ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cutar Diphtheria Ta Kashe Yara 122 A Nijeriya -UNICEF

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Diphtheria

Asusun Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF), ya ce zuwa yanzu cutar mashako ta kashe rayukan yara kanana 122 a Nijeriya. 

A wata sanarwa da wakiliyar UNICEF a Nijeriya, Dokta Cristian Munduate, ta fitar a ranar Juma’a, ta ce cutar ta shafi jihohi 27 a Nijeriya.

  • Majalisa Ta Ki Amincewa Da Shirin Tinubu Na Daukar Matakin Soji A Kan Nijar
  • Manchester United Ta Dauki Hujland Daga Atalanta

Kana ta ce, zuwa watan Yulin 2023, an samu wadanda suka kamu da cutar 3,850 yayin da aka tabbatar da mutum 1,387 sun kamu da cutar.

ADVERTISEMENT

Sanarwar, ta ce cutar ta shafi jihohin Kano, Yobe, Katsina, Lagos, Birnin tarayya Abuja, Sakkwato da Zamfara, wanda cutar ta kama a tsakanin yara ‘yan shekara 2 zuwa 14.

A cewarta, abin damuwa ne matuka da aka gano kaso 22 cikin 100 na wadanda suka kamu da cutar ba su karbar rigakafin cututtuka da ake yi wa yara.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

“Mafi rinjaye na yaran da suka kamu da cutar, musamman wadanda suka mutu ba su taba karbar rigakafin kariya ko sau daya ba.”

Cristian, ta kara da cewa domin yaki da cutar, UNICEF ta na hadin guiwa da cibiyar binciken cututtuka ta Nijeriya (NCDC), jihohin da lamarin ya shafa, hukumar kula da kiwon lafiya a matakin farko ta kasa (NPHCDA), domin samar da tallafin kwararru da yadda za a dakile cutar.

Tallafin na UNICEF ya kunshi kudade, saukaka jigila wajen kai rigakafi, tuntubar masu ruwa da tsaki, kayan aiki da taimakawa a bangaren rigakafin a jihohin da lamarin ya shafa.

A cewarta sauran sun hada horas da ma’aiktan kiwon lafiya, masu bada gudunmawa, samar da takunkumin fuska, man tsaftace hannu da sauran kayan aiki.

UNICEF, ta shawarci iyaye da suke tabbatar da ‘ya’yansu suna amsar rigakafin cututtuka domin kare su daga cututtuka.

Ta kuma bukaci gwamnatoci da su tashi tsaye wajen kawo karshen cutar, inda ta ba da tabbacin ba su cikakken goyon baya domin kare yaran Nijeriya daga cutar.

Diphtheria
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Firaministan Georgia: Bikin Bude Gasar Wasannin Daliban Jami’o’in Duniya Ta Chengdu Na Da Kayatarwa

Firaministan Georgia: Bikin Bude Gasar Wasannin Daliban Jami’o’in Duniya Ta Chengdu Na Da Kayatarwa

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.