• English
  • Business News
Thursday, September 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Ɗumi-Ɗumi: Jami’an Tsaro Sun Kama Manyan Shugabannin Ƙungiyar Ansaru 2

by Sadiq
4 weeks ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Da Ɗumi-Ɗumi: Jami’an Tsaro Sun Kama Manyan Shugabannin Ƙungiyar Ansaru 2
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, ya sanar da cewa jami’an tsaro sun kama manyan shugabannin ƙungiyar ‘yan ta’adda ta Ansaru bayan watanni ana nemansu ruwa a jallo.

Waɗanda aka kama sun haɗa da Mahmud Muhammad Usman, wanda aka fi sani da Abu Baraa, wanda shi ne shugaban ƙungiyar, da kuma mataimakinsa Mahmud al-Nigeri, wanda aka fi sani da Mallam Mamuda.

  • Hadin Tuwon Dawa
  • APC Ta Nemi A Soke Zaɓen Cike Gurbi A Kano Saboda Rikici

Ribadu ya ce dukkanninsu sun shafe shekaru suna cikin jerin waɗanda ake nema bisa laifin kai wa  jami’an tsaro da mutane hare-hare da gine-ginen gwamnati.

A lokacin da yake jawabi a Abuja ranar Asabar, Ribadu ya bayyana wannan a matsayin babban ci gaba a yaƙi da ta’addanci a Nijeriya.

Ya ce Abu Baraa shi ne yake kiran kansa “Sarkin Ansaru” tare da sama maɓoyar ta’addanci a sassa daban-daban na ƙasar nan.

Labarai Masu Nasaba

Ranar ‘Yancin Kai: Tinubu Zai Yi Wa ‘Yan Nijeriya Jawabi 1 Ga Oktoba

‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji 5 Wasu Mutum 10 A Zamfara

Ya kuma jagoranci sace mutane da fashi don tara kuɗaɗen da suke amfani da su wajen aikata ta’addanci.

Mataimakinsa Mamuda shi ne ke jagorantar rukunin “Mahmudawa” wanda ke aiki a kusa da Kainji National Park da ke tsakanin Jihar Neja da Kwara har zuwa Jamhuriyar Benin.

Ribadu ya ce Mamuda ya samu horo a Libya tsakanin shekarun 2013 da 2015, inda ya koyi amfani da makamai da kuma haɗa bama-bamai.

Ƙungiyar Ansaru ta fara ne a shekarar 2012 bayan ta ɓalle daga Boko Haram.

A farko ta yi ikirarin jihadi, amma daga baya ta fara kai wa jami’an tsaro, al’umma, da kuma gine-ginen gwamnati hare-hare.

Ƙungiyar kuma tana da alaƙa da Al-Qaeda a Arewacin Afirka.

A tsawon shekaru, ana danganta ƙungiyar da manyan laifuka da suka haɗa da balle gidan yarin Kuje a 2022, harin wajen haƙar uranium a Nijar, sace injiniyan Faransa Francis Collomp a 2013, sace Alhaji Musa Umar Uba na Daura a 2019, da kuma sace Sarkin Wawa.

Ribadu ya ce har yanzu suna da alaƙa da ƙungiyoyin ta’addanci a Mali, Nijar da Burkina Faso.

Ministan Watsa Labaru, Mohammed Idris, ya buƙaci ‘yan Nijeriya da su riƙa bai wa jami’an tsaro bayanai masu amfani don kawo ƙarshen ta’addanci.

Ya kuma roƙi kafafen yaɗa labarai kada su riƙa yaɗa manufar ‘yan ta’addan domin samun karɓuwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ta'addaAnsaruRibadu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Bukaci Japan Da Ta Yi Karatun Baya Game Da Batutuwan Tarihi Da Suka Shude Irinsu Batun Wurin Bauta Na Yasukuni

Next Post

Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta

Related

Akwai Bukatar Tinubu Ya Rubanya Kokarin Buhari Na Bunkasa Harkokin Noma  -Alhaji Umar
Manyan Labarai

Ranar ‘Yancin Kai: Tinubu Zai Yi Wa ‘Yan Nijeriya Jawabi 1 Ga Oktoba

7 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji 5 Wasu Mutum 10 A Zamfara

9 hours ago
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

11 hours ago
An Ɗauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya
Manyan Labarai

An Ɗauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya

12 hours ago
Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027
Manyan Labarai

Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

17 hours ago
majalisar kasa
Manyan Labarai

Majalisa Ta Bai Wa Minista Sa’o’i 48 Ya Bayyana A Gabanta Kan Hatsarin Jirgin Abuja Zuwa Kaduna

20 hours ago
Next Post
Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta

Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta

LABARAI MASU NASABA

Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

September 10, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS

Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS

September 10, 2025
Mataimakin Shugaban Unilever: Mun Kudiri Aniyar Zama “Masu Tseren Gudun Fanfalaki” A Kasar Sin

Mataimakin Shugaban Unilever: Mun Kudiri Aniyar Zama “Masu Tseren Gudun Fanfalaki” A Kasar Sin

September 10, 2025
Shettima Ya Yaba Wa Uba Sani Kan Kafa Majalisar Ƙwarewa Ta Jihar Kaduna

Shettima Ya Yaba Wa Uba Sani Kan Kafa Majalisar Ƙwarewa Ta Jihar Kaduna

September 10, 2025
Akwai Bukatar Tinubu Ya Rubanya Kokarin Buhari Na Bunkasa Harkokin Noma  -Alhaji Umar

Ranar ‘Yancin Kai: Tinubu Zai Yi Wa ‘Yan Nijeriya Jawabi 1 Ga Oktoba

September 10, 2025
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron CIFTIS Na Shekarar 2025

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron CIFTIS Na Shekarar 2025

September 10, 2025
“Hadin Kan Kasashen BRICS” Ya Karfafa Shawo Kan Kalubale

“Hadin Kan Kasashen BRICS” Ya Karfafa Shawo Kan Kalubale

September 10, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji 5 Wasu Mutum 10 A Zamfara

September 10, 2025
Jami’ar MAAUN Da Kwalejin Seneca ta Canada Sun Yi Haɗin Gwiwa Domin Samar Da Damarmaki Ga Ɗalibai A Duniya

Jami’ar MAAUN Da Kwalejin Seneca ta Canada Sun Yi Haɗin Gwiwa Domin Samar Da Damarmaki Ga Ɗalibai A Duniya

September 10, 2025
Jagororin Tsaro Da Na Sojoji Daga Sama Da Kasashe 100 Za Su Halarci Taro Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Beijing

Jagororin Tsaro Da Na Sojoji Daga Sama Da Kasashe 100 Za Su Halarci Taro Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Beijing

September 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.