ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CMG Ya Kaddamar Da Aikin Kafofin Watsa Labarai Na Kare Muhalli Na Sin Da Afirka

by CMG Hausa
4 years ago
CMG

A yayin bikin “Ranar Muhalli ta Duniya” da aka yi a yau Lahadi, an kaddamar da “Aikin kafofin watsa labarai na kare muhalli na Sin da Afirka” a hukumance, wanda sashen babban gidan rediyo da talabijin na kasar Sin wato CMG dake nahiyar Afirka ya kaddamar a Nairobi, babban birnin kasar Kenya.

A yayin bikin kaddamar da aikin, CMG da muhimman kafofin watsa labaru na wasu kasashen Afirka da dama, sun gabatar da shawarar “Yin murya domin muhallin halittu” tare, inda aka yi kira ga kafofin watsa labaru na kasar Sin da na Afirka da su hada karfi don inganta mu’amala da koyi da juna a tsakanin jama’a kan ra’ayoyi da ayyukan kare muhalli.

Wakilai sama da 30 daga kungiyoyin kasa da kasa kamar UNEP, UNDP, UNICEF, da WWF, wakilan shugabannin siyasa daga kasashen Afirka, jami’an hukumomin kare muhalli, da wakilan manyan kafofin yada labarai daga kasashen Afirka da dama ne suka halarci bikin kaddamar da aikin.

ADVERTISEMENT

Susan Gardner, darektar sashen kula da muhalli na UNEP, ta ce kafafen yada labarai na iya “jawo hankalin jama’a kan al’amurran muhalli da aka yi watsi da su, tare da gabatar da hujjoji ba tare da nuna banbanci ba ga jama’a”.

Shugaban kasar Seychelles, Wavel Ramkalawan, yayi imanin cewa, wajibi ne kafofin watsa labaru su fadakar da bil’adama su gane cewa, dukkanmu iyali guda ne, kuma makomar mu na zama irin ta bai daya ne. Kaddamar da wannan aikin, ya nuna muhimmancin hadin gwiwar kafofin watsa labaru na Sin da Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Ministan yawon bude ido na kasar Kenya Najib Balala ya bayyana cewa, yin magana da murya guda karkashin hadin gwiwa tsakanin kafofin watsa labaru na kasar Sin da na Afirka zai iya yin tasiri wajen fadakar da mutane masu yawa da su rungumi ayyukan dake shafar kiyayewa da kuma gyara duniyarmu.

Jawo hankalin jama’a na da matukar muhimmanci ga shirin kare muhalli.
A nasa bangaren, Yakubu Mohamed, shugaban gidan talabijin na kasa a Najeriya, ya ce akwai fa’ida ta musamman da kafafen yada labarai ke da su wajen janyo hankalin jama’a don su maida hankali kan batutuwan da suka shafi kiyaye muhalli. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

CMG
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma
Daga Birnin Sin

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani
Daga Birnin Sin

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana
Daga Birnin Sin

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Next Post
Saboda Alakata Da Gwamnatin Masari Ake Kokarin Ɓata Mun Suna – Mustapha Inuwa

Saboda Alakata Da Gwamnatin Masari Ake Kokarin Ɓata Mun Suna - Mustapha Inuwa

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026
Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.