• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Yiwuwar Wasu Gwamnoni 5 Su Sauya Sheka Kafin Zaben 2027

by Yusuf Shuaibu
8 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Da Yiwuwar Wasu Gwamnoni 5 Su Sauya Sheka Kafin Zaben 2027
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da zaben shekarar 2027 ke kara kunno kai, akwai zargi mai karfi na sauya sheka a tsakanin gwamnonin adawa guda 5 kafin zaben 2027, kamar yadda binciken LEADERSHIP ya tabbatar.

Binciken LEADERSHIP ya nuna cewa gwamnonin Abiya, Aled Otti, da na Inugu, Peter Mbah da na Delta, Sheriff Oborebwori da na Ribas, Siminalayi Fubara da na Akwa Ibom, Umoh Eno, sun tattaunawa kan shirinsu na yin watsi da jam’iyyunsu tare da sauya sheka zuwa APC mai mulki.

  • Bajintar Aiki: Majalisar Dattawa Ta Jinjina Wa Ministan Yaɗa Labarai
  • Hamas Ta Amince Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Da Isra’ila

Yayin da Mbah, Fubara, Eno, Oborebwori na cikin babbar jam’iyyar adawa ta PDP, Otti na jam’iyyar LP ne. Dukkanin jam’iyyun biyu a fama da rikice-rikicen cikin gida bayan kammala zaben 2023.

Wasu majiyoyi sun shaida wa LEADERSHIP cewa, wasu daga cikin gwamnonin ana masu matsinlamba don su koma jam’iyyar APC mai mulki, wasu kuma na ganin cewa, bisa la’akari da rashin zaman lafiya a cikin jam’iyyarsu, a shirye suke su shiga wani jam’iyya da zai kara musu damar samun wa’adi na biyu.

Tun bayan dawowar mulkin dimokuradiyya a Nijeriya a shekarar 1999, gwamnoni sama da 20 ne suka bar jam’iyyunsu na siyasa. Jihohin da suka fi yawan gwamnonin da suka sauya sheka sun hada da Sakkwato, Imo, Abiya da Adamawa.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

A Sakkwato, gwamnoni uku suka sauya sheka a jam’iyyunsu na asali, yayin da gwamnoni biyu masu ci a Imo da Abiya da Zamfara da Adamawa suka sauya sheka.

Sai dai kuma maganar ficewa daga jam’iyyar gwamnan Abiya ya kara ta’azzara ne yayin kaddamar da ginin filin jirgin saman Abiya, ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo ya bayyana cewa gwamnan Abiya zai koma APC.

Haka kuma, mataimakin shugaban majalisar wakilai, Benjamin Kalu, ya matsa wa Otti lamba ya koma APC.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa kawo yanzu ‘yan majalisar wakilai na jam’iyyar LP sama da 5 ne suka koma jam’iyyar APC.

A Jihar Ribas, Gwamna Fubara ya yi amfani da jam’iyyar APP wajen zaben kananan hukumomi, biyo bayan gazawar da ya yi wajen kwace tsarin PDP daga hannun Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya ci gaba da tattaunawa cewa zai iya ficewa daga PDP kafin zaben 2027.

Kusancin gwamnan Jihar Akwa Ibom, Eno da shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio, kasancewarsa daya daga cikin jiga-jigan jam’iyyar APC na kasa, ya iya yin tasiri wajen janwo ra’ayin gwamnan zuwa jam’iyya mai mulki.

A Inugu, rikicin cikin gida da ke kawo cikas a cikin jam’iyyar PDP a matakin kasa na iya sa gwamnan ya karkatar da hankalinsa zuwa wata jam’iyya.

Shugabannin jam’iyyar PDP na Jihar Delta, karkashin jagorancin kungiyar shugabannin PDP, sun tofa albarkacin bakinsu game da soyayyar Oborebwori da shugabannin APC. Shugabannin jam’iyyar, wato Mista Theophilus Ekiyor, Mista Ochuko Oghenekome, da Mista Ezekiel Chukwudi, a wata budaddiyar wasika, sun zargi gwamnan da yin alaka a sirrance da shugaban ma’aikatan fadar gwamnati na Shugaban Kasa, Bola Tinubu, Hon. Femi Gbajabiamila da gwamnan Jihar Legas, Mista Babajide Sanwo-Olu, domin ya samu wa’adi na biyu a matsayin gwamnan Delta.

Shugabannin jam’iyyar PDP na Jihar Delta, sun tofa albarkacin bakinsu game da soyayyar Oborebwori da shugabannin APC. Shugabannin jam’iyyar, wato Mista Theophilus Ekiyor, Mista Ochuko Oghenekome, da Mista Ezekiel Chukwudi, a wata budaddiyar wasika, sun zargi gwamnan da yin akala a sirrance da shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Hon. Femi Gbajabiamila da gwamnan Jihar Legas, Mista Babajide Sanwo-Olu, domin ya samu na wa’adi na biyu a matsayin gwamnan Delta.

Idan za a iya tunawa dai, dan majalisar tarayya kuma diyar tsohon gwamnan Jihar Delta, James Ibori, Hon. Erhiatake Ibori-Suenu, ta fice daga PDP zuwa APC a bara. Ibori dai ya yi zamani da Tinubu a matsayin gwamna a 1999 kuma makusancinsa ne.

Sai dai gwamnonin sun musanta wannan jita-jita, inda suka yi magana ta bakin mukarrabansu cewa ba za su bar jam’iyyarsu zuwa jam’iyyar APC mai mulki ba.

Haka zalika jam’iyyunsu sun bayyana irin wadannan ikirari a matsayin yaudarar jam’iyya mai mulki, inda suke neman haifar da rudani a cikin jam’iyyunsu da kuma zargin gwamnonin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2027GwamnoniZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hajjin 2025: Gwamantin Tarayya Ta Zabi Kamfanonin Jirage 4 Don Jigilar Maniyyata

Next Post

Za A Kammala Aikin Titin Abuja-Kaduna-Kano Cikin Watanni 14 – Gwamnati

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

6 days ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

7 days ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

7 days ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

2 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

2 weeks ago
Next Post
Za A Kammala Aikin Titin Abuja-Kaduna-Kano Cikin Watanni 14 – Gwamnati

Za A Kammala Aikin Titin Abuja-Kaduna-Kano Cikin Watanni 14 – Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

September 12, 2025
Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

September 12, 2025
Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

September 11, 2025
Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

September 11, 2025
Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

September 11, 2025
Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

September 11, 2025
Shettima

Shettima Ya Bada Umarnin Gaggauta Raba Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Ƙananan Manoma 

September 11, 2025
An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

September 11, 2025
Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.