• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CMG Ya Kaddamar Da Aikin Kafofin Watsa Labarai Na Kare Muhalli Na Sin Da Afirka

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
CMG Ya Kaddamar Da Aikin Kafofin Watsa Labarai Na Kare Muhalli Na Sin Da Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin bikin “Ranar Muhalli ta Duniya” da aka yi a yau Lahadi, an kaddamar da “Aikin kafofin watsa labarai na kare muhalli na Sin da Afirka” a hukumance, wanda sashen babban gidan rediyo da talabijin na kasar Sin wato CMG dake nahiyar Afirka ya kaddamar a Nairobi, babban birnin kasar Kenya.

A yayin bikin kaddamar da aikin, CMG da muhimman kafofin watsa labaru na wasu kasashen Afirka da dama, sun gabatar da shawarar “Yin murya domin muhallin halittu” tare, inda aka yi kira ga kafofin watsa labaru na kasar Sin da na Afirka da su hada karfi don inganta mu’amala da koyi da juna a tsakanin jama’a kan ra’ayoyi da ayyukan kare muhalli.

Wakilai sama da 30 daga kungiyoyin kasa da kasa kamar UNEP, UNDP, UNICEF, da WWF, wakilan shugabannin siyasa daga kasashen Afirka, jami’an hukumomin kare muhalli, da wakilan manyan kafofin yada labarai daga kasashen Afirka da dama ne suka halarci bikin kaddamar da aikin.

Susan Gardner, darektar sashen kula da muhalli na UNEP, ta ce kafafen yada labarai na iya “jawo hankalin jama’a kan al’amurran muhalli da aka yi watsi da su, tare da gabatar da hujjoji ba tare da nuna banbanci ba ga jama’a”.

Shugaban kasar Seychelles, Wavel Ramkalawan, yayi imanin cewa, wajibi ne kafofin watsa labaru su fadakar da bil’adama su gane cewa, dukkanmu iyali guda ne, kuma makomar mu na zama irin ta bai daya ne. Kaddamar da wannan aikin, ya nuna muhimmancin hadin gwiwar kafofin watsa labaru na Sin da Afirka.

Labarai Masu Nasaba

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

Ministan yawon bude ido na kasar Kenya Najib Balala ya bayyana cewa, yin magana da murya guda karkashin hadin gwiwa tsakanin kafofin watsa labaru na kasar Sin da na Afirka zai iya yin tasiri wajen fadakar da mutane masu yawa da su rungumi ayyukan dake shafar kiyayewa da kuma gyara duniyarmu.

Jawo hankalin jama’a na da matukar muhimmanci ga shirin kare muhalli.
A nasa bangaren, Yakubu Mohamed, shugaban gidan talabijin na kasa a Najeriya, ya ce akwai fa’ida ta musamman da kafafen yada labarai ke da su wajen janyo hankalin jama’a don su maida hankali kan batutuwan da suka shafi kiyaye muhalli. (Mai fassara: Bilkisu Xin)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dan Takarar Sanatan Bauchi Ta Kudu A NNPP Ya Janye Wa Sanata Mai Ci, Lawan Gumau

Next Post

Saboda Alakata Da Gwamnatin Masari Ake Kokarin Ɓata Mun Suna – Mustapha Inuwa

Related

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara
Daga Birnin Sin

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

18 hours ago
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva
Daga Birnin Sin

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

19 hours ago
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu
Daga Birnin Sin

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

21 hours ago
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali
Daga Birnin Sin

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

23 hours ago
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

23 hours ago
Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo
Daga Birnin Sin

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

2 days ago
Next Post
Saboda Alakata Da Gwamnatin Masari Ake Kokarin Ɓata Mun Suna – Mustapha Inuwa

Saboda Alakata Da Gwamnatin Masari Ake Kokarin Ɓata Mun Suna - Mustapha Inuwa

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU

Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU

May 11, 2025
2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

May 11, 2025
Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

May 11, 2025
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

May 11, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

May 11, 2025
Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

May 11, 2025
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

May 11, 2025
Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

May 11, 2025
Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

May 11, 2025
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

May 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.