• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Duminsa: Tinubu Ya Kori Hafsoshin Tsaron Nijeriya, Ya Nada Sabbi

Ya nada Ribadu a matsayin babban mai ba shi shawara kan sha'anin tsaro (NSA)

byMuhammad
2 years ago
Tinubu

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya amince da yi wa dukkan shugabannin hafsoshin tsaron Nijeriya da sufeto-Janar na ‘yan sanda da masu ba da shawara kan sha’anin tsaro da Kwanturola-Janar na Hukumar Kwastam murabus daga Ma’aikatunsu tare da maye gurbinsu nan take.

Hafsan hafsoshin sun hada da babban hafsan tsaro, Lucky Irabor da babban hafsan soji, Farouk Yahaya da Shugaban Hafsan Sojin Ruwa, Awwal Gambo sai shugaban hafsan sojin sama, Isiaka Amao da kuma Sufeto Janar na ‘Yansanda, Usman Alkali.

  • Kungiya Ta Yaba Wa Shugaba Tinubu Kan Inganta Tsaro Da Yaki Da Rashawa
  • Yanzu-yanzu: Tinubu Na Ganawa Ta Farko Da Shugabannin Tsaro

A cewar sanarwar da ta fito daga ofishin sakataren gwamnatin tarayya, sabbin jami’an da aka nada sune:
Mallam Nuhu Ribadu a matsayin babban mai ba da shawara kan sha’anin tsaron Nijeriya.

Sauran sun hada da “Maj. Janar C.G Musa Shugaban Hafsan Tsaro, Maj. T. A Lagbaja

“Shugaban hafson sojojin ruwa, Rear Admirral E. A Ogalla

LABARAI MASU NASABA

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

“AVM H.B Abubakar Shugaban Hafsan Sojan Sama sai DIG Kayode Egbetokun Mukaddashin Sufeto-Janar na ‘Yan Sanda.

“Maj. Janar EPA Undiandeye, matsayin shugaban hukumar leken asiri na kasa

Shugaban ya kuma amince da nadin:

“Col. Adebisi Onasanya, a matsayin kwamandan rundunar Soji.

“Lt. Col. Moshood Abiodun Yusuf, matsayin shugaban runduna ta 7, Asokoro, Abuja

“Lt. Col. Auwalu Baba Inuwa, matsayin shugaban runduna ta
177, Keffi, Nasarawa State

“Lt. Col. Mohammed J. Abdulkarim, matsayin shugaban runduna ta 102, Suleja, Niger

“Lt. Col. Olumide A. Akingbesote, matsayin shugaban runduna ta 176, Gwagwalada, Abuja

Kazalika, shugaban ya amince da nadin wasu hafsoshin soji a fadar shugaban kasa da suka hada da Maj. Isa Farouk Audu (N/14695) Babban Jami’i mai kula da Makamai na Gidan Gwamnati

“Capt. Kazeem Olalekan Sunmonu (N/16183) Babban Kwamandan Na Biyu

“Maj. Kamaru Koyejo Hamzat (N/14656) Babban Kwamandan Hukumar Leken Asiri ta Soja na fadar gwamnati

“Maj. TS Adeola (N/12860) Kwamanda, Makamai na Gidan Gwamnati

“Lt. A. Aminu (N/18578) Kwamandan Makamai na Gidan Gwamnati

Shugaban ya kuma amince da nadin wasu karin masu ba da shawara na musamman guda biyu (2), da manyan mataimaka biyu (2), wato:

“Hadiza Bala Usman mai ba da shawara ta musamman kan harkokin siyasa

“Hannatu Musa Musawa mai ba da shawara ta musamman kan tattalin arziki da al’adu

Sai Sanata Abdullahi Abubakar Gumel, matsayin mai ba da shawara kan sha’anin majalisar dokokin Nijeriya (Dattijai)

“Hon. (Barr) Olarewaju Kunle Ibrahim, matsayin babban mataimaki na musamman a majalisar wakilai ta Kasa (Majalisar Wakilai)

A karshe shugaban kasar ya amince da nadin Adeniyi Bashir Adewale a matsayin mai rikon mukamin Kwanturola Janar na Kwastam.

Sai dai shugabannin hukumar da aka nada da sufeto-janar na ‘yan sanda da kuma babban kwanturolan hukumar kwastam za su yi aiki a kan mukamansu, har sai an tabbatar da su kamar yadda kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya ya tanada.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025
Next Post
Wang Yi Da Qin Gang Sun Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Da Qin Gang Sun Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version