yi Amfani Da Shi Wajen Kaiwa Juna Hari 

Muhimman jawabai sun hada da bayani mai zurfi kan tasirin kasar Sin ga tattalin arzikin duniya, da muhimmiyar gudummawar da take bayarwa ga yanayin tattalin arzikin Najeriya daga bakin malama Fa’iza Mustapha. Yayin da Misis Patricia Naria, wacce ta wakilci mai girma ministan ma’aikatar yawon bude ido ta tarayya Najeriya, ta mayar da hankali kan bunkasa harkokin yawon bude ido a Najeriya da karfafa gwiwar matasa domin dakile kaura daga karkara zuwa birane.

 

Labarai Masu Nasaba

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Taron ya kasance dandalin tattaunawa da mu’amala mai karfi, inda ya bayyana irin gyare-gyaren da kasar Sin ke aiwatarwa, da tasirinsu a duniya, wanda ya nuna muhimmancin ci gaba da yin hadin gwiwa tsakanin Sin da Najeriya, wajen cimma muradun ci gaba na bai daya.

 

Bugu da kari, a ranar 24 ga watan Yuli agogon kasar Afirka ta Kudu, CMG ta gudanar da irin wannan taro a birnin Johannesburg, inda shugaban CMG Shen Haixiong ya gabatar da jawabi ta kafar bidiyo.

 

Shen Haixiong ya bayyana cewa, kwanan nan aka yi nasarar kammala cikakken zama karo na uku na kwamitin kolin JKS karo na 20 a birnin Beijing, wanda ya jawo hankalin duniya baki daya.

 

Wannan wani gagarumin ci gaba ne ga kasar Sin a sabon zamani. CMG ya himmatu wajen ba da labaran gyare-gyaren kasar Sin da bude kofa ga waje, da ba da labaran zamanantarwa irin ta kasar Sin, da yin aiki tukuru wajen gina gada ta cudanya da mu’amala, da tattaunawa, da fahimtar juna, da tuntubar juna tsakanin Sin da kasashen duniya.

 

Kazalika a wannan rana, CMG ya yi nasarar gudanar da taron tattaunawar a birnin Lusaka na kasar Zambiya. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Masana Sun Bayyana Alfanun Manufar Gyare-gyaren Kasar Sin A Sabon Zamani A Abuja

Next Post

Wasu Ɓata-gari Na Iya Amfani Da Zanga-zanga Domin Tada Zaune Tsaye – Minista

Related

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu
Daga Birnin Sin

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

4 hours ago
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

6 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

6 hours ago
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare
Daga Birnin Sin

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

18 hours ago
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali
Daga Birnin Sin

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

19 hours ago
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani
Daga Birnin Sin

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

20 hours ago
Next Post
Wasu Ɓata-gari Na Iya Amfani Da Zanga-zanga Domin Tada Zaune Tsaye – Minista

Wasu Ɓata-gari Na Iya Amfani Da Zanga-zanga Domin Tada Zaune Tsaye - Minista

LABARAI MASU NASABA

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.