• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Ɗumi-Ɗumi: Jami’an Tsaro Sun Kama Manyan Shugabannin Ƙungiyar Ansaru 2

by Sadiq
2 months ago
Ansaru

Mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, ya sanar da cewa jami’an tsaro sun kama manyan shugabannin ƙungiyar ‘yan ta’adda ta Ansaru bayan watanni ana nemansu ruwa a jallo.

Waɗanda aka kama sun haɗa da Mahmud Muhammad Usman, wanda aka fi sani da Abu Baraa, wanda shi ne shugaban ƙungiyar, da kuma mataimakinsa Mahmud al-Nigeri, wanda aka fi sani da Mallam Mamuda.

  • Hadin Tuwon Dawa
  • APC Ta Nemi A Soke Zaɓen Cike Gurbi A Kano Saboda Rikici

Ribadu ya ce dukkanninsu sun shafe shekaru suna cikin jerin waɗanda ake nema bisa laifin kai wa  jami’an tsaro da mutane hare-hare da gine-ginen gwamnati.

A lokacin da yake jawabi a Abuja ranar Asabar, Ribadu ya bayyana wannan a matsayin babban ci gaba a yaƙi da ta’addanci a Nijeriya.

Ya ce Abu Baraa shi ne yake kiran kansa “Sarkin Ansaru” tare da sama maɓoyar ta’addanci a sassa daban-daban na ƙasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Ya kuma jagoranci sace mutane da fashi don tara kuɗaɗen da suke amfani da su wajen aikata ta’addanci.

Mataimakinsa Mamuda shi ne ke jagorantar rukunin “Mahmudawa” wanda ke aiki a kusa da Kainji National Park da ke tsakanin Jihar Neja da Kwara har zuwa Jamhuriyar Benin.

Ribadu ya ce Mamuda ya samu horo a Libya tsakanin shekarun 2013 da 2015, inda ya koyi amfani da makamai da kuma haɗa bama-bamai.

Ƙungiyar Ansaru ta fara ne a shekarar 2012 bayan ta ɓalle daga Boko Haram.

A farko ta yi ikirarin jihadi, amma daga baya ta fara kai wa jami’an tsaro, al’umma, da kuma gine-ginen gwamnati hare-hare.

Ƙungiyar kuma tana da alaƙa da Al-Qaeda a Arewacin Afirka.

A tsawon shekaru, ana danganta ƙungiyar da manyan laifuka da suka haɗa da balle gidan yarin Kuje a 2022, harin wajen haƙar uranium a Nijar, sace injiniyan Faransa Francis Collomp a 2013, sace Alhaji Musa Umar Uba na Daura a 2019, da kuma sace Sarkin Wawa.

Ribadu ya ce har yanzu suna da alaƙa da ƙungiyoyin ta’addanci a Mali, Nijar da Burkina Faso.

Ministan Watsa Labaru, Mohammed Idris, ya buƙaci ‘yan Nijeriya da su riƙa bai wa jami’an tsaro bayanai masu amfani don kawo ƙarshen ta’addanci.

Ya kuma roƙi kafafen yaɗa labarai kada su riƙa yaɗa manufar ‘yan ta’addan domin samun karɓuwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

October 23, 2025
Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 23, 2025
Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna

October 23, 2025
Next Post
Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta

Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta

LABARAI MASU NASABA

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

October 23, 2025
Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

October 23, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

October 23, 2025
Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

October 23, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kasar Sin Ta Karyata Rahoto Na Zuki-ta-malle Da Wata Cibiyar Binciken Amurka Ta Fitar Game Da Hadin Gwiwar Sin Da Yammacin Afirka

October 23, 2025
An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

October 23, 2025
Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.