• English
  • Business News
Tuesday, June 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cutar Da Ke Kassara Gonakin Tumatir Ta Sake Bulla A Jihar Kano

by Abubakar Abba
2 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Cutar Da Ke Kassara Gonakin Tumatir Ta Sake Bulla A Jihar Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Manoman Tumatir a Jihar Kano, na ci gaba da fuskantar barkewar annobar cutar da ke lalata Tumatirin da suka shuka.

Cutar, wadda a turance ake kira da ‘Tuta Absoluta’, ta shafe shekaru tana lalata gonakin da aka shuka Tumatir.

  • Kwararru Sun Yi Musayar Ra’ayoyi Dangane Da Wayewar Kan Sin Da Afirka 
  • Kasar Sin Ta Mallaki Tasoshin Fasahar 5G Miliyan 4.4 A Halin Yanzu

Duk da kokarin da cibiyoyin bincike kan amfanin gona ke yi, wadanda suka hada da cibiyar binciken ‘ya’ayan itatuwa da ke garin Ibadan a Jihar Oyo, wannan cuta ta faskara samun magani.

Kazalika, duk binciken da kungiyoyin kasashen waje masu bayar da dauki na kawo karshen cutar, amma hakan ya gagari Kundila, duba da yadda cutar ta sake bulla a jihar.

Kungiyar manoman Tumatir ta kasa reshen Kano (TOGAN), karkashin jagorancin Alhaji Sani Danladi Yadakwari ta bayyana cewa, cutar ta kara barkewa a wasu gonakin manoman Tumatir a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

A cewarsa, hakan ya kuma jawo lalata gonakin na Tumatirin da ke wasu sassan jihar.

Yadakwari ya kara da cewa, hakan ya tilastawa manoman Tumatir da dama a jihar dakatar da nomansa, duba da irin mummunar asarar da suka yi.

Ya ci gaba da cewa, manoman Tumatir da suka fara lura da barkewar cutar ce suka sanar da kungiyar, inda kuma kungiyar ta shigo cikin lamarin ta kuma gano cewa, cutar ce ta sake dawowa gonakin manoman na Tumatir.

A cewarsa, maoman Tumatir a jihar, sun shafe shekaru suna yin asara sakamakon barkewar cutar, wanda hakan ya sanya wa manoman rashin sha’awar ci gaba da noman nasa.

“Mun gano bullar annobar ce a wasu gonakin da aka shuka Tumatir a

Garun Malam, Kura, Bunkure, Bagwai da sauransu”, in ji Yadakwari.

Ya sanar da cewa, duba da ilimin da muke da shi kan cutar, mun yi zargin cewa, annobar ce ta sake dawo ga gonakin na noman Tumatir da ke jihar.

“A bangaren kungiyar, mun dauki matakan da suka dace tare da rubuta wasika zuwa ga ma’aikatar aikin gona ta jihar, domin sanar da su dawowar annobar, inda a yanzu muke ci gaba da jiran amsa daga wurinsu”, a cewar Yadakwari.

Wannan cuta dai, an gano bullarta ne a shekarar 2016, wadda kuma ta jawo lalata gonakin manoma da dama da ke jihar.

Bugu da kari, bayan sake dawowar cutar, an fara fuskantar karancin Tumatir a akasarin kasuwannin da ke jhar, wanda kuma hakan ya haifar da tashin farashinsa zuwa sama da Naira 75.

Kazalika, manomansa da hukumomin gwamnati, sun tashi tsaye wajen yakar wannan cuta, amma sai dai, har yanzu kwalliya ba ta biya kudin sabulu ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CutakanoManomaTumatir
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwararru Sun Yi Musayar Ra’ayoyi Dangane Da Wayewar Kan Sin Da Afirka 

Next Post

Bankin Zenith Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3.97

Related

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

1 day ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

2 days ago
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
Noma Da Kiwo

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

2 days ago
Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
Noma Da Kiwo

Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 

4 days ago
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
Noma Da Kiwo

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

1 week ago
Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
Noma Da Kiwo

Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

1 week ago
Next Post
Bankin Zenith Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3.97

Bankin Zenith Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3.97

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi

Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi

June 23, 2025
EFCC Ta Kama Tsohon Babban Jami’in NNPC Kan Zargin Satar Dala Biliyan 7.2

EFCC Ta Kama Tsohon Babban Jami’in NNPC Kan Zargin Satar Dala Biliyan 7.2

June 23, 2025
Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana

Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana

June 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gargaɗin Amurka: Gwamnati Ta Bayar Da Tabbaci Akwai Tsaro A Abuja

June 23, 2025
Tawagar Likitocin Kasar Sin Sun Duba Marayu Marasa Lafiya Fiye Da 200 Kyauta A Zanzibar Ta Tanzaniya

Tawagar Likitocin Kasar Sin Sun Duba Marayu Marasa Lafiya Fiye Da 200 Kyauta A Zanzibar Ta Tanzaniya

June 23, 2025
An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

June 23, 2025
Za A Gudanar Da Taron Dandalin Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 16 a Birnin Tianjin Na Sin

Za A Gudanar Da Taron Dandalin Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 16 a Birnin Tianjin Na Sin

June 23, 2025
CMG Ya Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Kwamitin Shirya Gasar Wasannin Olympics Ta Milano Cortina Ta Shekarar 2026

CMG Ya Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Kwamitin Shirya Gasar Wasannin Olympics Ta Milano Cortina Ta Shekarar 2026

June 23, 2025
Karin Kudin Mai: Hakika An Ci Amanarmu, In Ji ‘Yan Kwadago

NNPC Ya Ƙara Kuɗin Fetur, Duba Sabon Farashin

June 23, 2025
Binciken CGTN: Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kasa Da Kasa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Amurka Kan Iran

Binciken CGTN: Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kasa Da Kasa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Amurka Kan Iran

June 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.