• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Yiwuwar Wasu Gwamnoni 5 Su Sauya Sheka Kafin Zaben 2027

by Yusuf Shuaibu
9 months ago
Zaben 2027

Yayin da zaben shekarar 2027 ke kara kunno kai, akwai zargi mai karfi na sauya sheka a tsakanin gwamnonin adawa guda 5 kafin zaben 2027, kamar yadda binciken LEADERSHIP ya tabbatar.

Binciken LEADERSHIP ya nuna cewa gwamnonin Abiya, Aled Otti, da na Inugu, Peter Mbah da na Delta, Sheriff Oborebwori da na Ribas, Siminalayi Fubara da na Akwa Ibom, Umoh Eno, sun tattaunawa kan shirinsu na yin watsi da jam’iyyunsu tare da sauya sheka zuwa APC mai mulki.

  • Bajintar Aiki: Majalisar Dattawa Ta Jinjina Wa Ministan Yaɗa Labarai
  • Hamas Ta Amince Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Da Isra’ila

Yayin da Mbah, Fubara, Eno, Oborebwori na cikin babbar jam’iyyar adawa ta PDP, Otti na jam’iyyar LP ne. Dukkanin jam’iyyun biyu a fama da rikice-rikicen cikin gida bayan kammala zaben 2023.

Wasu majiyoyi sun shaida wa LEADERSHIP cewa, wasu daga cikin gwamnonin ana masu matsinlamba don su koma jam’iyyar APC mai mulki, wasu kuma na ganin cewa, bisa la’akari da rashin zaman lafiya a cikin jam’iyyarsu, a shirye suke su shiga wani jam’iyya da zai kara musu damar samun wa’adi na biyu.

Tun bayan dawowar mulkin dimokuradiyya a Nijeriya a shekarar 1999, gwamnoni sama da 20 ne suka bar jam’iyyunsu na siyasa. Jihohin da suka fi yawan gwamnonin da suka sauya sheka sun hada da Sakkwato, Imo, Abiya da Adamawa.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

A Sakkwato, gwamnoni uku suka sauya sheka a jam’iyyunsu na asali, yayin da gwamnoni biyu masu ci a Imo da Abiya da Zamfara da Adamawa suka sauya sheka.

Sai dai kuma maganar ficewa daga jam’iyyar gwamnan Abiya ya kara ta’azzara ne yayin kaddamar da ginin filin jirgin saman Abiya, ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo ya bayyana cewa gwamnan Abiya zai koma APC.

Haka kuma, mataimakin shugaban majalisar wakilai, Benjamin Kalu, ya matsa wa Otti lamba ya koma APC.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa kawo yanzu ‘yan majalisar wakilai na jam’iyyar LP sama da 5 ne suka koma jam’iyyar APC.

A Jihar Ribas, Gwamna Fubara ya yi amfani da jam’iyyar APP wajen zaben kananan hukumomi, biyo bayan gazawar da ya yi wajen kwace tsarin PDP daga hannun Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya ci gaba da tattaunawa cewa zai iya ficewa daga PDP kafin zaben 2027.

Kusancin gwamnan Jihar Akwa Ibom, Eno da shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio, kasancewarsa daya daga cikin jiga-jigan jam’iyyar APC na kasa, ya iya yin tasiri wajen janwo ra’ayin gwamnan zuwa jam’iyya mai mulki.

A Inugu, rikicin cikin gida da ke kawo cikas a cikin jam’iyyar PDP a matakin kasa na iya sa gwamnan ya karkatar da hankalinsa zuwa wata jam’iyya.

Shugabannin jam’iyyar PDP na Jihar Delta, karkashin jagorancin kungiyar shugabannin PDP, sun tofa albarkacin bakinsu game da soyayyar Oborebwori da shugabannin APC. Shugabannin jam’iyyar, wato Mista Theophilus Ekiyor, Mista Ochuko Oghenekome, da Mista Ezekiel Chukwudi, a wata budaddiyar wasika, sun zargi gwamnan da yin alaka a sirrance da shugaban ma’aikatan fadar gwamnati na Shugaban Kasa, Bola Tinubu, Hon. Femi Gbajabiamila da gwamnan Jihar Legas, Mista Babajide Sanwo-Olu, domin ya samu wa’adi na biyu a matsayin gwamnan Delta.

Shugabannin jam’iyyar PDP na Jihar Delta, sun tofa albarkacin bakinsu game da soyayyar Oborebwori da shugabannin APC. Shugabannin jam’iyyar, wato Mista Theophilus Ekiyor, Mista Ochuko Oghenekome, da Mista Ezekiel Chukwudi, a wata budaddiyar wasika, sun zargi gwamnan da yin akala a sirrance da shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Hon. Femi Gbajabiamila da gwamnan Jihar Legas, Mista Babajide Sanwo-Olu, domin ya samu na wa’adi na biyu a matsayin gwamnan Delta.

Idan za a iya tunawa dai, dan majalisar tarayya kuma diyar tsohon gwamnan Jihar Delta, James Ibori, Hon. Erhiatake Ibori-Suenu, ta fice daga PDP zuwa APC a bara. Ibori dai ya yi zamani da Tinubu a matsayin gwamna a 1999 kuma makusancinsa ne.

Sai dai gwamnonin sun musanta wannan jita-jita, inda suka yi magana ta bakin mukarrabansu cewa ba za su bar jam’iyyarsu zuwa jam’iyyar APC mai mulki ba.

Haka zalika jam’iyyunsu sun bayyana irin wadannan ikirari a matsayin yaudarar jam’iyya mai mulki, inda suke neman haifar da rudani a cikin jam’iyyunsu da kuma zargin gwamnonin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
Za A Kammala Aikin Titin Abuja-Kaduna-Kano Cikin Watanni 14 – Gwamnati

Za A Kammala Aikin Titin Abuja-Kaduna-Kano Cikin Watanni 14 – Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.